Chapter 25
Chapter 25
d'ora hannun ta tayi dukka biyun a saman kanta tace "Wayyo Allahna na shiga uku ni Suhaima yau nice a waje har k'arfe goma sha d'aya da rabi innalillahi " Lokaci d'aya hawaye suka fara zubo mata ga wani mugun tsoro da sanyi da take ji, tafiya ta fara yi ta nufi k'ofar hall d'in taga duk yawan mutanen nan wayam sai wasu d'ai d'aiku wanda batasan fuskar su ba, tuni Suhaima ta samu waje d'aya ta raku6e ta fara rasgar kuka kamar wadda akai mata dukan tsiya. Kuka sosai take har da majina ta rasa mafita don duk a rud'e take ta kasa dai daita nutsuwar ta balle ta sami mafita gashi phone d'in Jiddah a hannun ta wa zata kirawo acikin familyn ta mutanen da basu yi maraba da zuwan ta cikin su ba matsayin bak'unta na kwanaki biyu, balle ta samu damar kiran wani daga ciki ya taimaka mata, gashi idan ma ta kirawo Yaya Aliyu d'aga musu hankali kafin ma yazo ma koma mai ne ya cinye ta kuma bata yi wa Jiddah adalci ba idan ta fad'a mishi yanzu ya zata yi wayyo Allah na, sake rushe wa da kuka Suhaima tayi sosai tana nan a raku6e taji an dafa mata kafad'a tare da cewa "Hey what are you doing here? " Wata irin firgita Suhaima tayi tare da jiyowa a tsorace had'a ido tayi da wannan guy d'in na d'azu yana tsaye daf da ita ya hard'e hannun shi a kirji, wani k'ugi cikin ta yayi wanda tana tunanin ma Sabeer yaji k'arar da cikin nata yayi matse k'afafun ta ta fara yi saboda daf take da sakin fitsari a tsaye jikin ta kuwa sai rawa yake wanda ya sanya wayar Jiddah ta fad'i a k'asa da bag d'in ta. Kallon ta Sabeer yake up and down yana sakin wani murmishi wani sanyin dad'i ne yake ratsa cikin zuciyar shi da gangar jikin shi, sauran kad'an dariya ta kubce mishi ganin yanda take matse k'afa tamkar wanda yake jin fitsari ya matse shi irin sosai d'in nan har k'arar da jikin ta yayi sai da yaji sautin. Ganin murmishin da yake ba k'aramin sake rud'ar da Suhaima yayi ba aikuwa fakar idon shi tayi ta tattara gown d'in ta da hannun ta kafin Sabeer ya ankara yaga Suhaima ta zura da gudu tayi hanyar fita daga gate, ba shiri shima ya d'auki phone d'in da bag nata da suka fad'i ya bita da gudu shima. Suhaima da ta bud'e kofar gate d'in zata fita da sauri ta dawo baya jin wani irin sanyi da ya busa ta gashi wajen duhu babu wadaccen haske sosai a wurin nan ta tsaya waje d'aya tana rawar jiki, da haka Sabeer ya cimmata tana tsaye sai ruwan hawaye da yake tsere saman kyakkyawar face d'in ta, ganin Sabeer a kusa da ita da sauri Suhaima ta bud'e baki tace "Don girman Allah kayi hak'uri da abin da nayi maka tsautsayi ni bazan sake ba har abada kayi hak'uri kada kayi min komai bansan kowa anan ba " Sosai ta bashi tausayi ganin irin rud'ewar da tayi cikin sanyin murya yace "Hey calm down babe babu abin da zan miki just I'll help you" Kamo hannun ta yayi ganin har yanzu bata daina rawar jiki ba kuma a rud'e take, jan hannun ta yake har cikin mota ya zaunar da ita tukunna ya zagayo seat d'in driver ya zauna kallon ta ya tsayayi na tsayin wasu minutes, kallon yake cikin wani irin yanayi ita kuwa kanta a sunkuye batasan abin da yake ba tsoro ne fal a tattare da ita addu'a take cikin zuciyar ta Allah yasa kada ya cutar da ni, kafin yayi wa motar key suka bar wajen sun d'an yi nisa suna tafiya tukunna ya jiyo ya kalle ta still har yanzu kanta a sunkuye. D'an girgiza kai yayi tare da sakin dan murmishi yace "Ina zamu je, i mean ina ne gidan da zan kai ki? " D'an satar kallon shi tayi ta fad'a duniyar tunani ita da take bak'uwa a garin yau ne zuwan ta na farko ina zata gane gidan, don haka sai tayi shiru kawai. Ganin haka yasa Sabeer yace "Ina jiran ki fah kinsan dare yayi fah idan baki da wajen zuwa kuma sai mu wuce guest house d'ina mu d'an huta zuwa gobe " Wani zaro ido Suhaima tayi tamkar idanun ta zasu firfirto wani tsoro da nadamar shiga motar shi ya dirar mata lokaci d'aya ashe d'an iska ma ta shiga motar shi yau na shiga tara ba uku ba, dariya sauran kad'an ta kubce wa Sabeer ganin yanda Suhaima ta koma. "Don Allah kasan gidan su amaryar Jiddah? " Suhaima ta fad'a cikin rawar murya, da mamaki ya kalle ta kafin yace "Oh nan zaki je kenan? " Da sauri Suhaima ta d'aga kanta alamar eh, mamaki ne sosai ya kama shi ta yanda akayi Suhaima tazo gidan tun da yasan halin 'yan gidan su da basa huld'a da talaka sai mai kud'i d'an uwan su. Kuyi hak'uri da wannan fan's mu had'u a next page muji ya zata kasance. Ga Sabeer da Suhaima sun had'u shin komai zai faru kuma?... Aishat A Muh'd ✍🏻 [2/4, 11:28 AM] Aıʂɧąɬ A Mųɧ'ɖ ✍🏻: A SANADIN SON KI Written by Aishat A Muh'd ♻ EXCLUSIVE WRITER'S FORUM Dedicated to my Sadeey saNaz PAGE 38-39 Babu wanda ya sake magana a cikin su kowannen su da tunanin da yake cikin zuciyar shi, amman Suhaima har yanzu hankalin tashe yake ganin har yanzu basu zo gidan ba ta sadaukar sace ta ma yayi tuni wasu sababbin waye sun cigaba da zuba saman fuskar ta, d'an kallon ta Sabeer yayi kad'an yana girgiza kai cike da mamakin ta ko wahalar kuka bata yi. Da haka suka k'arasa gidan Suhaima tana ganin an shiga cikin gidan ta tabbatar shine sai da ta saki ajiyar zuciya na kwanciyar hankali kafin ta sanya hannun ta saman face nata da niyyar goge hawaye sai taga an mik'a mata tissue kar6a tayi ta goge tukunna ta fara kok'arin bud'e kofar motar, kamar ance ta jiyo ta kalli side d'in su Jiddah aikuwa ta hango Jiddah tana tafiya cikin sauri tana goge fuska, da sauri Suhaima ta k'arasa fita kamar abin arzik'i ta rufe kofar motar sai ta zuro kanta ta jikin window da yake ya sauke glass d'in. Sabeer har zai yi wuce zuwa parking lot sai yaga ta zuro kanta sai ya tsaya ya d'auka godiya zata yi mishi sai hasashen shi yasha banban da na Suhaima don cikin tsiwa ta fara cewa "Uhm Malam ka d'auka godiya zan maka da ka zuba ido kana kallona har da bud'e kunnuwa don jin abin da zance, to ban gode ba kuma hak'urin da na baka d'azu in mistake ne, me yasa ma ka tausaya min ka d'auko ni da ka barni acan ma da nafi jin dad'i... " Da sauri Suhaima ta fitar da kanta tare da zurawa da gudu zuwa inda ta hango Jiddah a tsaye sai safa da marwa take, sakamakon wata cafka da Sabeer ya kawo mata ganin ta gudu ne yasa shi dunk'ule hannun shi ya naushi d'aya hannun kafin ya jingina kanshi jikin
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104