Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 12

Chapter 12

A Rubuce Take Book 1 Complete Hausa Novel – Widad and the Secret of House 1,313 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

wani cartoon,dama kuma Allah Allah take ta koma ta qarasa kalla. Da kallon mamaki ummu ta bita sanda ta shiga ganin nan da nan ta dawo "Har kinkai?" "eh na kai", ta amsa kai tsaye tana komawa cikin kujera ta lafe hankalinta duka yana kan cartoon din,jim ummu tayi kamar tana tantama,sai kuma ta dauke kanta taci gaba da sabgarta. Bayan minti goma sai naadir ya shigo ya cewa ummu "Yaaya ma'aruf yace ba'a gama abincin bane?" "Wanne abinci kuma bayan wanda aka kai masa,ko qaro musu za'ayi?" "Anya?,yace dai yunwa yakeji abincin yake jira" waiwayawa ummu tayi ga widad data lafe sosai gabanta na faduwa,amma sai tayi kamar bata a wajen,ta rufe idanunta kamar mai bacci,kallo daya ummu tayi mata tasan ba bacci takeyi ba,sam qarya bata mata kyau,tun dazun ta fahimci akwai lauje cikin nadi a maganarta "Widad a ina kika aje masa abincin?" Manyan fararen idanunta ta bude kamar zata saki kuka ta bawa ummu amsa "Yana kan motarsa" baki ummu ta kama tana kallonta "Kai jama'a" maama batulu ta fada cikin bacin rai,yayin data tsaya tana jiran jin irin fadan da ummu zatayi mata,idan ya kama da duka ma ta doke ta,yarinyar ta tsayewa rayuwarta gaba daya,gata qauna da kulawar da ummun ke bata nata yaran basu samu wannan ba,duk da suna samu dai dai gwargwado daga wajenta,amma ita butulu ba irinta takeso ba "Yanzu tsabaragen iskanci a aikeki widad kije ki dorawa mutum.abinci saman mota?,ta yaya to zaisan kin kai?,idan wani ya kifar kuma bai sani ba fa?" Ta qarashe maganar tana maida kallonta ga ummu wai ko ummun zata kama mata,amma sai taji tace "Ubangiji ya shiryeki,wannan quruciyar da shirme da kike fama dasu Allah ya maganta miki" ta juya ga naadir "Jeka dauka daga kan motarsa ka miqa masa" amsawa yaron yayi ya juya yana ficewa,ita kuwa batulu dole ta kama bakinta jin ummun bata kama mata ba,taso taci gaba da maganar tana sake zuga abin,sai abun ya tsaye mata arai,sosai.haushi ya cikata,yarinya sai nema mata mazan aure ake tana iya shege?,wa tafi goshi?,idan kyau ne yaransu gaba daya babu wanda bashi da dai dai nashi,rashin uwa kuma a kusa ai ba farau kanta ba,dukka yaran dake can gida tare dasu kowanne ba uwar gareshi ba,amma babu wanda ummun ke shagwaba haka kamar widad din,kai hasalima ba wanda ummu ta kama ta riqe sai widad din?. Da wannan takaicin ta baro gidan,saidai kuma ta qudire a ranta ba zataji takaicin banza ba,don haka da daddare bayan dawowar alhj mahmud ta zauna tayi masa famfo sosai,ta bashi labarin qarya da gaskiya kan abinda ya farun. Sosai kuwa ya tunxura,ransa ya baci,abun na yarinyar ya fara kaishi bango,zuciyarsa dama yaketa danna,abinda ya faranta ran batulu kenan ta gyara zama "Diya mace dai 'yar gidan wani ce,gwara a gyara mata zama tun yanzu,sannan idan tace shima ma'aruf bata sonshi kuma bansan wa takeso ba,gashi sai dad'a girma suke,kuma ita din ba wata budurwa ba bare ace akwai irin mijin da take hari,duka duka ma yaushe tasan rayuwa ma?". Shuru kawai yayi yana jinjina kai, tabbas zai dauki mataki,bazai bari yana ji yana gani ba gata ya lalata ba,duka sauran yaran da ake riqo a nan gidan ai ba haka suke ba,idan ma ummu ke daure mata gindi lallai gobe sai ya nuna mata kuskurenta. Har widad din ta kwanta ummu ta tasheta "Widad,karki sake aikata abinda kika aikata dazu kinji?,baki gani ma'aruf yayanki ne?,kuma shine zai zama mijinki a nan gaba?" Baki ta sake tana kallon ummu a sakarce,hawaye na shirin fara taruwar mata a idanu "Miji?,ni wallahi bana sonshi ummu" sai kuka ya kufce mata sosai,ta kuma birkicewa ummun gaba daya "Samu guri ki kwanta" kawai ummun tace da ita bayan ta gaji da koke kokenta,tana jinta daga kwancen tana jan sheshsheqar kuka har bacci yayi awon gaba da ita,wannan al'amari na widad......to wa take so?,Allah shine mafi sanin gaibu shine amsar da ummu ta bawa kanta daga qarshe,ta rufe idanunta tana fata ko meye zaizo yazo da sauqi. *W A S H E G A R I* Tunda ta tashi da fushin zancan ma'aruf ta tashi,ummu tayi tayi ta kulata taqi,ko larifa mutuniyarta yau babu 'yar hirar da suke tsakaninsu,da take zata kwaso undies dinta da uniform ma zata wanke mata nuna mata inda ta zubasu kawai tayi,amma abinka da zuciyar yaro qarfe goma na safe sai ta fito falo ta zauna,ummu na zaune kan one sitter,sai ta koma kan two sitter ta kwanta tana kallo a MBC3,duban sashenta ummu tayi taci gaba yankan farcenta ba tare da tace komai ba,daga nan suna jiyo hayaniyar yaran gidan a farfajiyar gidan,wanda ta tabbatar da ranta fes yake da tuni ta fice,idan ba harabar gidan ba to wajen anty madina. Sallamar abban nata ya sanyata miqewa ta zauna suna kusan hada baki ta da ummu wajen amsa masa,haka kawai taji gabanta ya fadi,kallo daya tayi masa ta shiga nutsuwarta. Bai jira sun gama amsa sallamar tasa ba ya qarasa wajen kayan kallon dake falon ya zaro wayar USB dake jin wuta ya nufo widad da ita,baikai ga isa ba kiran sunansa da ummu tayi da qarfi ya dakatar dashi,don tuni ta fahimci abinda yakeson aikatawa,saboda ya taba aikata hakan a baya "Kayi hauka ne mahmudu?,da raina da lafiyata?,ina zaune a falon zaka shigo ka dauki mabugi ka dakarmin ita?,to daketa nace?,wallahi wallahi kana dukanta saina rama mata,idan kuma kana shakka to bismillah" ummu ta fada ranta a mugun bace,abinda yasa ya yarda wayar hannun nasa kenan,yana qoqarin saita kansa,tare da qoqarin gano rashin dacewar abinda ya aikata din,wannan ya bawa widad damar miqewa da gudu ta isa ga ummun,ta fada jikinta gami da qanqameta tana sakin kuka,abinda ya taba zuciyar ummun,ya kuma saukar mata da tausayin widad din,saita dora hannunta saman kanta tana lallashinta. Gaban ummun ya qaraso ya russuna yana gaisheta,harara ta jefa masa "Bana buqatar gaisuwarka" saita zare widad daga jikinta tana umartarta data wuce daki,ta miqe tana sharbar hawaye,sannan cikin kaffa kaffa da mahaifin nata ta gewayeshi ta wuce. "Kiyi haquri,ni banyi haka don na bata miki rai ba,abinda yarinyar nan takeyi yayi yawa,kowa sai tace bata so?,har a aiketa taje ta dora abinci akan mota?,sa'anta ne shi?,fisabilillahi haka za'a zuba mata idanu?" Duk da taji sallamar halimatu a falon amma hakan bai dakatar da ita daga bashi amsa ba,ta gano daga inda tushen zancan ya fita "To cewa akayi lallai lallai sai ta sosu?,ko kuma fadar Allah ce?,uwayensu ba sai da kukaji kuna sonsu ba kuka auresu?,to ahir wallahi,a sakar mata mara hakanan,ita kadai kunbi kun sata a gaba?,da kai da masu zigoka din ka gaya musu,wallahi tallahi su fita a idona akan lamarin widad,ba wanda ya haifeta ko yayi wahalarta,saboda haka su kama kansu" qas yayi da kai "Allah ya bada haquri,ya huci zuciyarki" "Ameeen" ta amsa a fusace,sai ya miqe,yana son tambaya yaji alhaji yana kusa amma fushinta ya sanya don dole ya juya ya fice, halimatu ta bishi da kallo sannan ta dawo da dubanta ga ummun bayan ta tabe baki "Allah ya kyauta amma dai ummu ai da kin bari ya hukuntata,icce tun yana danye fa ake tanqwarashi"ta fada tana duban ummu da kyau "Ya kyauta abinda yafi haka,iccen qaniyarki,duk cikinku wa aka yiwa hakan iyee?" Ganin fadan

Table of Contents

Chapters

155 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138
  139. 139 Chapter 139
  140. 140 Chapter 140
  141. 141 Chapter 141
  142. 142 Chapter 142
  143. 143 Chapter 143
  144. 144 Chapter 144
  145. 145 Chapter 145
  146. 146 Chapter 146
  147. 147 Chapter 147
  148. 148 Chapter 148
  149. 149 Chapter 149
  150. 150 Chapter 150
  151. 151 Chapter 151
  152. 152 Chapter 152
  153. 153 Chapter 153
  154. 154 Chapter 154
  155. 155 Chapter 155
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});