Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 83

Chapter 83

Dafin Harshe Part 1 Complete Hausa Novel – Full Story 1,207 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

ba me yasa ka shigo rayuwata ka yi tsamo-tsamo a cikinta a wancan lokacin". Ya yi saurin katse mini hanzari"Amatullah ni ban so ki ba, na san dai tabbas akwai tausayinki da yake maƙale a ƙasan raina". Yana ƙare zancen ya miƙe tsaye ni ma na tashi na je na tsaya a gabansa. "Ka kalla cikin idanuna Muhammad Taufik sai ka sanar da ni cewar ba ka taɓa jin soyayyata a cikin ranka ba, ta hakan ne kawai zan yarda da kai. Har na iya amincewa abokinka". "Ya isa haka Amatullah ya isa mana". Ya yi zancen cikin wani iriyar sarƙarƙiyar amo mai bayyanar da tarin damuwar da yake tattare da shi, ya kai hannu ya shafo suman fuskarsa yana saki ajiyar zuciya mai nauyi. "Na ji Amatullah a lokacin na ji soyayyarki a cikin raina, na ji a raina cewan zan iya rayuwa da ke a cikin ko wani hali kika tsinci kanki a cikinsa. Wannan dalilin ne ya sanya na dage tsayin daka wajen ganin na nemo ki har kin dawo cikin ƴan uwanki. Na yarda har yanzu akwai soyyayarki a cikin raina sai dai tun lokacin da Saifullah ya zo min da batun yana sonki tun daga lokacin na shiga ba wa zuciyata haƙuri, don ba zan iya gasa da Saif akan komai ba ko ya kuwa nake tsananin so da ƙaunar abun ya kai ƙololuwa. Zan iya sadaukar da komai akan Saifullah raina ne kawai ba zan iya zarewa na ba shi ba shi ma ɗin don ba ni da iko akan hakan ne". Ya yi shuru na tsawon wasu mintuna kafin ya matso dab da ni idanunsa akaina ya ci gaba da furzo da sirrin take taskace cikin tsokar zuciyarsa. "Ba zan iya hana zuciyata son ki Amatullah har abada, kuma komai za ki yi ko ki zama hakan ba zai taɓa sanya soyayyar da nake yi miki ta sauya ba. Sai dai dole na danne abin da nake so don wanzuwar farin cikin aminina, zan taya sa yaƙin neman soyayyarki har sai na ga ya yi nasara. Sannan ina roƙonki don Allah kar ki fitar da wannan maganan, ina so yadda muka yi ta a nan mu burne ta a nan". Yana dasa aya a zancen ya sa kai ya fice yana ɗan lumshe idanunsa da suka cika da ruwan ƙwalla, da ido na raka shi har ya fice daga cikin falon daidai sa'ilin fitarsa daidai lokacin da na durƙushe akan gwiwoyina ina jero wani kuka marar sauti. Haka Anty Sawwama ta zo ta same ni ta ɗago ni daga inda nake durƙushe ta kwantar da ni a jikinta yayin da take shafa kaina cike da kulawa ta soma faɗin"Uwata ki daina wannan kukan ya isa haka, kuka ba ya magani da yana magani tabbas da yanzu ya kawar miki da dukkan matsalolinki. Kuka ba mafita ba ne sai dai ma ya haddasa miki wani ciwon kamata ya yi ki ɗaga hannu ki gode wa Allah da ya yi miki wannan suturan, har ya kawo miki mai sonki kuma ɗan gidan mutunci da nutsuwa. Ki yi istikara ki nema zaɓin Allah ya yi miki zaɓin da babu nadama, dana sani balle kuma cizon ɗan yatsa a cikinsa. In sha Allah ina ji a jikina rayuwarki ta kusa sauyawa farin ciki zai maye gurbin dukkan wasu baƙaƙen abubuwan da suka wakana a cikin rayuwarki". Luf! Na kwantar da kaina a jikinta ina cikin gaba da sauraron tarin nasihan da take yi mini, a haka ina kwance a jikinta har bacci ya ɗauke ni ba tare da na sani ba. Dogon bacci na yi ban tashi ba sai can yamma lilis na tashi na yi wanka na zo na gabatar da salla a makare, na daɗe kan sallayan ina ta tunani kafin na tashi na fito waje na yi wasu ayyukan kana na soma kici-kicin ɗaura girkin dare. Sai dab sallan magrib na gama girkin na sauƙe tare da yin alwala na shiga ciki na yi salla, ban tashi daga inda na yi sallan ba na ɗauko alƙur'ani na soma karanta cikin nutsuwa da fitar da haƙƙin ko wani harafi bisa ƙa'ida. Sai da na yi sallan isha'i kana na tashi na fito daga ɗakin lokacin har su Yaya Alhassan sun dawo, na zubo mana abinci tare da Anty Sawwama yayin da Yaya Alhassan, Amir da Umar suka ci nasu tare a kwano ɗaya kamar yadda al'adan gidan yake, bayan mun kama cin abincin na tattare kwanukan na je na wanke su ina doso ƙofan falon na ji Anty Sawwama tana sanar da Yaya Alhassan yadda suka yi da su Saifullah. Kaina a ƙasa na shigo cikin falon na wuce ɗaki daidai lokacin da nake jiyo muryar Yaya Alhassan yana faɗin"tabbas kam mutumin kirki ne, sai ta ya ta da addu'a in shi ne alkhairi gare ta Allah ya tabbatar...". Bai ƙarisa zancen ba sakamakon wani tarin da ya sarƙafe shi ya fara yin sa tamkar zai shiɗe, da sauri na juyo na fita waje na je na ɗebo masa ruwa na miƙa masa. Amsa ya yi ya ɗan sha kaɗan kafin tarin ya lafa muka haɗa ido da shi na ga ya yi hanzarin ɗauke na shi. Yana amsa sannun da Amir da Umar suka haɗe bakin wajen yi masa. Ya miƙe da hakan ya sa ni bin shi da kallo sai dai ko kaɗan ya ƙi yarda mu haɗa ido da shi, a taƙaice ya furta"Umma zan je na kwanta gabaɗaya ba na jin daɗin jikina". Bai jira amsar da za mu ba shi ba ya juya ya fice daga cikin falon, ya bar mu da tarin tambayoyi a ƙunshe a cikin ranmu. Ganin hawaye ya na ƙoƙarin ƙwace mini ya sanya ni na yi wuf na shige cikin ɗaki na zube akan katifa ina sakin hawayen tamkar bakin indararo, na daɗe ina kukan yayin da nake tuno zancen da muka yi na ƙarshe da Yaya Alhassan kafin sheiɗan ya yi nasara a kaina na sa ƙafata na guje wa gida da ƴan uwana masu tsananin ƙaunata. Tashi na yi na zauna tare da tafka wani uban tagumi cikin duhu dulum da ya mamaye cikin ɗakin ko tafin hannuna ba na iya gani, gabaɗaya na rasa mafita da yadda zan ɓullo wa lamarin balle har na sama matsaya guda da zan tsaya akan sa. Jin ƙaran waya na yi sai dai da yake ban saba da riƙe wayan ba, har ta gama rurin neman agaji ta yi shuru ban bi ta kanta ba, sai da aka ƙara ƙira a karo na biyu kafin na kai hannu na jawo wayar na zuba wa fuskar wayar kallo. Baƙuwan lamba ne babu suna, kuma a cikin maganganun da muka yi da Amir bai ce mini ya ba da lambar a kowa ba, hana ƙarya dai ya ce da ni ya sanya mini lambobin duk wanda ya dace a ciki. Ina ganin ƙiran har ya katse aka ƙara ƙira a karo na uku kafin na ɗaga na sanya ta a amsa-kuwwa na ajiye a gabana. Cikin wani irin sanyin murya mai ratsa jini da jijiyoyin ya bi har ta cikin ɓargo na ji an yi sallama, ba tare da na ɗauki muryar ba na amsa sallamar daga nan

Table of Contents

Chapters

98 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});