Chapter 62
Chapter 62
buqata a yanzu irin ya watsa ruwa a jikinsa ya kwanta. Sai data tabbatar tayi nesa da widad daga inda abbas yake sannan ta fito tabar sashen,bayan ta gama mata lallashin qarya da nuna kulawa,wanda qasan zuciyarta cike yake fal da tsana da kuma qiyayyar yarinyar,tana jin kamar ta budi idanu taga babu ita kwata kwata cikin gidan. Latifa ce ta sakata a gaba kan sai taci abinci,da yake a gajiye take,kuma yunwar take ji da gaske saita zauna taci din,tana tsaka da cin ma baccin ya kwasheta ko.hannu bata wanke ba,sai tatifa ce ta gyara wajen ta kuma tasheta ta koma dakinta. Washegari tunda wuri latifa taga kiran ummu,bata yi jinkiri ba ta daga,don dama tana da niyyar kiran nata,bayan sun gaisa widad ta fara tambaya,bata boye mata ba ta gaya mata yadda suka wuni jiya,muryar ummun ta canza,da alama ita kewar widad din tata takeyi,sai tace takai mata wayar. Bacci takeyi amma sanda tace mata ummu ce sai gata ta wartsake sarai,ta karba wayar tana kiran sunanta hawaye na shirin balle mata,tausayinsu duka ya kama latifan,sai ta fice tabar mata dakin bayan taja mata qofar. *Arewabooks: Huguma* KI KULANI miss xoxo DAUDAR GORA Billynabdul RUMBUN K'AYA hafsat rano IDON NERA Mamuhghee A RUBUCE TAKE huguma _sinkin labaran dake dauke da dukkan wasu nau'ikan salo da kuke so_ _masoya ku biya kudinku ta wannan hanyoyin_ 0022419171 Maryam sani Access bank Saiku tura shaidar biya ga +234 903 318 1070 *Masu katin waya ko VTU zaku tura ta nan* 09166221261 *Al'ummar nijer🇳🇪🇳🇪🇳🇪 zaku tuntubi wannan number* +227 96 09 67 63 *Thanks for choosing us*🔥🔥🔥🔥🔥🔥 *H U G U M A* *_A RUBUCE TAKE_* (K'addarata) Page 40 Kuka sosai ta sakarwa ummun,da qyar ta samu ta shawo kanta,cikin hikima da dabara irin ta manya ta dinga lallabata,har sai data gamsu ta kuma ji alamun sakewa da tayi sannan ta fara tambayar ta inda wayarta take,sam ta ma manta da wani batun wayarta,sai a sannan ta tuna tun randa suka iso da nujood ta gama game da ita tace ta saka mata a bedside drawer dinta. Kusan awa guda suka shafe da ummu a waya,har alhaji ma ya karba,Aafiya da rafi'ah da suka shigo suma dukkansu suka karba,sai da kudin ummu ya qare tsaf kiran ya yanke da kansa. Maganganun da sukayi da ummu yasa ta samu sassauci,sai walwalarta kadan ta dawo,ta sauko daga saman gadon da wayar riqe a hannunta da niyyar kaiwa latifa. Tana shirin bude kofar dakin aka turo qofar,sai ta danja da baya tana kallonshi yana shigowa dakin,sanye yake da wani yadi mai taushi,a ido kawai zaka fahimci bashi da kauri,saboda kana iya hangen fara qal din vest din dake jikinsa. Baya ta sake ja tana rakubewa,gabanta kuma yana faduwa,har ya qaraso cikin dakin,ya taka a hankali ya qarasa gaban madubinta ya tsaya "Ina kwana?" Ta gaidashi tana dan russunawa,sai ya maida dubansa a kanta,gaba daya a darare take, baisan me yasa ba,amma ya gama karantar dabi'unta tsaf na rashin sakewa da jama'a,da alama tana da wuyar sabo,shikam tako ta ina baiga ta inda wannan hadin zai zama me alfanu ba,saidai ya sani cewa,abinda babba ya hango,yaro ko ya hau dala da gauron dutse bazai hangoshi ba "Lafiya lau,ya kwanan baqunta?" Ya fadi yana gyara daurin agogonsa,bata san ya zatace ba sai tayi shuru kawai ta sadda kanta,ita kawai Allah Allah take ya fita mata a daki,kada latifa tazo ta gansu su biyu. Sai daya gama gyara agogon sannan ya maida kallonsa a kanta "Shikenan babu wani abu da kuke buqata?" Kai ta gyada masa da sauri,sai ya jinjina kai,ya sanya hannu a aljihunsa ya fidda kudi ya ajjiye mata,don dabi'arsa ce,haka yakewa hafsan,koda suna da komai baya taba fita ya barta hannu babu komai. Ido ta bude sosai ta zarosu waje tana kallon kudin,har ya kusa fita daga dakin sannan ta ankara,da hanzari tace "Don Allah ka dauke,kada latifa ta gani,ni banaso" qaramin murmushi ne ya subuce masa duk da bai shiryawa hakan ba,ya waiwayo yana kallonta da manyan idanunsa "Ba zata komai ba koda ta gani din,daga yanzu duk abinda na baki babu wanda zai miki fada don kin karba,right?" Jikinta a sanyaye ta gyada kanta,don dai ita ta sani ummu na fada sosai gasu basma ma idan wani ya musu kyauta suka karba,tana kallonsa har ya fice daga dakin,sai ta matsa kusa da kudin tana kallonsu ba tare data taba ba. Ja baya tayi kadan jin an sake buda qofar an shigo,latifa ce,idanunta nakan fuskar widad din "Kun gama wayar ne?" Kai ta gyada mata "Eh tun dazu,kinga kudi wai ya bani" ta fada a shagwabe cike da sakarci tana dubanta "Kuma Allah bani na roqshi ba" ta sake fada qwalla na cika mata idanu,dariya kufcewa latifa,ta yarda widad bayan quruciya ma harda sangarta irin ta goyon kaka ke damunta,qarasawa tayi inda take tsaye ta kama hannunta ta riqe "Don ya baki kudi ba komai bane,mijinki ne kinji, komai zai baki hakanan kome zaiyi miki ba haramun bane kin gane?", Kai ta gyada kawai bawai don ta fahimci me take nufi ba "Kuma ya akayi ya fita baki masa rakiya ba?" "Mu jera tare?" Ta tambayi latifa tana fidda idanu,saita jinjina mata kai "Eh mana,bakiga ummu na raka alhaji ba?" Shuru ta danyi tana tunowa,ta gyada kai a hankali "To daga yau kema haka zaki dinga yi masa kinji ko?" Fuska ta noqe,itadai wannan ai iskanci ne,batason irin wadan nan maganganun,haka dai ta gyadawa latifan kai,sannan ta sakata a gaba suka wuce kitchen. A ranar latifa ta fara gwada mata yadda zatayi wasu abubuwa cikin kitchen,kamar tsaftaceshi da inda zata dinga ajjiye komai a muhallinsa cikin kitchen din,yadda zata wanke kwanuka da sauransu. Da yammaci tana falonta a zaune bayan sun gama komai ta dinga jin hayaniyar yara,sai tayi mamaki don bata dauka akwai yara a gidan ba,daga nan ta yaye labulen falon nata,sai ta hangi su mimi suna wasa,tana son fita amma ita komai na gidan d'ari d'ari takeyi dashi,don haka taci gaba da kallonsu ta nan,har suka gama wasansu suka bar wajen. Tun qarfe shida ta gama lafta shinkafarta da miya,ta zubata cikin food flask,bata damu da jimawar da zaiyi kafin ya dawo ba,ko kuma gumin abincin da zai iya komawa cikin flask din ba. Fuskarta ta dauraye kawai,ta cire zanin jikinta ta nemo mahadin rigar ta saka,sannan ta tasa su mimi a gaba suka wuce sashen widad,tayi hakanne saboda ta hanashi dadewa acan,kada ya shiga yaje ya zauna,ko abinda ya faru jiya ya maimaita kansa,cikin ranta tana jin ko a jiyan ma kirsa ce kawai irin tata,ta sani cewa mace duk qanqantarta kaidi ne da ita,kada tazo tana tufka ta baya tana warware. Kan widad na saman cinyar latifa tana kitsa mata kalba tana warewa saboda santsin gashinta,sa'annan kuma ba wani kama mata takeyi da kyau ba,tana mata ne shigen yadda ummu ke mata idan tanason tayi baccin rana,latifan na bata labarun ban dariya,wanda ya sake sanyawa zuciyarta ta kuma saki. Koda tayi sallama hannu bibbiyu latifa ta karbeta,widad kuwa kamar ko yaushe binta tayi da kallo kafin ta zamo ta gaisheta kamar yadda take gaida dukan wanda ya girmeta,hakan kuma sai ya yiwa hafsat dadi,ta sake jin lallai itace a sama,ta dinga bin falon da kallo a fakaice,kafin ta koma
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119
- 120 Chapter 120
- 121 Chapter 121
- 122 Chapter 122
- 123 Chapter 123
- 124 Chapter 124
- 125 Chapter 125
- 126 Chapter 126
- 127 Chapter 127
- 128 Chapter 128
- 129 Chapter 129
- 130 Chapter 130
- 131 Chapter 131
- 132 Chapter 132
- 133 Chapter 133
- 134 Chapter 134
- 135 Chapter 135
- 136 Chapter 136
- 137 Chapter 137
- 138 Chapter 138
- 139 Chapter 139
- 140 Chapter 140
- 141 Chapter 141
- 142 Chapter 142
- 143 Chapter 143
- 144 Chapter 144
- 145 Chapter 145
- 146 Chapter 146
- 147 Chapter 147
- 148 Chapter 148
- 149 Chapter 149
- 150 Chapter 150
- 151 Chapter 151
- 152 Chapter 152
- 153 Chapter 153
- 154 Chapter 154
- 155 Chapter 155