Chapter 32
Chapter 32
ba tare da na san dalili ba [12/3, 2:54 PM] Aeesher: *DAFIN HARSHE* ©️ Maimuna Tijjani Iyam __________________________________________ Page 5️⃣6️⃣ Duk yadda na so na furzar da zallan mamakin da ya ganin sa ya ƙunsa mini bakina ya ƙi ba ni haɗin kai wajen aiwatar da hakan a aikatace, da ɗago idona ina kallonsa na ga ya watsa mini wani mummunan kallo da ban san sa'ilin da na rusunar da idanuna ƙasa ba. Sa boda cika ido da kwarjinin da yake da shi. "Zan jira ki a wajen motata ba zan iya tsayiwa a nan wajen ba". Yana gama maganar ya bar wajen ya nufi inda ya ajiye motar da yake can farkon layin na bi shi a baya zaƙwai-zaƙwai har muka isa ya jingina bayansa jikin motar tare da naɗe dukkan hannayensa a ƙirjinsa idanunsa a kaina ya furta"Anty ce ta ce a zo a duba ko lafiya kika tafi ba tare da kin yi mata sallama ba. Sai dai zuwan da na yi da kuma abin da idanuna suka gane min ya tabbatar min da cewar lafiya kike tun da har za iya fitowa ki gana da saurayi cikin wannan daren har da guzurin saƙo niƙi-niƙi a leda". Jikina ya yi sanyi ƙalau wasu hawaye suka kuma ciko mini idanuna sauran ƙiris su zubo na kai hannu na tare su. "Lafiya ƙalau kawai ba na jin daɗin jikina ne shi yasa na dawo. Amma ina sha Allah gobe sammako zan yi na zo.....". Tun kafin na kammala ƙarshen zancen ya tari numfashina. "Ba ma buƙatarki don haka ki yi zamanki. Idan ma ya zama dole to za a nema wata". "Ba kai ka ɗauke ni aiki ba ranka ya daɗe don haka ba ka da hurumin dakatar da ni, Hajiya ce kawai take da wannan ikon". Tabbas na hango mamakin zancena kwance a cikin idanunsa ya sauƙe numfashi da har sai da na ji sautin fitarsa. "Repeat yourself please". Duk da na fahimci abun da ya furta amma sai na sauya akalar zancen"a gaishe ta kuma a isar mata da saƙona". Ina gama furta haka na juya zan tafi na ji wata murya ta sauƙa a ƙofofin kunnuwana, muryar da ba zan taɓa manta tasirinta a cikin rayuwata ba. Muryar da ko ina gangaran mutuwa in na ji ta haƙiƙa zan gane amonta. Muryar da ta sama matsuguni ta zauna a cikin kwanyata ba tare da biyan tara ko haraji ba. Cak na tsaya jikina yana wani irin rawa tamkar wacce aka jona wa wutar lantarki haƙwarana suka datse harshena wanda ina da tabbacin har sai da ya fitar da jini. "Saif wai me ye yake faruwa ne? Ina ne nan wajen kuma?". "Ba komai Taukif shiga motar mu tafi kawai". "Wannan yarinyarta fa me ye haɗinka da ita? Na dai san ba ka zuwa ire-iren wajajen nan. Ke zo nan". Take ƙirjina ya soma dakan lugudan-lugudan tara-tara sau goma sha tara, zuffa ya soma tsantsafo mini sa'ilin da na ji takun tafiya ana kusanto inda nake tsaye har ƙamshin turaren jikinsa ya riga sa isowa gare ni. "Ke yarinya me ye kike yi a nan wajen?". "Ba-ba-ba-ba-ba babu". Na amsa masa a gajarce ina ɗaukar hanyar barin wajen cikin matuƙar sauti kamar zan tashi sama, har ƙafafuna suna haɗewa cikin doguwar rigan da ta gama jikina tsam tamkar tare aka halicce mu. Kaina tsaye na wuce ɗakina na zubu akan tabarma ko kukan na kasa yi illa kawai soyar da zuciyata take yi mini. Ƙirjina yana yi mini wani irin zafi tamkar ana watsa wa mini garwashin wuta ta yadda nake jin zafin yana ratsa wa har ta cikin nama da jijiyoyin jikina. Kan ka ce kabo gabaɗaya jikina ya ɗauki zafi har wani kakkarwa nake yi. "Innalillahi wa inna ilahirin raji'un!". Shi kaɗai na yi nasarar furta wa kafin zuciyata ta antaya cikin cakwakiyar tunani. Tabbas ko rantsuwa na yi ba zan yi kaffara ba wannan muryar Muhammad Taukif ne. Mutumin da ba zan iya mance da ranar da na far tozali da shi akan hanyata ta zuwa islamiyya da kuma kalamansa ba. Shi ne mutum na farko da na taɓa haɗuwa da shi a cikin rayuwata da zuciyata ta sama nutsuwa da kalamansa tun kafin na san halayensa da ɗabi'un balle har na kai ga sanin haƙiƙanin wane ne shi. In dai ta tabbata shi ne baƙon da na ji Saif yana batun zuwansa to ina cikin lukutin yanayi. Na yarce zuffan da ya kwanta a saman goshina kana na tashi na nufi ɗakin Hajiya Babba domin kai mata saƙon da aka bayar da sunanta. Na zauna a ƙasa ina yi mata sannu da hutawa ta amsa tare da zarce wa da faɗin"to ya ya kika gan shi ina fatan ya yi miki?". Na kawar da zancen ta hanyar faɗin"ga wannan ya ce a ba ki". Na miƙa ledodin dukka biyu ta amsa tana faɗaɗa annurin fuskarta bakinta har kunne. "Dukka wannan nawa? Amma mun yi waya da shi kafin shigowar ki ya ce ɗayan saƙon na ki ne. Don haka ga shi ke ma sai ki je ki fantama ki more wa ranki, don na san waɗanda zai ba ki gobe sai sun ci uban waɗannan". Na girgiza kaina"Hajiya ba zan ci ko naira ɗaya daga cikin kuɗinsa ba. Don bai kwanta mini a raina ba, Hajiya kamar yadda kuka sa na yi abin da kuke so ni ma ina da nawa sharaɗin da dokoki. Ba zan fara mu'amala da kowa ba sai wani mutum guda". "Wane ne wannan mutumin?". Na ɗan yi jim kafin can na ce"Sheikh Dawood Gaskiya dokin ƙarfe". Ta dafe ƙirjinta tare da waro idanunta waje"Sheikh Dawood dai da na sani mai tafsirin Alkur'ani?". Na gyaɗa mata kaina alamar e. Ta kallo ni da wutsiyar idonta tana faɗin"ke yarinyar nan watau bayan taurin kai da kafiyar tsiya tamkar kafiran farko har da hauka ma akwai a cikin kanki. Yo in ba hauka ba ta yaya kike tunanin za a iya jawo hankalin irin wannan mutumin da addini da tsoron Allah ya ratsa jini da jijiyarsa". "Ba zai yi wahalar shiga hannu ba Hajiya. Ni ko hanya ayi mini na gan shi ni kuma na yi miki alƙawarin sai na jawo hankalinsa cikin ɗan ƙanƙanin lokaci" Ta yi mini wani irin kallo irin kallon da mai hankali yake yi wa zautacce ta ja tsaki ta tofar tana mayar da hankalinta kan abin da take yi ta furta"bari Aminu ya damu mu yi magana tabbas akwai wani abu da yake yawo a cikin wannan kan nakin". Na cira kai na kalle cike da ƙwarin gwiwa na ce"babu komai a cikin kaina Hajiya, ki ba dama ni kuma na yi miki alƙawarin zan jawo shi har ya shigo hannu. Idan na gaza aikata abin da na furta na yarda ki haɗa mini kayana ki ɗaura mini a kaina ki kora ni daga cikin gidan nan sannan ki haɗa mini da ko wani irin wulaƙancin da kika yi niyya". "Kin san me ye kika faɗa kuwa?". "Ƙwarai kuwa Hajiya". Ta ɗan yi jim kafin can ta ce"shi kenan na ba ki dama amma idan kika kasa jan hankalinsa tabbas zan yaga miki rigar rashin mutumcin a bainar nasi, zan wulaƙanki irin wulaƙancin da ko
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98