Chapter 90
Chapter 90
shi kwanakin sai mafarkinki nake yi da zaran na kwanta bacci wannan ya ƙara tabbatar min da cewar akwai wani damuwa. Don Allah mene ne yake faruwa?". Maimakon na ba ta amsa sai kawai na fashe da kukan da ya yi matuƙar gigita mata tunaninta ta din ga jeranta mini tambayo ɗaya bayan ɗaya. "Subhanallahi! Hashashen zuciyata ya tabbata ke nan wai me yake faruwa ne sanar da ni idan akwai wani matsalan?". "Amira ina cikin matsala shi kenan na jefa kaina da wanda bai ji ba bai gani ba cikin matsalar da ni na yi silar ruruwanta". "Wani irin matsala ke nan?". Take na kwashe komai na yadda muka yi da Saif har da alƙawarin da na yi masa da kuma yadda ya daina ƙira na na tsawon kwanaki biyu, sannan na ƙara da faɗin"jikina ya na ba ni tabbas akwai wani matsalan tun da har na ji shi shuru na tsawon wannan lokacin, sai dai ban san abin da yake faruwa. Idan ma matsalar ce ba na fatan ta shafi kowa mussamman Saifullah da shi ne mutum na farko da ya fara ba n goyon baya kuma ya tsaya mini tsayin daka wajen ganin na cika wannan burin da ya daɗe a cikin rai. Daman sai da Yaya Alhassan ya gargaɗe ni amma na ƙi amfani da abin da ya faɗa mini har umartana ya yi akan na karya memory ɗin amma na yi kunnen uwar shegu". "Innalillahi wa inna ilahirin raji'un! Amatullah me yasa za ki aikata haka? Me yasa ke ba kya jin magana ne sannan ki na da kafiya akan abu. Na yi tunanin kin daɗe da mance wa da babin wannan mutumin a cikin rayuwarki ashe har yanzu ki na nan akan bakanki. Me yasa kike ƙoƙarin butulcewa rahamar da Ubangiji ya yi miki? Kike ta ƙoƙarin ganin kin bankaɗo sirrinki da Ubangiji ya lulluɓe ta a idon duniya?. Allah ya rufa miki asiri ya ceto ki daga rayuwar halakan da kika faɗa ya karkarto da hankalinki zuwa gida ki ka dawo rayuwa cikin ƴan uwanki, su ka rufa miki asiri suka yi miki gata suka ɗauke dukkan ɗawainiyyarki ta hanyar killace ki a cikin gida suna wadata ki da dukkanin abin buƙatun rayuwa. Daga ƙarshe Allah ya ɗaga kimarki ta hanyar yi miki tagomashi da samun mijin da yake shirye ya aure ki, duk wannan tarin ni'iman da Ubangiji ya lulluɓe ki da ita amma kike ƙoƙarin butulcewa". Izuwa yanzu kuka nake yi sosai wiwi don jikina ya gama mutuwa murus na kuma tabbatar wa cewar matsala ce ta hana Saifullah ƙira na ya sanar da ni halin da ake ciki. Sai da ta sallawantar da wasu mintuna kafin ta furta"yanzu dai ki yi haƙuri ki kwantar da hankali, ki yi addu'a Allah ya sa komai lafiya kuma shi ma yana cikin ƙoshin lafiya. Idan kin ga abun ya ci tura to ina mai ba ki shawara da ke ki ɗaga waya ki ƙira shi ki ji halin da ake ciki domin hakan ba laifi ba ne, masu iya magana su na cewa gaida mai gaishe ka ko da kuwa ba zai amsa ba". Sai da na zurfar da zafafan iska daga bakina kafin na ce da ita"na ƙira shi kuma?". Ta katse ni"to hakan laifi ne ko kuma haramun ne aikata hakan? Kin ga wannan jan ajin babu inda zai kai ki sai dai ya sauƙe ki a tashar nadama. Ki ɗauki waya ki ƙira shi ki ji halin da ake ciki alama ce ta nuna kin damu dashi, ko ke da nan ki na tunanin shi da yake ɗaga waya kullu yaumin ya ƙira ki shi bai san ciwon kansa da darajan kansa ba ne?". Luƙus jikina ya yi sanyi ƙalau har na kasa motsa wa daga inda nake zaune. "In sha Allah inna ga shurun ya yi yawa zan ƙira shi". Ban ƙari sa zancen ba ta katse mini hanzari"kamar ya ya? Ai yanzu ya kamata ki ƙira shi son samu m, mu na gama wayar nan ki ƙira shi". "Ki na ganin hakan ne mafita?". A kufule ta ce"ban sa ni ba, tun da ke nan zama kika yi kika miƙe ƙafa ki na jiran ƙiransa, to sai ki yi ta jira daga nan har zuwa ranar da mahadi zai bayyana". Ta gama furzar da zancen kit ta katse ƙiran ta bar ni da sauƙe tagwayen ajiyan zuciya tamkar wacce ta yi wani gagarumin aikin ƙarfi. Rumgume wayar na yi a ƙirjina tare da lumshe idanuna da ruwan hawaye yake zuba daga cikinsu ina yin zantukan na Amira suna yi mini amsa-kuwwa a cikin na'urar naɗan sautina tamkar a lokacin take furta mini su daki-daki. Wani sashin zuciyata ta gaskata abun da Amira ta ce da ni, don haka na ɗauki wayar na lalumo lambarsa na dannan masa ƙira sai dai ƙiran ba ya tafiya, a jere a jere sai da na yi masa ƙira uku amma duk ba ya tafiya. Dole ƙanwar na ƙi na haƙura na ajiye wayar na kwanta ina ta fama da tunani kala daban-daban bacci sai da ya cika cikakken ɓarawo kafin ya iya ɗauka na sai da na makara tashi sallan asubahi, ko da na iddar da sallan sai da na ƙara gwada layin Saif amma har yanzu ba ya tafi, ganin tunanin yana neman ya yi rikita mini kwanyata ya sanya ni ɗauko alƙur'ani na buɗe na soma karanta ban gushe ina yi ba har sai da na ji zuciyata ta sama nutsuwa wani sanyi ya ziyarci sashin ruhina. Ko da na gama karatun zama na yi a wajen na zabga wani uban tagumi. Ban san lokacin da Yaya Alhassan ya shigo cikin ɗakin ba har sai da saurin muryarsa ta ratsa dodon kunnuwana. "Tunanin me ye kike yi haka?". Na yi figigi na dawo cikin hayyacina"na'am ka ce me ye?". Ya kafe ni da ido kafin ya furta"tunanin me ye kike yi?". Na sadda kaina ƙasa"babu komai". "Koma dai mene ne tabbas kawai abin da yake damun ki, ki yi ƙoƙarin yaƙar duk damuwar da yake damunki a cikin ranki". "In sha Allah Yaya na gode sosai". Naira duhu uku ya zaro daga cikin aljihunsa ya ajiye mini a gabana tare da faɗin"ga wannan ki rage wani buƙatunki da shi, babu yawa ki yi maneji da shi". Wani daɗi na ji ya cika mini rai da ruhina har sai da ya haddasa mini tsiyayar da ƙwalla zan yi magana ya dakatar da ni ta hanyar ɗaga nuni hannu alamar ba ya son jin komai daga gare ni. "Ki yi abin da na ce miki kawai". Na buɗe baki zan yi godiya ya kuma katse ni"ba na son wannan godiyan nakin da ba shi da iyaka. Duk abin da na yi miki ki sa a ranki cewar haka daman wani nauyi ne da ya rataya a kaina na sauƙe shi". Kaina kawai na jinjina masa kafin na furta"Allah ya saka da alkhairi ya ƙara buɗi da azurki mai amfani". "Amin" ya Allah ya amsa da shi yayin da yake tashi ya miƙe tsaye haɗe da ƙara faɗin"babu wata matsalar ina fatan dai ko?". "E babu komai Yaya Alhassan, tabbas a zamana da ku kun wadata ni da komai babu abin da na
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98