Chapter 33
Chapter 33
kare ba zai ci ba. Zan tozarta ki irin tozarcin da za ki ƙwammace ina ma uwarki ba ta haifo ki kin zo cikin duniyar na ba. Zan muzanta ki irin muzancin da za ki zaɓi mutuwarki sau dubu akan rayuwarki. Zan jefa rayuwarki cikin ƙunci da takura da har sai kin daina jin daɗin rayuwar duniya sai kin ji a cikin ranki wanda yake kwance a cikin kabari ma ya fi ki ƴanci da walwala". Ba tare da wani tunani ko dogon nazari ba na amsa da faɗin"ma yarda da duk wasu sharruɗan da za ki gindaya mini. In sha Allah sai na jawo hankalinsa". "Kuma babu wanda zai taimaka miki ke kaɗai za ki yi wannan yaƙin. In ma ki ci in ma ki sha ƙasa". Na haɗiye wani miyau mai kauri daga maƙoshina da ya bushe tamkar ƙasar sahara a lokacin zafi. "Na yarda da dukkan sharruɗanki Hajiya". "Tashi ki je na sallame ki" Ban ce da ita komai ba na tashi na bar cikin ɗakin na koma ɗakinmu, na zauna na buga wani uban tagumi ina jin gabaɗaya duniyar ta yi mini zafi na ja numfashi na furzar ya fi sau shurin masaƙi. Hawayen idanuna sun kafe ƙaf tamkar rijiyar da ruwan cikin ta ya kafe na tsawon shekaru masu yawan gaske, sai yanzu ma yarda tabbas wani tashin hankalin ya wuce a yi masa hawaye sai dai kukan zuci wanda ya fi ciwo gami da raɗaɗi. A firgice Anty Sawwama ta farka daga baccin da ya cikakken ɓarawo har ya yi nasarar sace ta duk da girman tashin hankali da damuwar da yake cikin ƙalbinta da ta gama raunana. A tare Yaya Alhassan da Umar suka shigo cikin ɗakin, Umar ya kunna wutan lantarki take haske ya gauraye ko'ina. "Umma lafiya kuwa me ye yake faruwa?". Kasa magana ta yi illa zuffan da ta ci gaba da haɗa wa tamkar wacce aka sheƙa wa ruwa ya yi mata jilif. "Umar samu ruwa yanzu-yanzu". Da sauri Umar ya fita ya je ya ɗebo ruwan ya dawo ya miƙa wa Yaya Alhassan ya karɓa ya yi tufin wasu addu'o'i a cikin ya ba ta ta sha sannan ya shafa mata ragowar a fuskarta, take ta soma sauƙe ajiyar zuciya wani na bin wani. Umar ya riƙo hannunta ya sanya cikin nasa yana murza wa a hankali. "Umma lafiya kike? Ki na jin abin da muke faɗa?". Kanta ta gyaɗa alamar e tana zarce wa da faɗin"lafiya ƙalau wani mafarki kawai na yi da ya tsora ni ainun". "Wani irin mafarki ne haka Umma?". "Umar mafarkin nan dai da na saba yi a duk sa'ilin da na kwantar da haƙarƙarina da sunan bacci". Cike da damuwa Yaya Alhassan ya ce"mafarki kike yi da Kawu Manniru ya zo yana tambayarki amanar Amatullah da ya ba ki ko?". Cikin sanyin jiki ta gyaɗa kanta"ƙwarai kuwa har ta kai ta kawo ba na ƙaunar na kwanta bacci ko da kuwa na minti ɗaya ne. Ban san ina zan je da girman alƙawarin da Manniru ya bar min ba, Amatullah ina kika shiga ne a cikin duniyar?". "Umma don Allah ki rufa mana asiri ki cire wannan damuwar daga cikin ranki kar wani jinyar ya same ki a dalilin hakan. In Sha Allah Amatullah za ta dawo gare mu cikin aminci da yardan Allah, ina ji a jikina duk inda take tana hannu mai kyau kuma ba za ta taɓa aikata abin da Allah zai yi fushi da ita ba, don duk cikinmu babu wanda bai yarda da tarbiyyan Amatullah ba. Ƙaddarar ta ce kawai ta zo a irin wannan sigar wanda babu yanda muka iya ba za mu iya guje mata ba balle mu sauya mata fasali. Har yau ba mu fasa neman ta ba ina da yaƙinin duk wani mai nema watarana zai dace Umma don haka ki kwantar da hankalinki komai zai zo ƙarshe". Numfashi mai zafi ya ja ta furzar daga bakinta kafin ta sama lasisin faɗin"hakan nake fata da buri Alhassan. Allah ya yi muku albarka ya jiɓanci lamuranku yadda kuke ƙoƙarin yi min biyayya ku ma Allah ya azurta ku da ƴaƴan da za su yi muku fiye da haka". Cike da jin daɗin furucinta suka amsa da amin, Yaya Alhassan ya sa Umar ya zuba mata ruwa a cikin buta ta je ta yi alwala kana su ma suka je duk suka yi alwalan, Yaya Alhassan ya ja su limanci suka gabatar da sallan raka'a biyu na nafila suka miƙa ƙoƙon baran su zuwa ga sarkin da ba shi da abokin tarayya, Sarkin da ba ya ce a roƙo zai amsa. Ba su bar cikin ɗakin ba har sai da bacci ya ɗauke ta suka kunna karatun alƙur'ani a waya suka ajiye a cikin ɗakin. Yaya Alhassan ya tisa ta a gaba yana kallon ta tamkar bai taɓa ganin ta ba. Umar ya dafo kafaɗarsa cike da kulawa yake faɗin"Yaya Alhassan ka kwantar da hankalinka komai zai wuce kamar bai taɓa faruwa ba. Watarana sai dai labari". "Umar idan na ce ba na cikin damuwa haƙiƙa ma yi ƙarya mai girma, tun ranar da Amatullah ta ɓace ban ƙara samun kwanciyar hankali ba, ban ƙasa kasancewa cikin daidaitacciyar nutsuwa ba. Kullum a cikin fargana nake da fatan Allah ya sa tana cikin hannu mai aminci". "In Sha Allah za ta dawo gare mu cikin aminci. Ina ji a jikina Amatullah ba za ta taɓa sauƙa daga kan turban da muka san sa ta ba". "Allah ya amsa". "Amin ya Allah yaya Alhassan". Kashe wutar ɗakin suka yi suka koma nasu ɗakin cikin jimami da tarin damuwar da yake danƙare a cikin zuciyoyinsu. [12/3, 2:54 PM] Aeesher: *DAFIN HARSHE* ©️ Maimuna Tijjani Iyam __________________________________________ Page 5️⃣7️⃣ Haka kawai na wayi gari ina ji na cikin wani irin karsashi a jikina, wanda na danganta hakan da karatun alƙur'anin da na yi ta yi bayan na yi sallan asubahi. Na tisa haddan da yake kaina sosai har sai da na ji wani nutsuwa ya lulluɓe mini rai da ruhina. Sai da na ɗebo ruwa na yi wanka na mayar da kayan da yake jikina na duba ko'ina na rasa abin da zan tauna a cikin ɗakin, na gama cinye duk siyayyar da Hajiya Muhibbat ta yi mini kat. Numfashi na ja na fesar kafin na yi shirin tafiya wajen aikin zan fita na ji sautin da ya tirsasa mini tsayawa. "Madam fita za ki yi ne?". Na waigo na yi mata kallo guda tana kwance akan katifarta da ban ma san sa'ilin da ta dawo ba daren jiya sai wayen gari na yi na gan ta cikin ɗakin. "E ko na tsaya za ki aike ni ne?". "To ikon Allah wai na zaune ya faɗi. Abin ai bai kai haka ba, dama na ga muna zaune a ɗaki ɗaya ne akwai haƙƙin maƙwabta a kanmu ai ko?". Na bi ta da wani kallo don har yanzu ban manta zafafan kalaman da ta yaɓa mini ba ranar farko da ta zo cikin ɗakin. "Tambaya kike yi ko neman sani?". "Duk wanda kika ɗauka daga cikin biyun daidai ne". Ban amsa mata ba na ja tsaki na fice daga cikin ɗakin ina jin haushin abin da ta yi mini har
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98