Chapter 35
Chapter 35
qoqarin maidowa idanunsa ya hadasu waje daya,babu qarya.....tana da kyau,ita din kyakkyawace ta gasken gaske,to ko kyawun hajiya ta gani?,sai ya sake girgiza kansa,yasan hajiyan,tasan abun qwarai sarai,bai gano me ta hango masa ba,amma ya tabbatar akwai abinda ta hanga din. Saida suraj ya ajjiyeshi a gida sannan shima ya wuce,abbas din ya masa ban gajiya da godiya "Ai babu wannan tsakaninmu,kawai dai next time ka tafi kai kadai,saboda ka samu ku fahimci juna sosai, she's too young,dole sai kana janta a jiki da dabaru sannan zata saki jiki da kai,amma kuma ina me tabbatar maka indai aka samu shaquwa sabo da kusanci tsakaninka da ita,ina me tabbatar maka.....ina sake fadi ina mai tabbatar maka anan zaka fahimci komai basai an gaya maka ba" abinda suraj ya gaya masa kenan,wanda ya tsaya masa a rai,ya kasa fahimta kuma,da wannan maganar ya kwanta. Ita kuwa widad tana fitowa ta qara da dan gudu gudu,wani irin tsoro takeji da faduwar gaba sosai,don sai data tsaya a hanya tadan saisaita numfashinta tana dafe qirjinta da hannu,batasan me yasa batason wancan abokin nasa yana kallonta ba,to amma itafa wallahi mai wanna zubar maganar indai shine wanda uncle muhsin ya turo mata baiyi mata ba sam,saita tabe baki tana buda ledar daya bata,murmushi ya subuce mata da taga masoyiyar wato chocolate,saita zabura tayi cikin gidan tana qwalawa nujood kira. "Iyyeee,yammatan ummu,da alama ciniki ya fada tunda naga kin dade da yawa" hajjaa ta fada cikin salon tsokana tana murmushi,baki ta tura gaba tana ajjiyewa hajjaa ledar,kanta tsaye cike da zallar wautar quruciya tace "Ni gaskiya indai wannan mai surutun ne bana sonsa" dariya nujood ta sheqe da ita,kafin tace komai hajjaan da uncle muhsin ya bata aikin tuntubar widad din idan ta dawo aji ta bakinta tace da ita cikin tattara hankalinta "Saboda me?" "Ya cika siranta,kuma ya fiya magana" wannan karon nujood dariya harda fadowa "Bafa uncle abbas take fada ba,uncle suraj ne wallahi take nufi" sai hajjan itama ta saki dariya,tasan suraj din,duk da ba sosai ba,amma sai da nujood ta fada sannan ta tuna tabbas yana da kirki yana kuma da hira "To alhamdulillah,indai hakane uncle abbas yayi kenan?" Ta fada tana kallon widad,yadda suka tsareta suna jiran amsarta ya bata kunya,saita dauki filo ta cusa fuskarta a ciki tana dariya cike da jin kunya "Allah nidai hajjaa...."kunya ta sanyata tashi da gudu tayi dakinsu,sai suka bita da dariya,hajjaa taja chocolate din ta ajjiye da nufin idan uncle muhsin ya dawo ta nuna masa kafin su taba,ta kuma hada da gaya masa yadda sukayi da widad din. KI KULANI miss xoxo DAUDAR GORA Billynabdul RUMBUN K'AYA hafsat rano IDON NERA Mamuhghee A RUBUCE TAKE huguma _sinkin labaran dake dauke da dukkan wasu nau'ikan salo da kuke so_ _masoya ku biya kudinku ta wannan hanyoyin_ 0022419171 Maryam sani Access bank Saiku tura shaidar biya ga +234 903 318 1070 *Masu katin waya ko VTU zaku tura ta nan* 09166221261 *Al'ummar nijer🇳🇪🇳🇪🇳🇪 zaku tuntubi wannan number* +227 96 09 67 63 *Thanks for choosing us*🔥🔥🔥🔥🔥🔥 *H U G U M A* *_A RUBUCE TAKE_* (K'addarata) *Arewabooks:Huguma* Page 23 Duka dai yanata juya yadda abubuwan zasu kasance har ya gama abinda yakeyi yazo kwanciya,sai ya kauda wanann tunanin ya sake maimaita kiran hafsat amma kamar dai ko yaushe,sai abun ya shiga daure masa kai da kuma bashi tsoro,don haka ya sauya akalar kiran zuwa ga wani constable dake area din nasu,ya aikashi yaje gidansa ya duba masa lafiyarsu,cike da girmamawa ya amsa masa ya kashe wayar ya zauna yana jiran feedback. Bai haura minti biyar ba yayi kiransa "They're fine sir" "Are you sure?" "Yes sir" ya sake tabbatar masa,sai yaji ransa ya baci,ya kashe wayar ya ajjiye yana gyara kwanciyarsa gami da lumshe idanunsa yana furzar da iska daga bakinsa "Dole ya dauki mataki akan hafsat din,abun nata qara gaba yake,wannan zallar raini ne" ya fada a ransa. Washegari daga strolling ya wuce gidan hajiya a qasa,duk da 'yar tazarar dake tsakaninsu sai gashi yaje,saidai ya hada gumi sharkaf kafin ya isa din,hajiya nata masa sannu da fadan bai ganin nisa yayo wannan tafiyar a qafa?, qaramin murmushi ya saki "Hajiya kin manta aikina ne?,tafiya tsaiwa wahala da yunwa duka an koyamana juriyarsu"kai ta jinjina kawai "To Allah ya bamu dacewa" muneera ce ta hado masa breakfast kamar ko yaushe,yau din hajiya bata iya bari ya gama cin abincin ba ta jeho masa tambayar "ya ake ciki?,kaje kuwa?" Kai ya jinjina "Naje hajiya" "Ina fatan komai yayi?" Me zai iya cewa hajiya,bashi da wata amsa data wuce cewa "Alhamdulillahi" ya amsata yana kurbar tea dinsa,sai ta saki murmushi tana jin dadi har cikin ranta,ta sauke ajiyar zuciya "Inaso ayin auren nan a nan kurkusa abbas indai zai yiwu" da qyar ya hadiye bread din dake bakinsa,sannan ya daga idanunsa yana duban hajiyan "Kamar nan da yaushe kike so hajiya?" "Zuwa yaushe zaka shirya dai?" Shuru ya danyi,tunda ta magantu lallai da gaske tanaso ayi a kusa din,koda yaushe babban burinsa shine ya cika umarninta "Kada ka damu,kayi tunani a hankali,ko bayan ka koma ne sai ka fadi zuwa lokacin da kake ganin ka gama shiryawa" "To hajiya" ya fada cikin girmamawa,saidai tuni kwanyarsa tayi nisa wajen tunanin yadda abubuwa suke ta sauyawa suna zuwa masa a bazata. ~~~~~~~~ Sai la'asar ya koma gida,kai tsaye ya shiga bandaki yayi wanka,bayan ya fito ya fito zuwa sassanta don ya samu Black tea,cikin mintuna ya hada ya dawo falon da zummar zama,amma sai ya dinga jin kamar hayaniya hayaniya daga qofar gidan,sai ya miqe ya yaye laluben window din da ya bulla har harabar gidan,harabar gidan fes babu kowa hakanan babu komai,amma qoramar qofar gate din gidan a bude take,ya kuma tabbatar hayaniyar a qofar gidan sosai take tashi,don haka ya ajjiye cup din ya zura slipper dinsa da ya cire ya doshi qofar fita. Tun kafin ya qarasa ya dinga ji kamar muryar hafsa,amma sai ya qaryata kunnuwansa,tunda yasan bata nan,saidai yana dosar waje kunnuwansa na sake ji masa muryar tata. A hankali ya buda qofar ya fita,take idanuwansa suka gasgata masa abinda kunnuwansa suka ji,zallar mamaki ya kusa kasheshi a wajen "Hafsa a bauchi?" Ya yiwa kansa tambayar da bai san amsarta ba,yana sake zubawa hafsa din idanu,wadda bata ma fahimci ya fito ba,ta taqarqare sunata sa'insa ita da wani,nawwara na hannunta,mimi na tsaye gefanta tana riqe da hannunta,maqotansa biyu keta bada baki,yayin da wasu matasa dake sana'ar business center a wani dan container irin na mtn gaban gidan kadan suma suka iso wajen. Yana fitowa daya daga cikin maqotan nasa ya ganshi,da sauri yace "Yauwa alhmdlh,ga mai gidanta nan ma ya fito,mun dauka ai baka nan shi yasa tun dazu bamu yimaka magana ba" dukka idanu suka waiwayo suka zuba masa,take yaji ya muzanta,ya aro jarumta da juriya ya qaraso wajen yana riqe da hannun mimi,wadda tunda ta ganshi ta sheqo da gudu ta maqale ubanta. Qarawa yayi ya miqa hafsa din ita yana cewa "Wuce gida" saboda ganinta cikin mazan ba qaramin quntata masa rai yayi ba,ga kuma baqincikin tahowar da tayi babu izini ko shawara dashi. "Alhaji kayi haquri,amma babu inda zata saita cikamin kudina,zata gane ni din matsiyaci ne na ainihi" fuska a daure abbas ya juya yana dubansa "Kaga,barta ta
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119
- 120 Chapter 120
- 121 Chapter 121
- 122 Chapter 122
- 123 Chapter 123
- 124 Chapter 124
- 125 Chapter 125
- 126 Chapter 126
- 127 Chapter 127
- 128 Chapter 128
- 129 Chapter 129
- 130 Chapter 130
- 131 Chapter 131
- 132 Chapter 132
- 133 Chapter 133
- 134 Chapter 134
- 135 Chapter 135
- 136 Chapter 136
- 137 Chapter 137
- 138 Chapter 138
- 139 Chapter 139
- 140 Chapter 140
- 141 Chapter 141
- 142 Chapter 142
- 143 Chapter 143
- 144 Chapter 144
- 145 Chapter 145
- 146 Chapter 146
- 147 Chapter 147
- 148 Chapter 148
- 149 Chapter 149
- 150 Chapter 150
- 151 Chapter 151
- 152 Chapter 152
- 153 Chapter 153
- 154 Chapter 154
- 155 Chapter 155