Chapter 48
Chapter 48
rufe fuskarta anty madina na tayata dariyar "Zankadi,bude idonki ki gani" saita bude idon da sauri,ba qarya wayar ta hadu,take taji murnarta ta qaru,qaunar wayar kuma ta shigeta,suna shirin kunnawa momma tayi sallama falon "Wa'alaikumus salam,qaraso momma,duk sun cika falon" anty madina ta amsa tana qoqarin tattare kudaden waje guda "Wannan sabbin kudi fa,ko na liqi ne da kikayi canji?,aisai ki adana abunki,bikin da babu ko kidan qwarya bare DJ,kamar wata amaryar buzuzu" "Uhmmm,momma kenan" anty madina ta fada tana dariyar yaqe "Albarkar aure ai ake nema,bare widad ma nawa take?,ina qawayen ma bare ace za'a zauna yi mata irin wannan bidi'ar?,ni ban canzo kudin komai bama,angonta ne ya bata hade da wayar?" Sai a sannan idanunta yakai kan wayar "Kai!" Ta fada cikin ranta,tasan wayar fes,irin wayar da deena tace yallabai(mijinta) ya kawo mata tsarabarta ne daga india a wannan satin daya dawo daga course daga can "Tofa,da gamo da kasawa,kada fa muna nan mun shanya baki muna kallonta yarinya qarama amma ace har tasan komai,kodai ta bada wani abune aka bata wannan tukuicin haka?" Momma din ta fada tana kama baki, zuciyarta cike fal da qyashi da baqinciki,don ko yanzu data baro sassanta maganar da suka gama kenan da batulu matar babanta da 'yan uwanta da basu tafi ba,duka dai akan widad din,suna ganin komai anyi mata fiye dana 'yan uwanta,ana kuma wuce makadi da rawa a kanta saboda tana da daurin gindin ummu,sun manta kowanne aure da irin nasa nasabin yake zuwa,labarin lefe data samu,manyan mutanen da suka halarci daurin auren da kuma kayan da aketa hadawa za'a tafi jere dasu kawai sukeyi,banbamcin da ake nuna mata akan nasu 'ya'yan yayi yawa. KI KULANI miss xoxo DAUDAR GORA Billynabdul RUMBUN K'AYA hafsat rano IDON NERA Mamuhghee A RUBUCE TAKE huguma _sinkin labaran dake dauke da dukkan wasu nau'ikan salo da kuke so_ _masoya ku biya kudinku ta wannan hanyoyin_ 0022419171 Maryam sani Access bank Saiku tura shaidar biya ga +234 903 318 1070 *Masu katin waya ko VTU zaku tura ta nan* 09166221261 *Al'ummar nijer🇳🇪🇳🇪🇳🇪 zaku tuntubi wannan number* +227 90 16 59 91 *Zafafa biyar kadai keda sinqin nau'ikan kalar labarun da kukafiso jimilla a lokaci guda*🤝😄 *Thanks for choosing us*🔥🔥🔥🔥🔥🔥 *H U G U M A* *_A RUBUCE TAKE_* (K'addarata) *Arewabooks: Huguma* Page 31 Maganar ta qonawa anty madina rai sosai ta kuma bata haushi,sannan sai taji.maganar kamar tayi girma a kunnen widad,tana girmama dukka faccalolin nata saboda dukkansu sun girmeta,ita kadaice qarama a cikinsu,shi yasa take musu kallon yayunta,don haka ta tattara wayar da kudin ba tare data gama saita wayar ba ta miqawa widad "Kaiwa ummu ta gani ta adana miki,anjima zan shigo saina qarasa gyara miki" karban kayanta tayi ba tare data ma fahimci maganar me momma takeyi ba,ko baqincikin dake manne a ranta ba ta qara gaba cikin doki da zumudi. Da kallo momma ta bita sannan ta tabe baki "Kinga yarinya sai rawar kai take,Allah yasa bai lasa mata zuma a baki ba ya barmu da....." "Kai.....kai momma" anty madina ta fada tana kama kai fuskarta na nuna zallar rashin jin dadi "Wannan maganganun sunyi girma da yawa fa" "Wanne girma?,a wajen wa?, yarinyar da yanzu keda ita dukka matsayinku daya?,tabdijan,kina wasa da yaran yanzu,ni da rannan naji tana gaya musu zata tafi gidanta itama ta dinga girki irin nasu anty dina,tayi.bacci a gadonta?,to billhuwallazi kada ma kiyi mamaki idan akace miki ya gama lallatseta kafin ya tafi,ko ya fara buda hanyarsa" "To haka muke fata,aiba haram bane,me zan baki?" Tayi mai gaba daya saboda maganar ta soma isarta "Yauwa,mai zaki zuba mana,nawa ya qare gaba daya jiya suka zube shi a dambu" karbar robar tayi kawai ta miqe ta wuce store dinta dake manne a kitchen, cikin ranta tana tur da Ala wadai da irin wanna dabi:ar tata,banda abinta meye abun kishi da widad?,me za'a yiwa baqinciki akanta,yarinyar da bata da maraba da marainiya?,bata taka muku ba bata zubar muku ba amma kunbi kun qwarzabi kanku a kanta,batama san me suke ba,bata wani ganewa halinsu idan ba takurata sukayi da kyara ko hantara ba,shine zaka ga ranta ya baci saman fuskarta,ko kuma ta janye jiki daga gurin ba kuma zata dawo nan kusa ba. °°°°°°duk yadda take ta so ta tursasata kanta da zuciyarta.....ta tafi da zuciyar tata da ruhinta bisa doron shawarar da anty ummee ta dorata akai amma abun yana ta neman yaci tura,daga sanda labarin AN DAURA auren mijinta abbas sa wata gaba daya ta birkice,zuciyarta nata gaya mata anya mafita ce anty ummee ke bata?,ta tsaya kawai tayi masa hauka,tayi tawaye ta tada masa hankali har ya aje auren,wannan shine shawarar da mafi rinjayen sashe a zuciyarta ke bata,yayin da wani sashen yake gaya mata ta haqura taci gaba da tafiya a haka,saboda taga alfanun hakan,ta samu alkhairai masu yawa daga jikin abbas din. A ranar ita daya ce a gidan,ta tura yaran gidansu,ko wankan arziqi bata samu yi ba bare ta kintsa gidan,sai ta zauna dirshan,ta soma bin status din dukkan wanda tasan ya tafi kano daurin auren. Irin kyan da taga abbas yayi cikin dukka hotunan,da yadda taga fuskarsa shimfide da qayataccen murmushin nan nasa sake matuqar burgeta da daukar mata hankali sai taji ta sake birkicewa,saidai kaf hotunan bataga fuskar amaryar da taketa lalube ta gani ba. Jefa wayar tayi gefe tana rufe fuskarta da tafin hannunta,kuka ya subuce mata,abbas ya cuceta,kuma ko meye zaiyi mata bazai taba wanke kanshi ba,ba haka tasan abbas ba,bashi sa kallon mata ko kadan,bai shiga shirginsu kwata kwata,ya akayi wata mace ta gilmawa idanunsa har ya qyasa yaji yana son yin tarayya da ita?, macen ma yarinya qarama kamar yadda aketa bata labari?,ya zuwa yanzu ka ta fara tantamar anya yarinyar ce kamar yadda aka ce?,tasan tsarika da zabin abbas,ta yaya zai aura yarinya?. Wayar ta jawo da sauri ta cireta daga flight mode din data saka mata tun jiya,dai dai lokacin da saqon abbas ya fado wayarta bayan ya gaji da kiranta yana jin wayar a kashe,tsaki taja tayi fatali da saqon ta shiga duba number anty ummee. Bugu daya ta daga,kamar mai jiran kiran nata dama,kuka kawai ta saka mata,tayita yi har kudinta ya qare kiran ya katse,anty ummee daga can inda take zaune a falonta taja tsaki "Kuka ma yanzu kika fara,kishiya wasace,shegen son abun duniya irin naki,inda kin bada dama 'yan uwanki sunzo gidan an dan zauna dake aida an debe miki wannan damuwar,amma don kada mutum yazo yaci abinci da nama kika hana kowa zuwa,kyaci takaicinki ke kadai" ta fada tana bin kiran nata daya katse. "Anty ummee anya zan iya?,wallahi bakiji abinda nakeji a qirjina ba" ta fada cikin muryar kuka "Ke dole ki daure fa,saboda ribar ciki tafi rashin ribar yawa,wannan ce kadai hanya guda daya da zaki zauna salamun salamun a gidan,kuma kowa yayi miki.biyayya ba tare daya shirya ba,wannan itace kadai hanyar da zaki tankwabar da auren ma gaba daya ba tare da kowa ya zargeki ba,amma fa saikin jure sai kuma kin daure,in kikai haka gaba zaki godemin" Shuru tayi tana nazarin maganganun a kanta "Ki kwantar da hankalinki,idan kin samu lokaci kizo zan sake shirya miki yadda komai zaici gaba da tafiya" ta sake gaya mata bayan sunyi maganganu masu yawa da suka dan saka
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119
- 120 Chapter 120
- 121 Chapter 121
- 122 Chapter 122
- 123 Chapter 123
- 124 Chapter 124
- 125 Chapter 125
- 126 Chapter 126
- 127 Chapter 127
- 128 Chapter 128
- 129 Chapter 129
- 130 Chapter 130
- 131 Chapter 131
- 132 Chapter 132
- 133 Chapter 133
- 134 Chapter 134
- 135 Chapter 135
- 136 Chapter 136
- 137 Chapter 137
- 138 Chapter 138
- 139 Chapter 139
- 140 Chapter 140
- 141 Chapter 141
- 142 Chapter 142
- 143 Chapter 143
- 144 Chapter 144
- 145 Chapter 145
- 146 Chapter 146
- 147 Chapter 147
- 148 Chapter 148
- 149 Chapter 149
- 150 Chapter 150
- 151 Chapter 151
- 152 Chapter 152
- 153 Chapter 153
- 154 Chapter 154
- 155 Chapter 155