Chapter 22
Chapter 22
na amsa matsamin da take miƙo mini na ci gaba daga inda ta tsaya. Gwangwani madarar ruwa huɗu ta ɗauko duk ta ɓula su ban da madarar garin da ta ɗauko saket guda ta yanke bakinsu da almakashi. Ta ɗauko wani ƙaramin kwanon tangaran ta juye madarar garin a cikin ta dame shi da ruwa sannan ta juye cikin ruwan da yake tafasa akan wutan ta yi ta juya shi har sai da ya fara yin kauri, ta juye madarar ruwan gwangwani biyu ragowar biyun kuma ta ajiye su a gefe, ruwan flavour na ga ta tarfa a ƙadan a cikin kafin ta sauƙe shi. Ta ɗauko kofi mai marfi ta juye madarar ruwan guda biyu a ciki, gwangwanin huɗum gabaɗaya ta haɗa ta mayar da su inda ta ɗauko su. Tana juyo wa muka haɗa ido. "Wannan kallon fa?". Ta jefa mini tambayar cikin tsawa da ɗaga murya, na yi hanzarin rusunar da ƙwayoyin idanuna ƙasa tare da faɗin"ki yi haƙuri". Kafin ta kai ga furta wani kalma Hajiya Muhibbat ta shigo cikin kicin ɗin duk muka haɗe bakin wajen gaishe ta ta amsa mana fuskarta ɗauke da annurin da ya ƙara fitowa da kyawunta. "Sannunku da aiki". Ta yi furucin yayin da take sa hannu ta ɗauki ƙosan da yake gabana ta kai bakinta. "Amma ƙosan nan ba dai laushi ba, ke kika yi haɗa ƙullin ne?". Na jijjiga mata kaina alamar a'a tare da faɗin"ba ni ba ce". "Amma kuwa ya yi daɗi sosai. Na tabbatar Saif zai ji daɗinsa". Ta juya tana kallon Altine"ki shirya abincin a dinnig table, Amatullah kuma ta je sashin Saif ta ɗauko su Aryan ta yi musu wanka kafin ki gama". "To ranki ya daɗe uwarmu maganin kukanmu". Ba ta amsa mata ba ta juye ta fice daga cikin kicin ɗin tana amsa ƙiran da ya shigo cikin wayarta. Bayan fitanta mun fi mintuna uku cikinmu babu wanda ya yi magana, har na kammala tuyar ƙosan na sauƙar da man. Ganin shurun ya yi yawa ya sani kawar da shi ta hanyar faɗin"Anty ina ne sashin nasan na je na ɗauko su....". Tun kafin na rufe bakina take gallo mini harara wani na bin wani tamkar wacce na watsa garwashin wuta, ko na faɗi wani abun da bai yi mata daɗin ji a kunnuwanta ba. "Daman can ba ki san sashin nasan ba kika bari ta tafi daga nan ba ki tambaye ba?. Sai ki fita yanzu kam ai ki tambayo". Yadda ta furzo da zancen shi ya fi komai ƙona mini rai da har ban san lokacin da bakina ya suɓuce na furta kalaman da suka shayar da ita giyan mamaki ba. "Don na tambaye ki laifi ne? Na da ke ɗin gabaɗaya a ƙarƙashin Hajiyar muke kuma aiki muke yi don a biya mu". Ban tsaya sauraron amsar da za ta ba ni ba na fice daga cikin kicin ɗin zuciyata har wani tafasa take yi tsabar ɓacin ran da nake cikinsa. A rayuwata ta duniya na tsani a wulaƙanta ni balle a zo gandon da za tozarta ni. Sai da na fito cikin harabar gidan na riƙe ƙuguna ina tunanin inda ya kamata na nufa da zai sada ni sashin nasan, jiya dai lokacin da ya ce a shirya su Aryan za su fita wata ƙofa na ga ya shiga a cikin falon Hajiya babu jimawa kuma ya fito a shirye tana ba za ƙamshi. Na sauƙe ajiyan numfashi a hankali ina ƙara ɗaga kaina sama, idanuna suka sauƙa akan Baba mai gadi da yake nufo inda nake tsaye, hannunsa riƙe da bokatin ruwa. Da sauri na isa gare shi na kai hannu zan karɓa bokatin ya hana ni. "A'a ɗiyata bar shi ai ba za ki iya ba ma, wai bayi ne nake so na yi a shukokin nan mai musu bayin yau bai sama zuwa ba". Na saki taƙaitaccen murmushi kafin na ce"Allah sarki! Ni ma wai Hajiya ce ta ce a je sashin Saif a ɗauko su Aryan, kuma na kasa tantance wanne ne sashin na san". Da hannunsa ya yi mini nufi da sashin kafin ya furta"kin gan sa can shi ne sashin na san". "Ai kuwa Baba na gode sosai da sosai, Baba na ga zanen kanurai a fuskanka na ce ko kai ma kanuri ne?". Sai da ya murmusa kafin ya ce"gaba da baya ma kuwa, ni haifaffen jihar Borno ne cikin garin bama. Uwa da ubana duk kanurai ne". "Ni ma kuwa mahaifina kanuri ne sai dai ko kaɗan ban iya yaren ba". "Kuma ai ba shi ma da wahala idan aiyukan cikin gidan sun yi miki sauƙi ki dinga zuwa ina koya miki. Ko kuma ki zagaya wajen mai ɗakina". Cike da jin daɗi na furta"na gode sosai Allah ya saka da alkhairi". "Amin". Ya amsa da shi yana ƙara yalwata annurin dake kan fuskarsa, ya wuce wajen bayin shukansa ni ma na ɗauki hanyar sashin da na ya nuna mini. Wannan sashin da na ga ya shiga da safe ne. An ƙawata ƙofan sashin da shuke-shuken wasu turanni masu kyau da ɗaukar hankali da suka kasance launin gore da ruwan ɗorawa. Wasu a cikin wani abu kamar tukunyan ƙasa an taraye a sama. A hankali na isa bakin ƙofan na soma ƙwankwasa tare da rafza sallama. Har sai da na gaji da tsayiwar na juya zan tafi na ji an buɗe ƙofar na waigo na ga Aryan ne ko Ayan oho don ban iya tantance wane ne a cikin su ba. "Ayan ina Aryan ɗin?". Ta tsaya yana kallona"ba Ayan ba ne Aryan ne". "To ina shi Ayan ɗin? Mamanku ne ta ce ku zo a yi muku wanka". Kamar ba da Hausa na yi masa zancen ba ya tsaya yana ta kallona sai can ya ce"Umminmu?". Na gyaɗa masa kaina alamar e kafin ya ce da ni wani abu Saif ya iso wajen hannunsa saƙale cikin na Ayan. Ganin sa ya sanya ni na rusana ina gaishe shi sai dai bai amsa mini ba. Kwarjini da cika idon da ya yi mini ya sanya jikina fara karkarwa da ƙyar na haɗo kalmomin da zan furta suka zauna a bisa harshena. "Daman Hajiya ce ta ce su Ayan su zo a yi musu wanka". "Ki je abin ki za su zo". "To". Na amsa da shi a gajarce ina ɗaukan hanyar barin wajen, na runtse idanuna a ƙoƙarin daidaita nutsuwata da ta yi nisa da gangar jikina. Ni da uwata Hafsatu ta haife ni ban taɓa ganin mutum mai tsananin kwarjini da cika ido irin wannan bawan Allahn ba. Fuskarsa a sake take duk da ba ya murmushi amma fuskar ba a murtuƙe take ba. Ina tafe ina ta saƙe-saƙe a cikin raina har na isa sashin Hajiya ina shiga Aryan da Ayan suka shigo na kamo hannunsu ina faɗin"mu je na yi muku wanka ko?". Suka gyaɗa mini kansu alamar sun ji. Na ja hannunsa muka nufi cikin ɗakinsu, na cire musu kayansu na ɗaura musu towel muka shiga cikin banɗakin. Fanfon banɗakin irin na gidan Anty Zulaihatu ne mai na ruwan zafi da na sanyi, don haka ban shan wani wahala ba na kunna na ruwan zafin na tara na na tsirka shi da na sanyi daidai
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98