Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 103

Chapter 103

A Rubuce Take Book 1 Complete Hausa Novel – Widad and the Secret of House 1,322 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

har aka gama,motar nada wajen zama biyu,sai wajen zaman driver,hajiya ce ta fara shiga seat din da yake da maqotaka dana driver "Bazan shige ciki ba abbas saboda qafata" "Ba matsala hajiya yayi hakan" yana shirin yima muneera magana kan ta shiga gefan hajiya sai weedad ta fara takowa,tsaf ya fahimci abinda take shirin yi,jiya kawai dama kawaici yayi mata,a yanzun sai yayi kamar bai ganta ba,sai da tazo daf dashi ya sanya hannunsa ya riqe hannunta da kyau,baiko waiwaya ba bare kayi zaton ya riqeta din,cikin sauri ta daga kai tana kallon fuskarsa,yasha muur da kyau,baiko kallon sashen da take kamar bashi bane ya riqeta. Gyaran murya kadan yayi sannan ya kira muneera yace ta shiga gefan hajiya "Saura ki saki baki kima mutane bacci ki barta da kallon hanya" murmushi ta danyi "Bazanyi ba uncle in sha Allah" hannu yasa ya rufe murfin motar,ya bude seat din baya sannan ya waiwaya ya kalleta. Cikin sa'a itama shidin take kalla, idanuwansu suka hadu waje daya,har cikin jininsa sai da yaji wani abu mai kaifi ya saukar masa,ya kuma baza saqonsa zuwa kowanne sashe na jikinsa,ya sake dawo masa da sweet memorie dinsu na shekaran jiya,wannan ya sake sanyawa gaba daya jikinsa ya amsa "Shiga" ya fada da mugun sanyi,narke fuska tayi sannan ta matsa ta shige yabi bayanta,ya maida murfin ya rufe sannan ya yiwa samuel da suka saba yin tafiyar dashi magana kan ya tashi motar suje. Gefe daya na motar ta rakube,gaba daya fuskarta a narke take,kamar wadda ke jiran qiris ta sanya masa kuka,yi yayi kaman bai fahimta ba,sunata hirarsu shi da hajiya,har taji shurun widad din yayi yawa "Widad ko.tayi bacci ne?" Hajiyan ta tambaya ba tare data waiwayosu ba,sai sannan ya juya inda take zaunen,tausayi ta bashi da kuma dariya amma ya danne,suna hada ido sai hawayen da take maqalewa ya sauko,ya miqa hannunsa ya lalubo tafin hannunta,duk da yadda take faman boyonsa ya sanya shi cikin nasa,sannan a hankali ya janyota zuwa kusa dashi ya hade duk wata tazarar dake tsakaninsu sannan ya amsawa hajiyan a ladabce "Idonta biyu hajiya" "Au to madalla". Tun basuyi nisa da tafiyar ba bacci ya dauke hajiya,muneera ce kawai ta rage wadda taketa game da wayar hajiyan,har a sannan tafin hannunsa yana cikin nata yana yamutsawa,santsi da laushinsa ke haifar masa da wata kasala ta daban,maqoshinsa gaba daya ya bushe,ya kalleta ta gefe "Bani ruwa" ya fada a taqaice,kamar jira dama takeyi ta zame hannunta daga cikin nasa,saidai kafin ta gama zamewa ya maida hannun cikin nasa,ta juyo suka hada ido ya kada mata kai "Zan dinga hukuntaki fa" yayi maganar can qasa da wata irin gajiyayyar murya,sai tayi narai narai da ido tana kallonsa,ya girgiza mata kai da sauri "Kinayimin kuka zan cinye idanun" yadda yayi maganar with seriousness ya sanya mata dan jin tsoro,sai ta kifa kanta saman cinyarsa,abinda ya sanya numfashinsa yin qaura na wucin gadi,ita kuma ta tura kanta da kyau tana son goge hawayen daya fara fita kada ya gani. Da sauri ya saka hannunsa ya daga fuskartata,idanunsa suna rurrufewa,bugun zuciyarsa na fita da sauri "Ya isa....banaso.....idan nace ki bari ki dinga cewa to,understand?" Kai ta gyada masa "Good,bani ruwa" a hankali ta dauko masa ruwan,duk da yadda jikinta ke rawa,shima ya lura da hakan,sai ya sakar mata hannun ya karba ruwan,ya balle gorar ya sanya bakinsa bayan yayi bismillah ya soma sha. Tas ya shanyeta,ya maida numfashinsa,ya juya kadan suka hada ido,tunda ya fara shan ruwan ta zuba masa ido tana mamakin yadda yakeshan ruwan,kamar wanda ya jima baiga ruwa ba,suna hada idon ta dauke kanta,ya saki murmushi,ya gama karantar komai daga qwayar idonta "Zo kiji" ya kirata can qasa kamar yadda suke maganar tun daxu, saboda muneera da hajiya da suke cikin motar,bata musa ba ta matso dab dashi,sai yasake hade hannayensu waje daya yana kallonta "Menene auratayya?" yayi mata tambayar kai tsaye,tambayar da ya jima yanason mata ita,tambayar data sakata rufe idanunta gam lokaci guda,zuwa yanzu koda batasan ainihin me yake nufi ba,daga karance karancen data fara ta fuskanci wani abune mai girma,wani babban alaqa ce babban gini da kuma qatuwar dangantaka tsakanin namiji da mace,zuwa yanxu kuma tambayar ta girmi tunaninta,ta kuma haifar mata da wani jin nauyi da kuma kunya. Yadda ya rutsata da ido haka tabar idanun nata a kulle,wayyo Allah kawai take fada a ranta,itadai wannan iskancin ya fara isarta,inda ya barta kusa da hajiyar da duk haka bata faru ba,sai ya saki murmushi yana sakar mata hannyenta,bai sake cewa komai ba,haka itama,a haka har baccin ya soma fusgarta,sai yayi mata makari da manyan kafadunsa,sanda baccinta ya fara nisa kwance tayi bisa kafadun nasa ba tare data sani ba,wannan ya bashi wani irin yanayi mai dadi sanda suke keta dazuzzuka,yayin da tayi wani bacci mai dadin gaske bisa kafadun nasa. Cikin ikon Allah suka iso bauchi lafiya,yayi yayi da hajiya ta fara sauka gidansa amma tace sammm a gidanta zata sauka,dole haka ya wuce da ita gida,sanda suka isa gidan akwai mutane,yaranta matan su uku duka suna gidan su da yaransu,sun gyare gidan sunyi duk wani abu na tarbarta,kowa kallon widad yakeyi,cikin watannin ta sake girma da cika,tayi wani fresh,abinka da farra fata idan ya samu hutu,cikin girmamawa ta gaida kowannensu,tunda dui cikinsu babu sa'arta,sun haifeta ma,qaramar cikinsu ce take ganin zasuyi sa'anni da anty deena. Ina ka saka ina ka aje suka dinga yi da abbas din,shima da yake mai.kirki ne kuma na mutane sai yadan zauna shima a cikinsu kusan awa daya,lokacin har maqota da sauran matan kawunnansa sun fara shigowa yuwa hajiyan barka da zuwa,kusan kowa ya shigo idonsa akan widad "Amaryar abbas ce?" Haka suke tambaya,kowa da abinda ke cikin ransa,ya kusa shafe awa daya sannan ya miqe da zummar tafiya "Dauko mayafinki ku wuce widad kinji,sannunki kema da qoqari ansha hidima,Allah yayi albarka ya bada zuri'a ta gari" baki baba usaina ta tabe,matar daya daga cikin kawunnansa,wadda suna da 'yar alaqa da hafsat din,fuska ta marairaice wa hajiyan,qasa qasa take gaya mata "Don Allah hajiya a barni a nan na kwana" can qasan ranta tana fargabar yadda yake liqe mata,a yanzun baya jin shakkar tabata,idan mommy hafsat ta gani tace mata meye?,gwara tana nan din,basu hadu ba bare ta gani. "Yaa abbas,ka barta zuwa anjima din kamar haka takeso tace ko?" Qanwarsa ta fada wadda ke kusa da hajiya,ta kuma ji abinda take fada din "Idan ka fito saika biyo ku tafi,idan ma baka zo din ba zan sanya a rakota" hajiya ta qara masa bayani. Idonsa ya maida kan widad din data wani lafe a gefan hajiyan,suka hada ido sai ya dauke kansa,itama janye nata idanun tayi cikin ranta tana jin kamar ta tsira,ya gyada kai "Shikenan hajiya,a huta lafiya" "To Allah yayi albarka,a gaida kishiyoyina" a hankali ya juya ya fice daga falon "Tirqashi" baaba usaina ta fada,yaaya bara'atu ta daga kai ta kalleta "Baaba usaina lafiya ko?" Baki ta tabe a fakaice,amma a zahiri sai tadan murmusa "Ina ganin rashin kunya irin ta yaran zamani,kema banda abinki hajiya kibar masa matarsa su wuce mana" "A'ah gwara ta zauna a gaisa sosai,aita kwan biyu dama bataxo ba" hajiya ta amsa mata cikin bagarar da zancan,don batason dogon zance. Sai da suka tsaya a hanya ya sake yin siyayya

Table of Contents

Chapters

155 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138
  139. 139 Chapter 139
  140. 140 Chapter 140
  141. 141 Chapter 141
  142. 142 Chapter 142
  143. 143 Chapter 143
  144. 144 Chapter 144
  145. 145 Chapter 145
  146. 146 Chapter 146
  147. 147 Chapter 147
  148. 148 Chapter 148
  149. 149 Chapter 149
  150. 150 Chapter 150
  151. 151 Chapter 151
  152. 152 Chapter 152
  153. 153 Chapter 153
  154. 154 Chapter 154
  155. 155 Chapter 155
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});