Chapter 46
Chapter 46
backyard din gidan,basa so kowa ya tsaidasu bare kwalliyar tata ta baci,suna tafe anty madina na jaddada mata kada ta sake tayi kuka,zata bata fuskarta "Ke maison kwalliya,kinga yadda kikayi kyau kuwa widad,baki taba kyau irin na yau ba" takanji dadi idan akace kwalliya tayi mata kyau,musamman daya zamana ita din mai son kwalliyarce,to amma kuma bata samunta sai lokaci lokaci,yau din da anty madina ke cewa tayi kyau sai bata ji wannan dadin da takanji ba,ta daiyi qoqarin dakewa,tanason farantawa anty madina rai,saboda kirkinta da yadda take sonta. Sallamarsu cikin falon ya ja hankalin jama'ar dake falon,badawiyya abokiyar wasa ga widad din,wadda shigowarta kenan falon ta saki guda data ratsa falon gaba daya. "Ma sha Allah.....ma sha Allah,widad Allah yasa anyi a sa'a,Allah yasa mutu ka raba" bakunan masoyanta dake wajen ya cika da addu'a,yayin da kishi hassada da kuma qyashi ya cika zukatan wadanda ke qin jininta hakanan. Gaban ummu suka so kaita,amma saita musu nuni dasu ajjiyeta gaban abbas din ba tare da tayi magana ba,sun fahimta,saboda haka suka nufi gaban abbas din da ita,ganin haka yasa tun kafin su qaraso suraj da muhammad da suka masa rakiyar suka janye baya,suka basu fili sosai. A hankali suka tsugunnar da ita a gaban nasa,rabin fuskarta yana rufe,saidai hakan bai hana kayan adon dake jikinta bayyana ba,suka ja da baya,sai falon ya dauki hayaniyar abokan wasa da suketa yiwa juna tsiya tsakaninsu da uncle muhsin,abinda ya dan janye idanun mutane kenan daga kan abbas da widad din. Tana zama awajen wani irin qamshi ya soma fita daga jikinta,sassanyan qamshi mai fusgar hankali da kwantar da zuciya,irin qamshin dake saurin sakawa zuciya karaya da wani irin sassanyan yanayi,ya daga idanunsa a hankali,fararen hannayenta da suka jan lalle irin na asalin yamalawa su ya fara gani,a hankali yaci gaba da kallonsu kafin ya daga kai zuwa ga fuskarta,dai dai sanda itama ta daga kanta zuwa gareshi don ta gaidashi kamar yadda anty madina ta gaya mata,fuskarta ta fito tarwai da wani irin haske data qara "Ina yini" ta furta,bugun zuciyarta na bayyana har saman harshenta,ya kuma biyo ta sautin gaisuwarta ya sanya lafazinta fita a rarrabe,amma hakan sai ya qarawa sautinta mai cike da quruciya kyau,sai ya dan lumshe idanunsa kadan yana amsawa "Lafiya qalau" yana ganin fuskarta a yau ta sake zama ta manya fiye da ranar da ya ganta a gidan muhsin,a yau din ta dan sake zama babba kadan ba kamar ranar ba "Sir.....me hoton ya gama dauka,saura na tsaye da wanda za'ayi muku da hajiya ummu saboda tarihi ko?" Sam baima san zaman da tayi wai hoto akeyi ba,muhsin ya cuceshi,yanzun idan baiyi wasa ba kafin la'asar hoton ya riga rana fadawa cikin kafofin internet,ko a haka baisan yadda akayi labarin bikinsa ya karade duniya ba,ko ina ka duba tsakanin whatsapp twitter facebook da instagram zancan da akeyi kenan "Dagota mana please,yanzu yanzu aka gama baka amanarta fa suna kallonka" suraj ya rada masa,no more option sai bata hannunsa da yayi "Taso" ya fada yana kallonta,labbansa daya furta taso din take kalla,tsoro da mamaki fal idanunta,dama shima dan iska ne?,abinda take fada kenan a ranta,a gabansu ummun yake bata hannunsa?,bashi da kunya ashe shima?. Bata gama wannan tunanin ba taji ya kama lallausan tafin hannunta,ba shiri ta miqe ta kuma zame hannunta da sauri hawaye suka fara taruwa a idanunta,lallai saita gayawa ummu abinda yayi mata,so yake ta mutu?,bayan ummu ta hanata tsaiwa kusa da kowa ma?. _to masu karatu,gafa amarya widad mai cike da tarin wauta quruciya gata kuma goyon kaka,ba'a fara wasan bama,muje zuwa dai_😂😅👏🏽 KI KULANI miss xoxo DAUDAR GORA Billynabdul RUMBUN K'AYA hafsat rano IDON NERA Mamuhghee A RUBUCE TAKE huguma _sinkin labaran dake dauke da dukkan wasu nau'ikan salo da kuke so_ _masoya ku biya kudinku ta wannan hanyoyin_ 0022419171 Maryam sani Access bank Saiku tura shaidar biya ga +234 903 318 1070 *Masu katin waya ko VTU zaku tura ta nan* 09166221261 *Al'ummar nijer🇳🇪🇳🇪🇳🇪 zaku tuntubi wannan number* +227 96 09 67 63 *Thanks for choosing us*🔥🔥🔥🔥🔥🔥 *H U G U M A* *_A RUBUCE TAKE_* (K'addarata) *Arewabooks: Huguma* Page 30 Anty deena ta ankara da yadda taketa narai narai da idanu,kadan take jira ta fara sakin ruwan hawayen nata,murya qasa qasa ta yadda ba wanda zaijisu tace "Haba mana widad,so kike ummu ta gani hankalinta ya tashi?" Kai ta girgiza tana kallon idanun anty deena da golden eyes dinta "Okay,maza hadiye,hadiye kinji qanwata" kai ta sake gyadawa,sannan aka fara daukan hoto. Gaba daya ji yayi ya qosa ayi a gama,murya can qasa yace da muhsin "Please muhsin,am tired wallahi" murmushi yayi,sau tari yana bashi dariya,bai taba ganin dan police wanda bai jure hayaniya ba irinsa "Okay" ya fada yana dagawa widad hannu,a hankali ta qaraso wajen tana kauda idanunta daga kallon abbas,haka kawai idan ta kalleshi sai taji gabanta ya fadi "Maza kusa ayi muku ku biyu" wani irin tsoro ya kamata,gabanta ya tsananta faduwa,sai ta narke cike da tsoro tana kallon uncle muhsin,wanda shi sam baima san me takeyi ba "Matsa widad lokaci na qure musu" anty deena ta fada,kamar kazar da qwai ya fashewa a ciki ta fara takawa zuwa kusa dashi,nesa kadan dashi ta tsaya,saida mai hoton yayita magana da taimakawar gargadin da anty deena ke mata da idanu ta sake matsawa aka dauka "Enough please" ya sake fada "Dama ai an gama" suraj ya amsa wannan karon yana dariya,sallama sukayi dasu ummu,akwai yiwuwar su kwana a kano,duk da babu tabbas, uncle muhsin keson hakan,saboda akwai walima daya shirya musu. Tun daga wannan lokacin gaba daya ta sake zama sukuku,ita gaba daya komai ya kwance mata,hakanan banbarakwai take kallon komai,daga qarshe dai a daki ta qule ta qarasa yininta,duk kuwa da sabgar da ake cikin gidan. Da daddare kuwa bata yarda ta kwana da kowa ba sai a bayan ummu,kowa tsiyar ai dole su rabu yake mata,wannan ya sanya zuciyarta karyewa ta kuma soma kuka sosai,da qyar ummu ta rarrasheta. ********Washegari tun da safe anty madina ta aiko kiranta,tana sanye da dogon hijab da ummu ta fidda mata,ganin cewa a yanzun wani nauyi ya hau kanta,kuma gidan akwai 'ya'yan baffaninta maza,ga kuma baqi maza still 'yan biki da basu kai ga tafiya ba. A kitchen ta taddata tana ta hidimar hada abincin safe,sai ta waiwayo tana kallonta "A'ah,ya haka?,bakiyi wanka ba dama?" Baki ta turo gaba a shagwabe tace "Anty madina duka duka yaushe garin ya waye?,kuma Allah an fara sanyi fa" rai anty madina ta bata sosai "A'ah,daga yau sai yau,kada na sake gani,idan akace mace tana da aure da wuri take wanka ta gyara jikinta kinji ko?,ta fidda kayanta tayi kwalliya sosai" kai ta gyada a sanyaye,ita dai komai sai ace aure aure,duk an takurata da kalmar nan. "Shiga dakina a hankali kada ki tada min abba,akwai turarenki da kika bari jiya saman mirror,ki dauka ki feshe jikinki sosai,sai kizo zan aikeki" amsawa tayi da to,don ita badai qauna da turare ba,ta wuce dakin anty madinan. Ba jimawa sai gata ta dawo,tana ta zanga qamshi kuwa,ta nuna mata wani baske tace "Dauki maza kikai sitting room din kawunnanki" ba tare data kawo komai a ranta ba ta amsa da to,ta dauki kwandon tayi ficewarta,tana tafe tana tsayawa magana da mutanen dake mata magana a hanya,cikin
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119
- 120 Chapter 120
- 121 Chapter 121
- 122 Chapter 122
- 123 Chapter 123
- 124 Chapter 124
- 125 Chapter 125
- 126 Chapter 126
- 127 Chapter 127
- 128 Chapter 128
- 129 Chapter 129
- 130 Chapter 130
- 131 Chapter 131
- 132 Chapter 132
- 133 Chapter 133
- 134 Chapter 134
- 135 Chapter 135
- 136 Chapter 136
- 137 Chapter 137
- 138 Chapter 138
- 139 Chapter 139
- 140 Chapter 140
- 141 Chapter 141
- 142 Chapter 142
- 143 Chapter 143
- 144 Chapter 144
- 145 Chapter 145
- 146 Chapter 146
- 147 Chapter 147
- 148 Chapter 148
- 149 Chapter 149
- 150 Chapter 150
- 151 Chapter 151
- 152 Chapter 152
- 153 Chapter 153
- 154 Chapter 154
- 155 Chapter 155