Chapter 99
Chapter 99
toilet tayi wanka, d'aure da towel ta fito d'an k'arami, had'a ido tayi da Sabeer wanda yake zaune kusa da gadon Na'eem da Shaheed yana lilasu a hankali murmishi suka sakarwa junan su cike da so, wani mayataccen kallo Sabeer yake bin ta dashi wanda tun safe ta kula da irin wannan kallon nashi, ita tsoron ma zuwa kusa dashi take hannun shi ya mik'a mata bata yi musu ba ta mik'a nata ya rik'e shi tare da janyo ta jikin shi ya fara shinshina wuyan ta zuwa bayan ta hura mata iskar bakin shi yayi cikin kunnen ta wanda ya haddasawa Suhaima kasala cikin muryar rad'a yace "Baby nah ki bani wannan damar please ina son kasance wa dake nayi missing d'in ki da lot " Duk da ta gane nufin shi amman da taji abin da yace sai da taji fad'uwar gaba amman ya zata yi tunda hakk'in shi ne wanda ya rataya kan wuyanta, don haka k'ara shigewa jikin shi tayi kawai tana cusa face nata a chest d'in shi. "Bari naje nayi wanka koh? " Ya k'arasa maganar yana d'aga mata gira, tashi yayi ya wuce toilet yayi wanka sannan ya fito ya tarar da ita har ta shirya cikin wata gown ta bacci iyakar rabin cinyarta (da yake Sabeer ya sanya Jiddah d'ebo mata kayan ta ba tare da wani ya gane ba) ta gyara gashin ta sai tashin kamshi take, kallonta yake kamar yau ya fara ganin ta. Agurguje ya shirya ya taho wajen ta ya rungume ta cikin jikin shi yana faman aika mata da zafafan sak'onnin shi cikin wani irin salo mai wuyar fassara, wannan daren sun raya shi sosai cikin wani irin kaunar junan su anan Sabeer ya gama tabbatar wa Suhaima itace rayuwar shi haka ita ma a 6angaren ta gwarzon nata shine jin dad'in rayuwar ta suna addu'a da fatan Allah ya barsu har karshen rayuwar su. Rayuwar su suke cike da jin dad'i da kwanciyar hankali suna kula da yaran su sosai da haka har Na'eem da Shaheed suka tasamma shekara d'aya yaran sunyi wani irin girma gashi suna wata goma suka iya tafiya gudun su suke ko'ina zuwa lokacin Aunty Aliyah tana d'auke da tsohon ciki itama, zumunci Jiddah da Suhaima kuwa kullum k'aruwa yake idan bata zo ba to za suyi waya junan su, tsakanin Suhaima da Sabeer kuwa kullum soyayyar su k'ara k'arfi take kula suke bawa junan su sosai, Daddy kuwa a weekend yake zuwa ganin jikokin shi. Suna watanni goma sha bakwai Suhaima ta yaye su, yayin da Aunty Aliyah kuma ta haihu aka samu mace sunan Umman su Suhaima aka sanya mata wato Fatima suna kiran ta da Ameerah, Yah Aliyu ma karatun shi ya d'auki zafi yana daf da had'a degree d'in shi a Buk. Wani zuwa weekend da Daddy yayi yace yana son Na'eem da Shaheed su bishi suyi mishi kwana 2 sunyi matuk'ar shak'uwa da Daddy sosai, a tsorace Sabeer ya barwa Daddy yaran shi don yana jin tsoron kada Mumy ta kashe musu yara, tsaf Daddy ya karance shi girgiza kai kawai yayi yana murmishi bai ga laifin shi ba yana da gaskiyar shi baisan yanzu yanda Mumy ta koma ba ne duk wannan ji da kan babu shi. ********** Duk wani jin dad'i gashi nan akwai shi sai dai babu kwanciyar hankali, duk tayi bak'i ta rame Dr Faridah kenan wato Mumy abin duniya yayi mata yawa wajen shekara 2 bata sanya tilon d'anta a idon ba tayi neman tayi binciken duk a banza tayi kok'arin tambayar Daddy akan inda d'anta yake but yace shima neman shi yake k'arshe ma rufe ta da fad'a yayi ai duk laifin ta ne gashi ta salwantar mishi da rayuwar d'an shi ba'a san inda yake ba. Ta 6angaren Dr Ahmad d'an fillo dasu Hajjah Hauwaa suma suna cikin wannan tsantsar tashin hankalin na rasa sanin inda Sabeer sunyi binciken iyakar iyawar su amman basu ji d'uriyar inda yake amman Dr Ahmad d'an fillo yaso d'ago Daddy yasan inda Sabeer yake ganin yanda hankalin shi yake kwance bai d'aga hankalin shi sosai ba akan 6atan Sabeer amman sai Daddy ya nuna mishi ba haka, tun daga lokacin Dr Ahmad d'an fillo ya kwanta rashin lafiya saboda 6atan Sabeer d'an lelen shi yayi kuka sosai yana mai nadamar da tun lokacin yayi magana matar shi ta dawo gare shi tun da dalilin ta suka neme shi suka rasa, Haka ma Mumy ta kwanta ciwo a tsaitsaye ko hospital bata iya zuwa jinin ta hau sosai damuwa biyu ce ta had'e mata rashin tilon d'anta da kuma juya mata baya da mijinta yayi duk a dalilin Suhaima, wadda zuwa wannan lokacin tayi nadamar abin da ta aikata yafi sau ba adadi tayi kukan sosai da bata aikata hakan ba da tuni d'anta na kusa da ita har da jikokin ta ma, har tana fatan ta d'an samu sauk'i ta nemi garin su Suhaima taje ta nemi yafiyar ta ko zata samu sassauci cikin zuciyar ta da rayuwarta gaba d'aya. Tun safe yau jikin ta ya rikice ga Daddy baya nan yafita tana kwance a falo wajen 4 na yamma ne jefi jefi tana kallon tv tana kallon African Tv suna wa'azi na marigayi sheik Ja'afar Mahmoud Adam (Allah ya jik'an shi da rahma Amin), lokaci zuwa lokaci gaban ta na fad'uwa. Sallama Daddy yayi ya shigo palourn hannun shi rik'e da Na'eem da Shaheed suna d'an tsalle tsallen su, wata zabura Mumy tayi ganin wasu kyawawan yara masu matuk'ar kama da junan su kuma abin da ya k'ara hargitsa ta ganin yanda suke matuk'ar kama da Daddy da kuma Sabeer, nan take wani tunani ya d'arsu cikin zuciyar ta ko Daddy aure ya sake bata sani ba matar ta haifa mishi yara. Da d'an gudun su suka k'arasa inda take tare da rungume mata k'afafun ta, sakin baki kawa tayi tana kallon su wani irin sanyi taji jikinta yayi ta zame ta zauna lokaci d'aya wani mugun son yaran ya ratsa mata cikin zuciyar ta da zuciya d'aya ta d'ago su zuwa jikin ta cikin murmishi take cewa "Ya sunan ku yara nah?" Na'eem da yafi surutu cikin muryar shi wadda bata kware ba yace "Ni sunan Na'eym wannan kuma Sha'eed" Ya k'arasa fad'i yana Shaheed da d'an yatsan shi, "Masha Allah sunan masu dad'i Allah ya albarkaci rayuwar ku " "Amin " Daddy ya amsa cikin zuciyar shi, d'agowa tayi ta kalli Daddy tare da cewa "Daddy yaushe ka sami yara masu kama da kai bansani ba? " Murmishi yayi yana tafiya Stairs yana cewa "Bana wa bane aron su aka bani na kwana 2 " Cikin d'okin murya tace "Da gaske kake Daddy?" "Ban ta6a yi miki wannan wasan ba gaskiyar kenan " Washe baki tayi duk yanda jikinta babu dad'i amma sai taji lokaci d'aya kamar an cire mata ciwon cikin farinciki take cewa "Nagode Thank U very much Daddy naji dad'in ganin yaran ji nake kamar my Son nake gani Allah ya biyaka " Ta k'arasa maganar hawaye na fita daga eyes nata sosai Daddy yaji wani mugun tausayin ta lokaci yayi da Dr Faridah ya kamata tasan ainahin inda d'anta yake yana gama wannan tunanin ya wuce stairs
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104