Chapter 8
Chapter 8
lokacin da zaki daina gudun kitso" "Babu rana"ta amsa mata tana Allah Allah a gama cire mata ta tsallake ta gudu ma daga falon. "Tubarkalla ma sha Allah 'yammatan ummu,lallai dole mu caji 'yan samari kudi,irin wannan kyau haka?" Anty madina dake shigowa dauke da babban farantin data yanka musu fruit ta fada tana murmushi,cikin yanayi na nuna jin kunya abinda ke nuni da soma girman widad dim ta boye fuskarta tana dariya "Bafa wasu samari anty Allah" "Aah fada kike wallahi,kowa fa ya sani" wuf tayi ta tashi saboda yadda sauran 'yan uwanta ke juyowa suna kallonta,wasunsu suna mata dariya ne da gaske har zuciyarsu,yayin da wasunsu kallon hassada qyashi da baqinciki ne suke.jifanta dashi,abu guda daya da bai taba dadata da qasa ba,itakam indai zata jita wajen ummunta to komai lafiya lau,takan manta da dukka wasu qananun abubuwa dake tasowa ko kuma faruwa cikin gidan. "Ina zaki sauranki kitso ai" anty madina ta fada,sai ta tsaya tana duban anty madina,fuskarta dauke da zallar quruciya ta narke fuska,abinda ke nuna gab take da fara tara hawaye "Don Allah anty a barshi,nayi bayan sallah" haba ta kama tana kallonta "Anya widad?,ke wannan sumar bata damunki ne?" Dariyar yadda anty madinan ta saki baki ya kamata "Ai shikenan,ki biya ta kitchen,ki cewa yalwa ta baki abincin ki kaiwa ma'aruf" sunan da anty madinan ta ambata sai taji kamar tace mata ba zata aiken ba,amma anty madina tafi gaban haka a wajensu,dukkaninsu suna mata kallon babbar yaya, kasancewar dukka manyan yayyansu mata suna gidajen aurensu,a kaf surukan gidan kuma ita dince mai qananun shekarun da suke iya sakewa suke komai tare da ita,itama kuma ta riqesu tamkar qannen nata. Ba'a son ranta ba ta biya kitchen din ta dauki abincin,ta fito tana dariyar yadda yalwa keta koda kyan qunshin nata,tsakaninta da dukka ma'aikatan gidan qauna ce da soyayya,koda kuwa ba masu aikin sassan nasu ba,idan ka ture wautarta da quruciya da tabara ta goyon kaka,ita din yarinya ce mai matuqar girmama wanda ya girmeta,zaiyi wuya ka sameta da laifin rashin kunya,kai koda laifi akayi cikin gidan da wahala ka samu sunanta a ciki,idan kaji an ambaci sunanta to wata wautar aka tafka,ko kuma ta taba sakalcin nata data saba,wannan ya sanya ummu bata ragawa duk wanda ya tabata,takan ce "Nasa halin kayata fes,duk wanda yace tayi wani abu idan ma sharri ne zan gane ato,nasan me zata aikata,hakanan kuma nasan abinda ba zata aikata ba". Har ta isa qofar dakunansu taji hayaniyar mutane a dakin nasa,da alama baqi yayi abokansa,tsaki taja,ta koma da baya cikin takun da basu fi goma ba,ta tsaya dab da motarsa. Sai data qarewa motar kallo sannan ta matsa kusa da boot din motar ta dora masa abincin a nan,ta kama gabanta hankali kwance ta wuce sassan ummu. Saidai tana sallama a sassan taji nadamar dawowa sassan ta kamata,babu wanda ya gaya mata yazo gidan,da babu abinda zai sanyata dawowa yanzu,sun riga da sun ganta gaba dayansu,harda na'eema diyar anty halimatu da tazo gidan sallah,saboda haka duk wata dama ta komawa ta qwace mata babu ita,sai taci gaba da takawa cikin falon tana tsuke fuska,hadi da sake gayyato bacin rai saman fuskarta,uwa uba dama ga yunwa dake cin hanjinta,taqi abincin wajen anty madina saboda ba cimarta ta dafa ba,tace sai ta dawo wajen ummunta. *_RIGIJI GABJI!_*🔥🔥 *_WANI KAYA SAI AMALE_*🔥🔥🔥 *FITATTUN ZAFAFAN DA BABU NA BIYUNSU*🔥🔥 *JERIN GWANON LITATTAFAI ABOKAN TAFIYAR JUNA MASU MABANBANTAN LABARAI DA FASAHA* *_'YAN BIYAR DIN NAN NE FA_* *_SARAKAN LABARUN_* *NISHADI* *CAKWAKIYA* *GWAGWARMAYA* *BARKWANCI* *TSANTSAR DARASIN RAYUWA* *TARE DA* *ZAZZAFAN SALO NA SOYAYYA MAI RIKITA TUNANI DA TSUNDUMA MAI KARATU CIKIN TAFKIN SHAUQI* *SUN SAKE SHIRYAWA TSAF,DAUKE DA WANI TARAGO MAI CIKE DA LABARAI MASU ZAZZAFAN ZAFI!!!* *KIN SHIRYA MADAM?* *MAZA ANTAYA NAKI KUDADEN KIBI SAHUN AYARIN MATA MASU AJI TA HANYAR BIYAN KUDIN NAKI KARATUN WADAN NAN LITTAFAI KAMAR HAKA* *DAUD'AR GORA* Billynabdul *KI KULANI* Missxoxo *IDON NERA* Mamuhghee *RUMBUN K'AYA* hafsat rano *A RUBUCE TAKE* Huguma *ZAKI IYA BIYA KAI TSAYE TA WANNAN ACCOUNT DIN* 0022419171 Maryam Access bank Saiki tura shaidar biyanki ta wannan number 09033181070 *MASU TURA KATIN MTN KO VTU KUMA ZASU TURA WA WANNAN NUMBER TARE DA SHAIDAR BIYANSU* 09166221261 *Yan nijer 🇳🇪🇳🇪kuma zasu tuntubi wannan number* +227 90 16 59 91 *Muna godiya da ci gaba da zabin zafafa biyar a koda yaushe*🙏🏾🙏🏾 *H U G U M A* *_A RUBUCE TAKE_* (K'addarata) Page 05 *MAAB LUXURY HOME* *_idan kaji gangami akwai labari_* *_SABUWAR DUNIYA CE_* *ALFAHARIN UWAR GIDA* *FARINCIKIN AMARYA* *MAIDA TSOHON GIDA SABO* *DUNIYAR QYALE QYALE* *KAYA NA ALFAHARI DA TAQAMA* *_Ba iya kyawun idanu suka tsaya ba,harma da ingancinsu da kuma qwarkonsu,ka dade kana mora kana kece tsara a tsakanin tsararraku da sauran mutane_* *nasan zaku tambaya ina ne nan?* *MAAB LUXURY HOME* 😊 *Kai daga jin sunan ma babu tambaya* *_duniyar qawata muku gidajenku ku ganku kamar a wata nahiya ko wata duniyar_* *Suna kawo kayan kitchen rankatakaf manya da qananu* *Kayan gado dana parlor* *Kai...suna kawo kowanne nau'in kayan ado na cikin gida* *Karkiyi qasa a gwiwa kuma kada kiyi sake ma dafe,maza garzaya ki nemesu a* _adress dinsu dake No 22 Ahmadu bello way,kano state_ *Ko kuma kuyi order din kayanku kuna daga gida ta shafinsu na instagram* @maabluxuryhome *Facebook* @maabluxuryhome *Ko ku nemesu ta lambar wayarsu kamar haka* 08034631010 *Kyau inganci da rahusa shine takenmu*😊😊🤝🤝🤝🤝 ____________________________ Idanu ya zuba mata yana kallonta,kullum sake canza masa takeyi,tana dada girma tana kuma sauyawa,yana kuma sake jinta a ransa,a haka ta qaraso wajen,amma ko sau daya taqi kallon sashen da yake zaune ma. "Ina yini?" Ta gaidashi tana rusunawa kadan,saidai bashi take fuskanta ba,wani sashe na daban take fuskanta "Lafiya lau widad,ya shirye shiryen sallah?" "Lafiya" ta amsa masa a cunkushe tana duban ummu "Ummu yunwa nakeji,me aka dafa?" Abinda ta tsana ummun ta fara yi wato miqewa,da alama zata basu waje kenan,gamin haka sai tayi wuf ta riga ummun miqewa,daga kai tayi ta kalleta "Ki zauna, na'eema zata kawo miki abincin yanzu" yadda ummu tayi maganar babu wasa saman fuskarta ya sanya ta koma jiki a mace ta zauna tana tara hawaye a idanunta,tana kallonsu suka fice daga falon. Ajiyar zuciya ummun ta sauke bayan barinta wajen,wanan wanne irin abune haka?,me yake faruwa ne?,har yanzu komai yaqi ya canza tsakaninta da mahfood din?'. Cikinsu shi da ita ba wanda ya iya cewa komai,har na'eema ta kawo abincin ta ajjiye ta juya ta fice,a hankali yasa hannu ya jawo abincin gabansa sannan yace "Kamar yunwa naji kince kina ji ko?,matso kici abincin kada ya huce" ko kallonsa batayi ba bare yasa ran zata cin,yayita fama amma qememe tayi biris,dole yaja ledar da yazo da ita zuwa gabansa "Ga kayan sallah nan,da fatan za'ayi kwalliya me kyau" sosai ya sake quleta,don tana da son kwalliya da gayu sai ya maidata wata qwalamammiya?,bashi da aiki sai kawo mata kayayyaki,yadda taji haushinsa sosai a yau din har taji tana qwarin gwiwar gaya masa abinda bata taba gaya masan ba,daga fararen manyan idanuwanta tayi ta azasu a kansa "Nifa bana so,banason komai naka,sannan ma ni ba wani auren dangi da zanyi,ni ba yanzu ma zanyi aure ba,don Allah ka rabu dani,ni.....bana sonka" dai dai lokacin da alhaji mahmud salim mahaifinta yayi sallama cikin falon ya kuma
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119
- 120 Chapter 120
- 121 Chapter 121
- 122 Chapter 122
- 123 Chapter 123
- 124 Chapter 124
- 125 Chapter 125
- 126 Chapter 126
- 127 Chapter 127
- 128 Chapter 128
- 129 Chapter 129
- 130 Chapter 130
- 131 Chapter 131
- 132 Chapter 132
- 133 Chapter 133
- 134 Chapter 134
- 135 Chapter 135
- 136 Chapter 136
- 137 Chapter 137
- 138 Chapter 138
- 139 Chapter 139
- 140 Chapter 140
- 141 Chapter 141
- 142 Chapter 142
- 143 Chapter 143
- 144 Chapter 144
- 145 Chapter 145
- 146 Chapter 146
- 147 Chapter 147
- 148 Chapter 148
- 149 Chapter 149
- 150 Chapter 150
- 151 Chapter 151
- 152 Chapter 152
- 153 Chapter 153
- 154 Chapter 154
- 155 Chapter 155