Chapter 30
Chapter 30
mutum ne don duk faɗin garin nan babu inda zan shiga ba a san sunansa ko an san shi a fuska ba. Rimi-rimi ya aiko aka ɗauke ta zuwa otel yarinyar nan ta burma masa wuƙa a cikinsa ta ji ajalinsa har lahira ta kwashe masa maƙudan kudaɗe ta tsallake boda, ta bar ni a cikin masifa da ha'ula'i aka yi mini rufgudu na yi trending a cikin garin nan. Da ƙyar aka same ta a can yankin sudan aka cafke ta kafin na sama salama, ke ma na lura wannan simi-simin da kike yi tsabar tsagwaron munafurci da iya ƙulla luggu". Ilahirin jikina gabaɗaya ya yi sanyi ƙalau sai da na ja dogon numfashi na fesar kafin cikin rauni na furta"Hajiya har cikin raina na yanke wannan hukuncin". Ta ɗan yi jim tana bi na da kallo kafin can cikin wani irin dakakkiyar murya ta ce da ni"ke yarinya sa idonki a cikin nawa ni ɗin nan da kike gani wargi ce daidai ƙugun ko wacce ƴar bariki da take jin karanta ya kai tsaiko". A hankali na cira kai na sanya idanuna a cikin nata sai dai na kasa jurar jimirin haɗa ido da ita babu shiri na rusunar da ƙwayoyin idanuna ƙasa ina sauraran zancen da ta ɗaura da shi. "Ina fatan abin da kika furta su kasance gaskiya don ina mai tabbatar miki da cewar duk abin da kika jangalo a kanki zai ƙare don duk tsuntsun da ya ja ruwa shi ruwa kan duka. Akwai sharruɗa da nake gindayawa duk wata yarinyar da take cikin gidan nan, duk wani namijin da kuka yi mu'amala da shi ina da kaso ɗaya cikin uku na abin da ya sallame ki ina fatan ki na saurarana?". Na gyaɗa mata kaina alamar e da hakan ya ba ta damar cewa"ki na da mutane a ƙasa ko kuma mu nema miki duk yadda kike da suran nan babu wanda zai gan ki ya ji ba ki burge shi ba balle har ya kau da kai". "Babu wasu a ƙasa". Na amsa mata muryata can ƙasa kamar an dannen kwaɓo a cikin ruwan zafi. "To ku shirya da dare bayan misalin ƙarfe takwas za ki yi baƙo". Kaina kawai na jin wani irin abu yana tasowa tun daga ɗan yatsana yana bin dukkan sassan jikina, na tashi cikin rashin kuzari da ƙwarin jiki zan fita na ji an ƙira sunana da hakan ya tilasta mini tsaya wa ba tare da na waigo ba. "Ke kuma La'aniyatu me ye ya fito da ke daga cikin ɗakin? Ke da kika ce ba ki da lafiya kanki yana yi miki ciwo". "Umma ni fa na warke. Sai ki yi ta garƙame ni a ɗaki kamar wata ƙaramar yarinya kuma na daɗe da gane manufarki akan hakan. Harkar da kike jawo ƴaƴan wasu cikinta ne ni ba kya so na bi wannan layin, ai an ce duk abin da ka shuka Umma shi za ka girba". Tsam Hajiya Babba ta miƙe"ke La'aniyatu ki san irin maganan da za ki na furta domin ni ɗin uwarki ce. Kuma duk lalacewa ta ba za ki sauya ni a matsayin mahaifiyarki ba kamar yadda duk lalacewar tuwo ba a sauya masa suna". "Ni ban ce zan sauya ki a matsayinki ba amma ina gaya miki abin da yake zahiri ne wanda ko ba ji ma ko ba daɗe ko kuma raye ko ba ma ciki rayayyu, babu makawa sai hakan ya faru....". Ba ta ƙarishe zancen ba Hajiya Babba ta zuga mata mari mai matuƙar sauri har sai da hancin cikina ya kaɗa. "Tsinanniya wacce ba ta san haƙƙin uwa ba, in sha Allahu ke kam ba za ki gama da wannan duniyar salin ƙalin ba. Da ba a cikin ɗakin nan na haife ki ba sai na ce sauya min ke aka yi a asibiti, duk ƙoƙarin da nake yi wajen inganta rayuwarki da ganin ba ki nema komai kin rasa ba La'aniyatu ba kya gani?" Ta ƙarƙare zancen cikin sanyin amon. Kasa motsawa na yi daga inda nake tsaye munanan kalaman Hajiya Babba suka jirkita mini tunanina, na tuna da Ummanta a lokacin da take jifa na da makamantan irin waɗannan kalaman wanda ina da yaƙinin su suka yi tasiri a kaina har na tsinci kai a cikin gidan karuwai da ƴan daudu. Ji na yi an ja hannun aka fizgo ni muka fice daga cikin ɗakin ba mu tsaya a ko'ina ba sai cikin ɗakina. Na fizge hannuna daga cikin riƙon da ta yi mini. "La'aniyatu me ye haka kike yi?". A zafafe ta mayar min da tambaya"me ye kika ga na yi?". Na watsa mata wani kallo don ban taɓa raina wayo, hankali da hangen nisanta ba irin na yau. "Hajiya fa mahaifiyarki ce ko me ye take aikatawa hakan ba shi zai ba ki damar da za ki na faɗa mata duk wani abun da ya zo bakinki, ba tare da kin tauna kalaman ba". "Ni yanzu ba wannan ba shin da gaske kike za ki bi hanyar da suke so?". Na harare ta da wutsiyar idanuna kafin na ce"ƙwarai kuwa". Ina dasa aya na wuce zan zauna ta jayo gefen hijabina. "Me yasa za ki aminci bayan kin yi wa kanki alƙawarin ba za ki aikata ɓarna ba? Ke ma kenan za ki zama ba ki da bambamci da ragowar matan gidan nan? Kin san yadda suke yin wulaƙantaccen ƙarshe kuwa? Wasun su su kamo da jinyar da za ta yi ajalinsu, wasu shaye-shaye ya haukatar da su yayin da wasu kuma tsufa yake cim musu duk waɗanda suke mu'amala da shi su yi ɓatan gado su gudu ko sama ko ƙasa. Idan ba ki yi sa'a ba kuma har da kuzurin cuta za ta jajiɓowa kansu wasu kuma su haifa shegu waɗanda ba su da uba, haka rayuwarsu da ta yaran za ta faɗa garari su zama abin wulaƙantawa da tozarwa a tsakanin al'umma". Na cire hannunta daga jikina na je na yi zamana ina cire hijabin da yake kaina"duk na san da hakan, me ye zan zauna na yi bayan ga abin da ya kawo ni nan ban yi shi ba. La'aniyatu duk matan cikin gidan nan ƙaryan bariki suke yi yanzu ne zan nuna musu ainihin abin da kalmar ta ƙunsa, domin zan warware musu zare da abawa. Ke dai kawai ki zuba mini ido ki kuma bi ni da fatan alkhairi". "Mata da yawa da haka suke fara har su zarje su zama jan wuya. Amatullah ina jiye miki tsoron abin da kike shirin aikatawa zai haifar miki a nan gaba, kin ga muranen nan ba su da tausayi balle imami da zarar sun fara nannaɗa garɗin mace to ba sa barin ta haka banza wallahi har malamai da bokaye suna bi, don wasu ba a cin kuɗinsu a zauna lafiya". Taƙaitaccen murmushi na yi kafin na ce da ita"ni kuwa zan ci kuɗin kuma lafiya sumul". "Amatullah". Ta ƙira sunana cikin wani irin yanayi da ya fi kama da na zallan mamakin da ba sirka shi da komai. Na ɗage mata idona guda alamar lafiya? Ta zo ta zauna a kusa da ni tare da riƙo hannuna za ta yi magana na dakatar da ita. "Ki zuba
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98