Chapter 93
Chapter 93
ƙira don ta ji daga gare ni akan abin da Anty Zulaihatu ta ƙira ta sanar mata, na kuwa tabbatar mata da zancen ta yi hamdala tare da yi mana addu'a. Take aka soma shiri da shirye-shiryen tarban iyayen Saifullah gobe ranar Anty Zulaihatu a gidan ta kwana, washe gari da yamma lilis magabatan Saifullah suka zo su gidan Anty Sawwama neman aurena a hannun Yaya Alhassan aka kuma ba su tare da sanya auren nan da sati huɗu masu zuwa. Ranar wuni na yi da zazzaɓi da boda fargaba da zulumi da dare muka sha kukanmu tare da Anty Sawwama da Anty Zulaihatu sa boda tuno Abba da muka yi da hashashen irin farin cikin da zai yi don ganin wannan ranan in da yana raye. Bayan kwana biyu Amir ya ɓullo da wani zancen wai na je na yi gwajin genotype, Anty Sawwama ta yi kai da fata ta ce ba zan je ba, har da faka hujja da cewar su a lokacinsu duk ba a yin wannan gwaji ga shi kuma har suka gama haihuwarsu lafiya sumul, daga su har ƴaƴan. Sai da ta ga shi ma kansa Saifullah ɗin ya goya bayan a je a yi gwajin sa boda gujewa afkuwar matsala, sannan ta saduda ta zubar da makaman yaƙinta. Muka cire ranar da za mu je mu yi gwajin lokacin ana sauran sati uku bikin, duk da tun kafin lokacin shi Saifullah ya shaida mini cewar na shi AS ne don ya daɗe da sanin hakan. Rananr gwajin tare muka je da Anty Zulaihatu da kuma Umar muka je aka yi mana gwaji ni da shi, aka je mu ɗan jira kafin sakamakon ya fito haka muka jira aka fito sakamakon Saifullah da Umar suka shiga amsowa. Babu jima wa suka fito ba su ce da mu komai ba muka shiga mota muka tafi, maimakon mu koma gida sai muka ƙara wuce wa wani asibitin, Anty Zulaihatu ta gaza jurewa har sai da ta tambaya ko lafiya suka ce da ita lafiya kawai su na so tabbatar da wani abu ne. Wani gwajin aka ƙara yi mana, kamar karon farko Saifullah da Umar ne suka shiga suka also sakamakon. A wannan lokacin yanayin da suka shiga ya yi muni sosai haka muka shiga mota zuwa gida ya faka a ƙofar gidan, ya ce mu shiga ciki ga shi nan shiga wa, haka muka sauƙa ni da Anty Zulaihatu muka shiga cikin gidan, kowa da abin da yake saƙawa a cikin ransa. [12/27, 5:50 PM] Maimunatu Iyam🥰: *DAFIN HARSHE* ©️ Maimuna Tijjani Iyam ______________________________________ Page 8️⃣1️⃣ Tun da muka shiga cikin gidan na kasa zaune balle tsaye ɗaki na shiga na yi ta safa da marwa, yayin da tunani kala-kala suke ziyartar ƙaramar curin kwanyata. Cikin wannan halin Anty Zulaihatu ta shigo ta ƙira ni ta ce na zo falo ana nema na, haka na biyo ta a baya har suka iso cikin falon inda muka iske Umar da Anty Sawwama zaune a cikin falo. Muka ƙariso ciki muka zauna. "Da kuke asibitin ya ya aka yi? Na ga kamar gabaɗayanku hankalinku ba a kwance yake ba. Ko dai wata cutar aka ce ɗaya daga cikinku yana ɗauke da ita?". Anty Sawwama ta yi tambayar tana kafe Saifullah da ido da ya kasa cewa uffan illa sadda kansa ƙasa da ta yi. Anty Zulaihatu ne ta yi magana a madadinsa"wallahi Umma mu ma ba mu san abin da yake faruwa ba, sun dai ce mu shigo ciki ne kawai ba tare da sun sanar da mu komai ba". Takardan sakamakon gwajin Saifullah ya miƙa wa Anty Zulaihatu ta amsa yayin da yake koro jawabansa. "Mun je asibitin farko aka yi gwaji inda sakamakon ya nuna cewa ni da ita Amatullah gabaɗayanmu AS ne, daman ni na san nawa na zo ne don a ƙara tabbatar wa, ban yarda da sakamakon don a wasu lokutan ana samun matsala dangane da kayan aikin gwaji ko kuma daga su kansu ma'aikatan hakan ya sa muka ƙara zuwa wani asibitin aka ƙara gudanar da wani binciken, nan ma ba a sama canji daga wancan gwajin na farkon ba. Tabbas ta tabbata ni da Amatullahi dukkan mu AS ne". "Me ye hakan ke nan ya ke nufi ɗan nan? Shi AS ɗin mene ne aibunsa? Ni fa shi yasa tun farko ban yarda aje a yi wannan gwajin ba sa boda gudun wanzuwar matsalolin da wannan nan mutanen masu jajayen kunnuwan nan suka kawo". "Umma hakan ya nufin aure a tsakaninsu ba zai taɓa yiyuwa ba, sa boda ko da an yi auren matsaloli da tashin hankalin da za su biyo bayan auren sai ya tushe duk ginin soyayyar da aka yi ta wargaza komai". Anty Zulaihatu ta yi zancen tana juya farar takardar sakamakon gwajin da yake riƙe a hannunta. "To sai me ye don dukkan su AS ne? Mu da can a lokacin mu ana wannan gwajin ne amma ba ga shi mun yi auren mun haihu lafiya sumul ba. In sha Allah babu abin da zai hana auren Saifullah da Amatullah". Anty Sawwama ta yi zancen tana tashi ta yi shigewarta cikin ɗakinta, da kallo dukkaninmu muka bi ta kafin Anty Zulaihatu ta saka salati cikin tsananin damuwa da rashin mafita da kuma madafa. "Anty yanzu ya ya za a yi a fahimtar da ita illan da yake tattare da hakan?". Saifullah ya yi zancen muryarsa har rawa take yi yayin da yake tsayar da idanunsa akan Anty Zulaihatu. "Wallahi ban san yadda zan yi wa Umma bayani ta fahimta illan wannan abun ba. Amma bari na ƙira Yaya Alhassan na sanar da shi halin da ake ciki". "A'a kar ki ƙira shi alhalin yana can wajen aikinsa, idan ya dawo kawai ki yi masa bayani ni ma in sha Allah zan ƙira shi mu yi magana a waya". "To shi kenan duk yadda ka ce haka za a yi". Sai a lokacin Umar ya buɗe baki ya yi magana damuwa jingim a tattare da furucinsa"ni na ma rasa abin da zan ce, gabaɗaya lissafina ya katse". Dafo kafaɗarsa Saifullah ya yi cikin salon ƙarfafa masa gwiwa ya soma faɗin"haka Allah ya ƙaddara Umar, sannan ko wani Bawa ba ya wuce ƙaddararsa a rayuwa. Wataƙila Allah bai ƙaddara akwai aure tsakanina da Amatullah ba. Mu ƴan Adam ne kawai muke lissafinmu amma tun kafin wanzuwan mu a bayan ƙasa ya rubuta abin da zai kasance da Bawa, mussamman a sha'anin aure ka san an ce wani ba ya auran matar wani". Anty Zulaihatu kam kasa jurewa ta yi ta tashi ta bar cikin falon ta na matsar ƙwalla, daga bisani ma Umar tashi ya yi ya fita. Ban taɓa zato da tunanin cewa tashin hankali idan ya girmama ba a ma samun damar zubar da ƙwalla ba, sai da na tsinci kaina cikin wannan matsanancin halin. Duk yadda na so na zubar da hawaye na kasa yin hakan idanuna ya bushe ya soye tamkar na soyayyan kifin da aka tsamo daga cikin mai. Na yi nisa cikin tunanin da na dulmiya a cikinsa na tsinkayo muryarsa dab da ni da hakan ya ba ni tabbacin cewar ya sauya wajen zama ya dawo kusa da inda nake zaune. "Amatullah
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98