Chapter 27
Chapter 27
tana dubansa shaidan na sake ingizata. Murya a sanyaye rose tayi sallama kafin yace komai ta rigashi "Sorry sir,na kiraka da dare ko?,a baiwa madam haquri" "No,kada ki damu,wani abunne ya faru?" Cikin gurbatacciyar hausarta ta fara masa bayani "Eh....dazun da kuna meeting mimi tayi bacci a office ta yar da dan kunnenta ne,dana duba kuma naga kaman gold ne,so don kada ayita nema hankali ya tashi shi yasa nace bari nayi maka magana" ajiyar zuciya ya sauke yana qoqarin cooling temper dinsa "Is okay,ba damuwa,ki aje wajenki,idan na shigo gobe zan karba,idan ban shigo ba zansa ko samuel ki bawa sai ya kawo" "Okay sir" "Sorry rose,am sorry" "No sir,babu komai fa,nasan bata ganeni bane" "Good night" ya fada yana datse wayar,ya cillata saman gadonsa,sannan ya waiwayo gareta. Bacin ran data gani cikin idanunsa ya sake sanya jikinta yin laushi,bayan ta gane wace rose din "Indai rashin hankali da rashin nutsuwa zaki saka a gaban hankalinki zakita aikata abinda zai kaiki ga nadama mara amfani,tsabar banzan kishinki yasa idanunki sun rufe ki kasa gane wace tayi kiran,rose dince baki sani ba?,kiyi a hankali dani ki fita idanuna hafsat,idan kika kaini bango zan baki mamaki wallahi" can qasan ranta taja tsaki,ya jima yana fadin zai bata mamaki,wanne mamaki kenan,amma a saman fuskarta saita yamutsa fuska tana nuna rashin jin dadi "Ai kasan bansan ita bace,inda na sani ai bazanyi mata haka ba,kuma itama ta yaya zata kira.mutum da aurensa a irin wannan lokaci?" "Bakiji dalilin da yasa ta kira bane?" Ya fada a tsawace ransa na sake baci,har abada kenan ita ba zata gane tayi laifi ba saita kawo nata uzurin? "Ina jaddada miki ki shiga hankalinki,bani da lokacin kule kulen mata,amma idan naso ke baki isa ki hanani ko ki tsaidani ba" ya fada yana nunata da yatsa. Maganar ta doketa itama,to me yake nufi?,taso hasala amma sai ta bagarar,tasan ya fada ne kawai don ya tunzurata ya bata haushi itama,tafi kowa sanin waye abbas din,bata da wannan damuwar don ya fada. Yadda ya banzatar da ita yana shiryawa taji duk ta takura,saita taka a hankali ta isa inda yake tsaye,ta rungume faffadan bayansa da yake shirin lullubewa da riga "Kayi haquri don Allah,kuma na shirya zan bika kadunan" maganar tata tazo masa a bazata,wannan yayi nasarar saukar da fushinsa cikin qasa da second biyar,ya ajjiye rigar hannun nasa,ya waiwayo ya kama hannyenta ya zaunar da ita gefan gadon sannan shima ya zauna. Cikin qwayar idanunta ya sanya nashi sannan ya fara mata magana a tausashe "Bansan me yasa kika kasa fahimatata ba har yanzu,tsahon shekara biyar cikin ta shida,bani da burin da ya wuce naga gidana da iyalina cikin walwala fahimta da kuma qaunar juna,wannan rayuwar ba itace mafarkina ba a rayuwar aure na,inason gidana ya zama very romantic place,matata ta zama tafi kowacce mace iya soyayya tsafta tattali da iya kula dani,wannan shine nawa qarfin gwiwar da zai bani damar tafi da ayyukana yadda ya dace,ya kuma qara kusancinmu,ban takuraki zuwa kaduna saboda radin kaina ba,nayi hakanne saboda na jawo kusanci a tsakaninmu,kusancin da zai sake haifar da sabuwar soyayya da shaquwa tsakanina dake,ni abbas babu wata mace a gaba a yanzu,duk sanda kuma kikaga wata mace ta shiga rayuwata ba shakka gazawarki ne,daga gareki ne,na baki wannan satar amsar,ruwanki ki tare ko ina kiyi gadin qofar,ruwanki ki bada dama a shiga,amma kiyi qoqari mu zauna lafiya" a daren dai anyi abun arziqi,duk da daurewa kawai takeyi,abubuwa biyu ne sukayi mata tsaye a rai,maganarsa ta qarshe da kuma taraddadin barin bauchi ta koma rayuwar kaduna. A dukka hasashenta bata ga wata qofa da ta baiwa wata mace ta shiga rayuwarsa ba,tana kishinsa irin kishin dake matsewa kowacce mace qofar shiga rayuwar mijin wata,tana kaffa kaffa da shigarsa da fitarsa,a gida gwagwadon abinda zata iya tana masa,saidai shi da baya gani ma,amma tana takura a abubuwa da yawa duk don sabodashi,batasan kuma me ya rage ba,me yakeso kuma?. _wannan kenan_ Kwanaki biyu suka qara suka gama shirinsu,har zuwa lokacin yana mamakin abinda ya sauya mata ra'ayin binsa kadunan,saidai bai matsa da sai ya sani ba,tunda zurfafa binciken a wadansu lokuttan ba alkhairi yake haifarwa ba. Ana gobe zasu tafi ya sanyata ta shirya don suje su yiwa hajiya sallama,daga nan kuma ya sauketa a gidansu,tana ta qoqarin danne zuciyarta ne,da kuma bin dukka abinda yakeso,saboda bataso ta bata hanyar data fara sharewa kanta,don antyn ummee tana ta jan kunnenta kan sai tayi juriya,kuma saita kula,don haka ta shirya ta bishi. Hannu bibbiyu hajiyan ta karbeta kamar yadda ta saba,cikin kirki da karamcin nan nata,ba laifi hafsat din kadaran kadaham itama,har suka gama gaisawar suka taba hira sama sama,saita miqe tana duba agogo gami da kallonsa "Inaga ya kamata ka saukeni a gidan,lokacin yana tafiya" kansa ya dauke daga kan jaridar da yake dubawa ya kalleta,har ya buda baki zaiyi magana hajiyan ta rigashi "Gaskiya kam,kuma sallama zakuyi ya kamata ace kinje da wuri don ki samu isashen lokaci,tashi ka sauketa abbas" baice uffan ba,saboda maganar hajiya gaba take da maganar kowa a fadin duniya,banda haka xamanta a gidan yayi kadan sosai,duka duka ko awa guda bata rufa ba,sai ya ajjiye jaridar ya miqe yana daukan key din motar sa ya fice,ta yiwa hajiya sallama,ita kuma tasa muneera ta bita da kayan amfanin kitchen data tanadar musu,kamar su kuka kubewa daddawa kanwa da yaji da sauransu,saboda tasan abbas din ma'abocin son tuwo ne,a halayya kuma irin ta hafsat din babu lallai ta tsaya tunanin tanadarsu,ta bisu da addu'a suka lafiya,qwaqwalwarta fal mamakin yadda hafsat din ta sauya ra'ayi,duk da bata tsaya tambayar abbas din ba. *********** Gab da sallar magariba hajjaa ta iso gidan hajiyan,cike da gajiya da kuma farincikin gama cooking classe din da sukayi na kwanaki biyar,wanda dai dai yake da na kwanaki sittin a wata makarantar,ita kanta tasan ta qaru over da abubuwa masu yawa. Tana shiga ta miqawa nujood jakarta ta daura alwala kawai sannan ta shige falon hajiyan,ta zauna suka gaisa hajiyan tayi mata sannu,sannan ta kira muneera kan ta zubo abincin dare suci kafin su wuce "Hajiya da kin barsu,yauma kafin na fito sai da nayi girki" "Me yasa kike nuna wa gidan nan kamar ba gidanku bane hadiyya?,kinga muneera zubo,idan ba zata ci ba yaran zasu ci,xakuci ai ko widad?" Tayi tambayar tana kallon widad,wadda keta faman hada kayansu a jaka tana kammalewa. Murmushi ta saki tana sadda kanta qasa,ba tare data amsawa hajiyan ba "Au,babarki zaki goyawa baya kenan,sai faman hada kaya kike,kamar dama kin gaji da zuwa gidanmu " wannan karon har sai da haqoranta suka fito tana dariya cike da kunya "Ba haka bane hajiya,muna ta saki aiki fa kwama biyar din nan,kema zaki huta" maganar yarinyar saita burgeta,ta kuma sake saka mata qaunarta a zuciyarta,haka kawai cikin kwanakin taji yarinyar ta kwanta mata,tana kuma burgeta,saboda taga bambancin dabi'a tsakaninta da sauran yara,sau tari takan zauna nan kusa da hajiyan suyita hira abinsu,widad din najin hajiya kamar ummunta,idan tana tare da ita sai taji kamar ummu,tana debe mata kewarta sosai. "Ni ai ban gaji da ganinku ba widad" "To mu zauna hajiya?" Ta tambayeta cike da quruciya,murmushi hajiyan ta sake,ta waiwaya tana duban hajjaa dai dai sanda ta sallame daga sallar "nikam da zaku bani widad da nayi murna
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119
- 120 Chapter 120
- 121 Chapter 121
- 122 Chapter 122
- 123 Chapter 123
- 124 Chapter 124
- 125 Chapter 125
- 126 Chapter 126
- 127 Chapter 127
- 128 Chapter 128
- 129 Chapter 129
- 130 Chapter 130
- 131 Chapter 131
- 132 Chapter 132
- 133 Chapter 133
- 134 Chapter 134
- 135 Chapter 135
- 136 Chapter 136
- 137 Chapter 137
- 138 Chapter 138
- 139 Chapter 139
- 140 Chapter 140
- 141 Chapter 141
- 142 Chapter 142
- 143 Chapter 143
- 144 Chapter 144
- 145 Chapter 145
- 146 Chapter 146
- 147 Chapter 147
- 148 Chapter 148
- 149 Chapter 149
- 150 Chapter 150
- 151 Chapter 151
- 152 Chapter 152
- 153 Chapter 153
- 154 Chapter 154
- 155 Chapter 155