Chapter 123
Chapter 123
fatarta datayi wani fresh. Qwarewa tayi, saboda gaba daya bata ji takunsa ba,ya sanyata a kafadarsa yana dan dukan bayanta harta daina tarin sannan ya janye jikinsa kadan "Ki dauko komai?,samuel yazo xamu wuce" kai ta jinjina masa alamar eh,sai ya miqa mata document din hannunsa,ya ja mayafin dake kanta ya soma nada mata shi. Baya ya danja ya kalleta,she looks very gorgeous,sai yaji kishinta yayi bala'in kamashi,har yaji kamar dama bai kira samuel ba. Hannunta ya kama ya isa da ita gaban wani dan fashion mirror dake maqale cikin falon, murmushi ya subuce mata,ya akayi ya iya rolling haka?,ta cikin idanunta ya karanci tambayar dake cikin zuciyarta,sai ya saki murmushi "Mimi da nawwara" a taqaice ya amsa mata amma ta gane,saita kauce gefe daya saboda kallon da yake jifanta dashi ta madubin yana mata nauyi da yawa. Kafin su fita ya kira samuel ya masa aiken dole,wai fita dan kantin dake kusa da gidan ya karbo kasa biro,kafin ya dawo suna cikin motar,yana isowa yace ya aje masa wajensa zai karba,don kada ma.ya juyo har ya ganta,ya amsa masa a ladabce ya kunna motar suka fice daga gidan. Tun basuyi nisa ba bacci ya soma fusgarta,sai yayi mata majingina da kafadarsa sosai,ya lalubo hannunsa ya sanya a tafin hannunsa ya hadesu waje daya. Kusan awa biyu ta kwashe tana bacci,sanda ta farka saita janye jikinta daga nasa cikin jin nauyi,ya murmusa kadan yana dubanta "Kin more min kafada,sai naci tararki" kafada ta noqe tana dariya cikin jin kunya. Awa biyu da rabin suka shiga garin bauchi,sai tadan dubeshi har yanzu hannunsa yana cikin nata "Gidan hajiya zaka saukeni" ta fada qasa qasa,don sam sai taji bata qaunar zuwa gidan. Waiwayowa yayi ya zube mata manyan fararen idanunsa yana kallonta qasa qasa,cikin zuciyarsa yake son qiyasta yadda hakan zata faru,sai kuma ya girgiza kansa a hankali kafin ya dauke idamunsa a kanta "Ba yau ba" ya fadi kansa tsaye,don baya jin zai iys nesa da ita "Don Allah uncle" ta fada a mugun shagwabe kamar zata saki kuka "No,Baby" komawa tayi ta lafe jikinta a sanyaye tayi shuru,tafison gidan hajiyan,tafi qaunar zama a can,saita fara sharar hawaye kafin ta sake masa siririn kukanta. Idonsa ya lumshe yana jin wani abu mara dadi yana taba zuciyarsa,irin abinda bai tana jin kamarsa ba,duk da dama shi din kusan weak point dinsa kenan "Is okay" ya fada yana sanya hannunsa cikin nata,sannan ya bawa samuel umarnin canza titi zuwa titin da zai kaisu unguwar gida dubu. Ajiyar zuciya ta sauke,ta sake lafewa tana dan sakin murmushi "Na gode" waiwaya yayi a hankali ya kalleta,sai ya sanya hannu yaja hancinta "Karkiyi saurin godemin,don idan munje ba lallai bane na barki ki kwana ba" baki ta tura gaba,sai ta kwantar da kanta ba tare da tace masa komai ba,ya sake sakin qaramin murmushi yana kallon hanya hadi da matse hannunta sosai kuma a tausashe cikin tafin hannunsa,can qasan zuciyarsa yana jin wani abu mai qarfi a kanta yana sake ginuwa. Ita ta fara shigewa gidan hajiyan cike da karsashi, zuciyarta fal farinciki,don kusan wata guda kenan bata zo ba,zuwanta na qarshe har suka koma batazo gidan ba. Su biyu ne falon,ita da gwaggwo fanteka suna taba hira,sun gama cin abinci kenan tayi sallama,sosai farincikin dake fuskar hajiyan ya bayyana,ta amsa sallamar tana cewa "A'ah,mutan kaduna.....irin wannan ba zata haka?" "Aiko dai,haka amaryar abas din ta fara canzawa,ah lallai yarinya taji kiwo" gwaggwo fanteka data kama haba cike da jin wani abu a ranta me kama da qyashi qyashi ta fada,maganar da ta yiwa widad din nauyi,karon farko da kunyar hajiya ta kamata,musamman da ta tuna abinda ya wanzu tsakaninta da abbas din,sai take ganin kamar ma kowa yana iya karantar hakan,don haka tun daga dan nesa dasu ta zube tana gaidasu. Cikin kulawa hajiyan ta amsa, gwaggwo fanteka kuwa ta zuba mata ido tana kallonta,sosai widad din ta canza,ta fara cika ta kuma yi kyau abinta,ta amsa tata gaisuwar tana sauke numfashi hadi da gyara zamanta "Kundai tafi kunbar uwar gida da jiran gida ko?" Ta jeho widad da batasan ma kan asalin abinda kae faruwa ba tambaya "Uhmmm,ina ruwan widad,ita da batasan komai ba akai" hajiya tayi saurin karbar zancan "To ai shikenan,Allah ya kyauta" ta sake fada tana gyara zamanta,dai dai sanda abbas yayi sallama ya shigo parlor din,qaninsa muneer yana biye dashi da babban ledar da muddin da ransa da lafiyarsa baya gaza shigowa da hajiyan tashi ita. Washe baki gwaggwo fanteka tahau yi tana sake gyara zama,lallai yau din ta shigo a sa'a,tasan cewa shar da ita zata fita,harda ita wajen marabtar abbas din,ya duqa ya gaidasu cikin girmamawa sannan ya koma ya zauna sosai daura da hajiyan tasa. Miqewa gwaggwo fanteka tayi tana cewa "Ni bari na wuce gida,naga la'asariya ta kusa" "Ki tsaya mana ki karbi tsarabar taki?" "A'ah haba,kya dai aiko muneera ko muniru ya kawomin,yallabai Allah ya huta gajiya" hannu abbas ya sanya a aljihunsa ya fidda sabbin 'yan dubu dubu ya miqa mata,tasa hannu kuwa ta amshe babu tayi tana zuba godiya. Nan falon hajiyan yayi zamansa suna hirar yaushe gamo,duk danda widad dake kitchen tare da muneera ta gifta sai taji ranta ya mata sanyi,ta kuma sake godewa Allah,kallo daya ta yiwa abbas din harma da widad din ta karanci akwai wani gagarumin sabon canji cikin rayuwarsu,walwalar abbas din ta qaru,idan ma ba idonta bane ke mata gizo har 'yar qiba taga yadan qara,abinda bata taba gani a tare dashi ba,sannan duk sanda widad din zata gifta idanuwansa suna biye da ita,kamar yadda itama duk sanda ta ratso ta falon saita saci kallonsa. Ana idar da sallar la'asar yayi shirin wucewa gida,yace ta fito su wuce,amma saita sakar masa darunta tana maqale wuya,idan zata shekara tana masa wannan shagwabar yanason gani,ba kuma zai gaji ba,tilas ya haqura ya barta bayan hajiya ta sanya baki,ya wuce gidan shi kadai,amma cikin jikinta da zuciyarsa duka sai yakejin wani iri babu dadi,kamar ya baro wani b'ari ne na zuciyarsa a wani waje. *H U G U M A* *_A RUBUCE TAKE_* (K'addarata) *Arewabooks:Huguma* Page 81 Kamar ko yaushe a harabar gidan ya cimma yaran,sunata wasan qasa sunyi futu futu dasu,qasa har saman kansu,amma hakan bai hanasu murnar ganin juna ba,ya tsugunna ya kwashe abinsa sunata masa surutu yana kerbewa. Dab da zai shiga sashen nata ta fito,sanye da atamfa dinkin doguwar riga,tayi daurin ture kaga tsiya,duka gashinta da ba kasafai ta fiya son kitso ba ya fito abinsa ta qasan daurin,hannun brassiere dinta daya fito ta kafadarta ya sake muzanta shigar tata,atamfar anko ce da sukayi biki tun shekaran jiya,kuma tun shekaran jiyan take jikinta bata cire ba,sam batayi tsammanin zuwansa a yau din ba,shi yasa ta saki jiki ya sheqi baccinta,bata jima da tashi ba ta biyo sahun su mimi jin shuru ba motsinsu tun dazun. Tare hanya tayi tana masa sannu da zuwa hadi da karbar jakar hannunsa,bata son ya shiga sashen nata,saboda ita kadai tasan irin badaqalar daya kwasa ba,don hatta da uniform din mimi yana zube a falon da school bag harma da tsadajjen lunch box dinta daya siya mata "Mu qarasa sashen naka,dama fitowar da nayi gyarawa zanje nayi" ta fada tana sake kankane hanyar. Bai musa mata ba,don a yadda takeyin din
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119
- 120 Chapter 120
- 121 Chapter 121
- 122 Chapter 122
- 123 Chapter 123
- 124 Chapter 124
- 125 Chapter 125
- 126 Chapter 126
- 127 Chapter 127
- 128 Chapter 128
- 129 Chapter 129
- 130 Chapter 130
- 131 Chapter 131
- 132 Chapter 132
- 133 Chapter 133
- 134 Chapter 134
- 135 Chapter 135
- 136 Chapter 136
- 137 Chapter 137
- 138 Chapter 138
- 139 Chapter 139
- 140 Chapter 140
- 141 Chapter 141
- 142 Chapter 142
- 143 Chapter 143
- 144 Chapter 144
- 145 Chapter 145
- 146 Chapter 146
- 147 Chapter 147
- 148 Chapter 148
- 149 Chapter 149
- 150 Chapter 150
- 151 Chapter 151
- 152 Chapter 152
- 153 Chapter 153
- 154 Chapter 154
- 155 Chapter 155