Chapter 103
Chapter 103
Suhaima yanzu bata da wata matsala yanzu sai tason cigaba da karatun ta kuma tasan komai lokaci ne idan Allah ya nufa zata yi ne. *AFTER 2 YEAR'S* Abubuwa da dama sun faru acikin wad'annan shekarun ta 6angaren Yah Aliyu ya kammala karatun shi na mass com har ya samu aiki a freedom radio a 6angaren labarai, Sabeer kyautar gida yayi mishi don yafi samun sauk'in zuwa wajen aikin da kuma sabuwar mota amman sam Yah Aliyu yak'i kar6a sai dakyar aka shawo kanshi ya kar6a, tuni suka tashi suka dawo cikin gari wannan gidan nasu na kauye kuma suka barwa Mahaifin su bayan Sabeer ya k'ara gyarashi tare da gidan su Babaa Lantana da Baba Adamu, anan aka matsawa mahaifin su Suhaima da yayi aure babu 6ata lokaci ya sami wata mata wadda auren ta d'aya mijin ya rasu ko haihuwa bata yi ba don haka ya aureta suna zaman su cikin kwanciyar hankali. Haka kuma sun samu en uwan Umman su (Fatima) wad'anda suka zo kauyen suna neman su har suka dace wajen samun Baba Umaru, a lokacin aka nemo su Aliyu da Suhaima suka zo don ganawa da family d'in su wad'anda basu ta6a gani ba, sunyi mamaki sosai na ganin irin manyan mutanen da suka zo a matsayin en uwan Umman su, labari aka zauna yi bayan ansha koke koke da neman gafarar juna inda suke ba da labarin su en asalin garin kd ne, ashe Mahaifin su ne maraya ne Mahaifin Fatima ya d'auke shi aiki matsayin drivern shi so daga nan suka fara soyayya babu wanda ya sani bayan ta gama schl ne aka had'a ta aure da wani d'an uwanta wanda bama a k'asar 9ja yake aiki ba tak'i yarda sai tace sai Umar shine kadai wanda zata aura a k'arshe suka gudu sai neman su akayi aka rasa, shine en uwanta suka yi fushi da ita sosai har suka k'i neman ta sai kuma daga baya zuciyoyin su suka yi sanyi aka fara neman su amman ba'a gansu ba sai yanzu Allah ya tak'aita musu wahalar su. Atime d'in da suka ji Fatima ta mutu sunyi kuka sosai iyayen ta sun yafe mata abin da tayi musu, nan fah aka gabatar musu da Suhaima da Aliyu saboda tsabar murna rungume su suka yi, Suhaima da Aliyu sunji dad'in ganin family d'in su sosai, sai yamma suka fara shirin tafiya Aliyu yayi musu alkawarin zasu zo har kd d'in, nan suka tafi kamar kada a tafi haka suke ji. Daren ranar Suhaima take bawa Sabeer labarin komai ya tayata murna sosai, bayan sati d'aya suka shirya suka tafi kd sosai suka yi mugun mamakin ganin irin had'add'un gidajen su ashe manyan en boko ne, en siyasa da kuma en kasuwa da yake Umman su ita kadai ce mace duk maza ne yayyannin ta wajen su bakwai kuma suna raye har da yaran su manya ma. Tar6a sosai suka yi musu ji suke kamar su had'iye su don so tattalin su suke sosai har sukayi kwanak biyu aka zagaya dangi sosai sannan suka dawo gida Suhaima har da kuka ta na rabuwa dasu sun shak'u da Hajia mahaifiyar Umman su sosai. Bayan dawowar su ne Jiddah ta haifi d'anta namiji ansha suna sosai su Suhaima, acikin lokacin ne ita ma Suhaima ta samu ciki sai dai mai sauk'in laulayi ne ba kamar cikin Na'eem da Shaheed ba, Sabeer yaji dad'i sosai sai kula yake bata da tattali kamar shine cikin farko haka ma su Dr Faridah ba'a barsu a baya ba suma sosai suke kulata, haka ta cigaba da rainon cikinta cikin kwanciyar hankali. After 9 months ne Allah ya sauki Suhaima lafiya ta haifi twince d'inta dukka mata tsakanin Sabeer, Mumy, Daddy da Dr Ahmad d'an fillo bansan wanda yafi murna ba acikin su, bayan sun dawo gida nan fah gida ya cika da en uwa da abokanan arzik'i sai taya murna ake na samun wannan karuwar da akayi, washe garin haihuwar ne mutan kd suka taho da abubuwan arziki sosai sai lokacin Mumy take ganin en uwan Suhaima sosai tasha jinin jikinta don tasan bazasu nuna musu komai ba nan zuciyar ta ya dad'a kyashin halinta tabbas ba'a son wulakanta d'an adam don bakasan irin baiwar da Allah yayi mishi ba. Ranar suna yaran suka ci sunan Dr Faridah da kuma Fatima suna kiran su da Shaheeda da kuma Afnan, sosai ansha suna da walima an kashe kud'i sosai a wannan sunan sai fatan Allah ya rayasu. Haka lokaci ya cigaba da tafiya har sukayi arba'in duk family na Suhaima sai da suka je sosai sai da sukayi wurin 1week a kd Hajia sai da ta gyara jikarta sosai sannan suka dawo gida, twince na da 5months Aunty Aliyah ta sake haihuwar mace wadda taci Sunan Suhaima Yah Aliyu ya mayar da sunan k'anwar shi nan aka sha suna aka watse. Duk wani jin dad'i da kwanciyar hankali Suhaima tana samun shi wajen gwarzon mijinta Sabeer, itama ta bashi duk wata kulawa da ta kama zaman su suke cikin jin dad'i, Na'eem da Shaheed tuni Dr Faridah ta sanya su a tsadaddiyar wata prvt schl sai hutu suke zuwa gidan iyayen su don har islamia da tahfiz duk an sanya su ban da extra lesson da ake musu a gidan masha Allah kuma yaran brain nasu naja gasu nutsattsu basu da hayaniya sosai. Bayan wasu en shekaru Shaheeda da Afnan sunyi wayo sosai har an yaye su, a lokacin Sabeer ya samawa Suhaima schl a Buk tana karantar medicine sosai Suhaima ta nuna farincikin ta haka ma Yah Aliyu yaji dad'in barin Suhaima da Sabeer yayi ta cigaba da karatu har godiya yayi wa Sabeer. Ta 6angaren Yah Aliyu kuwa Alhmdllh duk wani bud'i yana samu ta 6angaren aikin shi, gashi sun had'a hannu da Sabeer sun bud'e wani tafkeken gidan gona a kauyen nasu Suhaima da kuma wurin hutawar su inda sunje sosai wajen yayi kyau sun d'ibi ma'aikata suna biyan su, sosai en kauyen sun ji dad'i hakan don an rage masu zaman banza babu sana'a. Duk sunje sunyi aikin hajji da Omarah sun yawata k'asashe sosai musamman Suhaima ma don Sabeer yace honeymoon d'in da basu yi ba suna farkon auren auren yanzu zasu yi shi nan suka zube Shaheedah da Afnan hannun su Dr Faridah suka wuce honeymoon d'in su, sai da sukayi wajen wata hud'u sannan suka dawo gida har da tsarabar ciki. Tun safe take faman zirga zirga a tsakanin kitchen saboda yau Sabeer zai dawo daga tafiyar da yayi ta tsayin wata 1, ta gama had'a mishi abubuwan ci dana sha ta gyara ko'ina sannan ta barwa er aikinta wanke wanke, upstairs ta haye ta shiga d'akin su Shaheedah wanka tayi musu ta shirya su cikin wasu English wears na gown sai dai tsayin ta iyakar gwiwar su ne sannan ta gyara musu gashin kansu style mai kyau tayi musu sunyi matuk'ar yin kyau gashi kayan iri d'aya komai da komai daman kuma komai iri d'aya ake yi musu peck ta basu a cheek nasu suma suka yi mata sannan ta mik'e tsaye tace "Wow! Emmatan Daddy kunyi kyau bari naje nayi wanka sai mu d'auki pic's before jirgin su Daddy yayi landing koh "
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104