Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 76

Chapter 76

Dafin Harshe Part 1 Complete Hausa Novel – Full Story 1,207 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

ƙafa da ƙafa ya zo shi har cikin gidan nan don kawai ya yi mana gaisuwa to mu mutunta juna. Su yi abin da ya kawo su mu watse". Hawaye ne kawai yake ta ambaliya a fuskana ina faɗin"Anty a duniya babu mutumin da ya taɓa gayyaya mini baƙaƙan maganganuna, ya suffanta ni da abin da ko kusa ban aikata shi ba kamar wannan mutumin. Har yanzu idan na rufe idanuna ina tuna munanan kalamansa gare ni". Shuru ya biyo bayan zancena na ƙarshe har na tsawon wani lokaci kafin can na tsinkayo muryar Saif ya sauƙa a cikin kunnuwana. "Tabbas duk abin da kika faɗa haka ne babu kuskure ko ƙage a cikinsa, na aikata miki abubuwa da dama na zarge akan abin da ba ki aikata ba. Sannan akan idona aka wulaƙanta ki na kasa cewa komai. Sai dai duk da hakan ke ce mace ta farko da ta fara kawo mana ɗauki a cikin rayuwarmu ta warware mana wani babban ƙullin da duk ba mu san shi ba. Ranar da kika sanar da mu wannan abun washe gari na tafi garin Abuja na sauƙa a wannan otel ɗin da kika ba mu bayanansa, haƙiƙa na gane wa idanuna abun mamaki don da idona na kama Yaya Saddam da karuwa su na kwance a cikin ɗakin otel ɗin. An yi rikici sosai har sai daga bisani Anty Muhibbat ta ji komai ta bi mu can Abujan sai dai ga mamakina ko kaɗan ba ta ga laifin Yaya Saddam ba sai ma ƙoƙarin ba shi kariya da take yi ta ko wacce fuska. Hakan ya jefa ni cikin tunanin da na baza ma nemon gaskiyar da yake ƙunshe ƙasan kalaman kariyar da take ba wa Yaya Saddam. Nan na gano cewar kafin aurensu ita ɗin budurwan marigayi abokinsa ne watau Yaya Usman da suka yi wa junansu alƙawarin aure tun suna jami'a, wannan dalilin ya sanya suka mayar da kansu tamkar miji da mata ta hanyar biyawa junansu buƙata ba tare da shakkan kowa da komai ba. A lokacin Yaya Saddam ya san komai aka tsaka da wannan lamarin Allah ya karɓi rayuwar Yaya Usman a lokacin Anty Muhibbat tana ɗauke da cikinsa, a sa'ilin da ta sanar da Yaya Saddam da ake ciki ya shiga cikin matuƙar tashin hankali ya nema a zubar da cikin amma ta nuna hakan ba zai taɓa yiyuwa hasalima ko dai ya aure ta ya rufa mata asiri ko kuma ta je ta bayyanawa ita mahaifiyar Yaya Usman ɗin halin da ake ciki". Ya dakata ta hanyar jan dogon numfashi ya fesar kafin ya ɗaura daga inda ya tsaya"idan akwai wanda mahaifiyar Yaya Usman ta yarda da shi ta kuma aminta da shi to a bayan Yaya Saddam yake. Wannan matar ta taka rawan gani a cikin rayuwarmu gabaɗaya, a gidanta ya yi karatu ba ta taɓa nuna masa bambamci tsakaninsa da ƴaƴan da ta haifa ba, hatta ni ta nuna min so da ƙauna lokacin da iyayenmu suka rasu ta ja mu a jikinta ta maye mana gurbin duk wani abun da muke jin cewar mun yi rashinsa. Wannan dalilin Yaya Saddam ya dubae har ya abin ce da auren Anty Muhibbat bayan sun yi yarjejeniyar za a zubar da jikin da take ɗauke da shi. Ba na mance kukan farin cikin da mahaifiyar Yaya Usman ta yi lokacin da ta ji cewar Yaya Saddam ne zai auri Matar da Yaya Usman ya so aura Allah bai yi ba. Ta yi hidima sosai a bikin har Allah ya ƙaddara musu kasancewa a matsayin mata da miji har da rabon haihuwar Aryan da Ayan. Sun yi auren ne kawai amma Anty Muhibbat ta san cewa babu ko da ɗigon soyayyarta a cikin zuciyarsa, tun daga wannan lokacin zuciyarta take ayyana mata cewar za ta jure komai daga gare sa don dai kawai wannan sirrin da suke rufe bai fito duniya kowa ya ji ba. Don ya kasa yarda da ita duk da kuwa mutuwar Yaya Usman ya sanya ta sauya". Al'ajabi da mamaki suka taru suka hana mu magana daga ni har ragowar mutanen da suke zaune a cikin falon. Anty Sawwama ta yi ta jinjina lamarin tare da yi mana nasiha mai ratsa jini da jijiya ta ƙarƙare da jan hankulanmu akan mu ji tsoron Allah a cikin dukkan abin da za mu aika. Har aka gama komai ban ɗago kaina ba balle na ce wani abu aka gabatar da addu'ar neman gafara da rahama ga Ummata kana suka fara haramar tafiya. Ko cira kai ban yi na dube su ba sai jin Muhammad Taufik na yi tana magana da Yaya Alhassan cikin girmamawa. "Yallaɓai idan babu damuwa mu na son magana da Amatullah a waje". Ba tare da nazari ko dogon tunanina ba Yaya Alhassan ya furta"ba komai ai, mu je daga wajen sai ta fito". Daga haka suka fuce. Anty Sawwama ta dafo kaina da na kwantar jikin ƙafafunta"tashi ki je ki ji abin da za su gaya miki". "Me ye kuma za su ce mini Anty? Duk abin da za su faɗa ai sun faɗe shi a cikin falon nan. Gaisuwar rasuwa suka zo yi kuma sun yi mene ne kuma ya yi saura?". Cikin lallashi ta ce"ki yi haƙuri ki tashi ki je ki ji abin da za su ce da ke kin ji Uwata?". Ba don raina ya so ba na tashi na nufi wajen ina goge guntun ƙwallan da yake ƙoƙ zubowa daga cikin idanuna. A ƙofan gida na iske su tare da Yaya Alhassan da Amir na iso wajen bakina ɗauke da sallamar da suka haɗe baki wajen amsawa. Yaya Alhassan da Amir suka yi musu sallama ta hanyar yin musabaha kana suka koma cikin gidan suka bar ni tsaye da su. Kusan mintuna biyu cikinmu babu wanda ya yi magana kafin can Saif ya ce"daman godiya nake so na yi miki sannan kuma na ba ki haƙuri akan duk abubuwan da suka faru, haƙiƙa na aikata miki ba daidai ba". Ban bar shi ya ƙarisa ba na ɗaga masa hannu alamar ya dakata. "Kamar yadda tun a ciki aka buƙaci na manta da duk abin da ya faru, to ka ƙaddara cewa komai ya wuce". Ya sadda kansa ƙasa yana murza zoben dake saƙala a ƴatsun hannunsa kafin ya ce"na gode". "Amatullah". Muhammad Taufik ya furta a karo na farko tun bayan da na fito waje, na ɗaga idona ina kallonsa yayin da shi ɗin ma ni yake kallo, take na ji wasu hawaye su na bin kuncina ba zan iya juran irin kallon da yake yi mini ba don haka na juya na shige cikin gida da hanzari, kai tsaye ɗaki na wuce ina shiga na faɗa kan katifa ina kuka marar sauti. Haka na wuni a cikin ɗakin in a fito waje to alwala zan yi ina yi nake koma wa cikin ɗakin. Washe da safe bayan mun yi karin kumallo ina zaune a ɗaki kawai na ji an yi sallama, idanuna a lumshe na amsa sallamar da hakan ya ke daida da ba ta iznin shigo wa. "Amatullah". Take na wartsake na tashi na miƙe tsam sa boda amon muryar ba ta kasance baƙuwa ga kunnuwana ba. Na ware idanuna akan

Table of Contents

Chapters

98 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});