Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 77

Chapter 77

A Sanadin Sonki Book 1 Complete Hausa Novel – A Story of Love, Sacrifice and Destiny 1,204 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

min komai don baki da kamata a duniyar nan " Kallon Yah Aliyu tayi kafin ta sauke ajiyar zuciya ta fara zayyana mishi abubuwan da suke faruwa gaba d'aya bata 6oye musu komai ba tana gama fad'in ta sake fashewa da kuka, Aunty Aliyah wadda take kukan tausayin Suhaima ta janyo ta jikin ta tana rarrashin ta. Yah Aliyu kuwa wani zafi zuciyar yake yi sai wani huci mai zafi da yake fitarwa zagaye tsakar gidan yake hannun shi goye a bayan shi ya ma rasa abin cewa can ya bud'e baki cikin kakkausar murya yace "Yau ni Aliyu za'a wulak'anta aci mana mutunci don kawai muna talaka, abin da Sabeer zai aikata mana kenan lallai yau koda bai sake ki ba ni ni Aliyu na sanya almakashi na datse igiyoyin da suke tsakanin ku dashi bake bashi har abadaaaa.......... Aıʂɧąɬ A Mųɧ'ɖ ✍🏻 [4/12, 10:39 PM] Aıʂɧąɬ A Mųɧ'ɖ ✍🏻: *A̺͆ S̺͆A̺͆N̺͆A̺͆D̺͆I̺͆N̺͆ S̺͆O̺͆N̺͆ K̺͆I̺͆* Wྂrྂiྂtྂtྂeྂnྂ bྂyྂ Aྂıʂɧąɬ Aྂ Mྂųɧ'ɖ ɖɛɖı¢ąɬɛɖ ɬơ ɱყ ʂąɖɛɛყ ʂąŋąʑ ♻ *єχ¢ℓυѕινє ωяιтєя'ѕ fσяυм* *PAGE 95-96* Yana sauke wani irin huci Yah Aliyu ya k'arasa maganar ga wasu hawaye na bak'inciki da suke zubo mishi idan ya tuna yanda aka zubar wa k'anwar shi ciki har sau biyu, an cuci k'anwar shi cuta ba k'arama idan ya tuna idan kuma shine iya k'wanta aduniya fa, idan ya kasance iyakar 'ya'yan da zata haifa ne a iya duniya fah shikenan angama cutar k'anwar shi ba ita ba ganin 'ya'yan da zata haifa wasu can daban sun zubar mata dashi. "Inaaa! Bazai yiwu ba dole sai na d'auki fansar abin da akayi wa k'anwata koda zai kasance abu na k'arshe a rayuwashi, an cuce mu don abin da akayi wa Suhaima tamkar shi aka yiwa. Komawa yayi ya zauna tare da janyo Suhaima kusa dashi ya sanya hannun shi ya d'ago kanta suna kallon juna yace "Suhaima baki da kowa sama dani don haka wannan abin da akayi miki sai na d'auki fansar shi koda duk abin da na mallaka a duniyar nan zai k'are " Girgiza kanta Suhaima kawai take cikin kuka take cewa "Nooo! Yaya kada ka kula su na bar mutum da Allah duk wanda yayi min wannan abun shi da Allah " Idanun shi jawur yace "A'a k'anwata baza ayi haka ba sun zalunce ki da yawa bazan kyale su ba don suna tunk'aho su masu kud'i ko suna tunanin zan ji tsoron su to wallahi a'a sai na ja dasu kuma sai nayi nasara " Hannun shi Suhaima ta k'ank'ame tana kuka tace "Na had'a ka da girman Allah Yaya kayi hak'uri ka kyale su idan har kana son ganin farinciki na mu bar wanda ya aikata da Allah da sannu Allah zai saka min " Tsayawa yayi kallon ta na wasu 'yan mintuna kafin yace "Tabbas ina son ganin ki cikin farinciki k'anwata zan kyale su saboda ke kawai".. Rungume shi tayi tana cewa "Yawwa Yaya na nagode " Shafa kanta yayi sannan yace "Allah yayi miki albarka k'anwata, yanzu bari na kai miki ruwa kiyi wanka da sallah kici abinci" "Amin Yaya na " Har ta mik'e ya sake rik'e hannun ta sannan yace "K'anwata kiyi min alkawarin kin rabu da Sabeer har abada " Shiru Suhaima tayi tana mai sunkuyar da kanta ta rasa abin da zata ce ma, ta d'an jima ahaka sannan ta d'ago kanta ta kalli Yaya Aliyu wanda yake kallonta yana jiran me zatace, har ta bud'e bakinta zata yi magana da sauri Aunty Aliyah ta tari numfashin ta tare da cewa "Yaya abar wannan maganar don Allah taje tayi wanka tukunna " Aunty ta fad'i hakan ne don batason Suhaima tayiwa Aliyu alkawari don tasan irin soyayyar da Suhaima da Sabeer suke yiwa junan su rabasu abu mai wahala ne tasan kuma idan ya huce sai ya dawo inda Suhaima take, tasan mak'iya ne basa son ganin su tare musamman 'yan uwan Sabeer da tasan irin k'iyayyar da suke yiwa Suhaima saboda kawai don ta kasance talaka 'yar kauye, tana son Suhaima da Sabeer amman sai ya gane kuskuren shi na yanke hukunci kafin bincike. Sakin hannun ta Aliyu yayi sannan yace "Je ki kiyi wankan " Cikin sanyin jiki ta wuce yayi da Yah Aliyu ya bita da kallon tausayi yarinya k'arama an mayar da ita bazawara auren da ko shekara bai rufa ba, da ace ana dawo da abin da ya wuce da ya dawo rayuwar su baya ko dan ya goge Sabeer daga rayuwar Suhaima, amman ina kaddara ta riga fata Allah ya rubuta sai hakan ya faru dasu zasu rungumi kaddara su koma zasu cigaba da godewa Allah a duk halin da suka tsinci kansu aciki, wasu hawaye ne suka zubo mishi da ya tuna mahaifiyar su da irin bak'incikin da ta fuskanta awajen d'a namiji kafin ta mutu. Baisan ma hawayen na zuba ba sai da yaji hannun Aunty Aliyah suna goge mishi hawayen, cikin sanyin murya tace "Kayi hak'uri Yaya komai tsanani yana tare da sauk'i rayuwar Suhaima zata inganta agaba insha Allah " "Amin mata ta! Na gode da kulawar ki agare ni " Tashi yayi yana kok'arin had'awa Suhaima ruwan wanka nan Aunty Aliyah ta kar6a ta had'a mata sannan ta kai mata toilet. Shiga d'akin ta tayi ta tarar da Suhaima a zaune ko kayan jikin ta bata cire ba nan tayi zaman rarrashin ta kafin ta cire kayan ta d'aura zani ta fita wanka inda Aunty Aliyah take fad'a mata bayan tayi wankan ta zauna cikin ruwan d'umi sosai. Bayan ta gama wankan ne ta sai kayan Aunty Aliyah ta sanya saboda kayanta sunyi datti gashi tafiya bata kwanciyar hankali ba bata taho da wasu ba, abinci ma kasa ci tayi sai fura Aunty Aliyah ta dama ta Yah Aliyu da kanshi yake bata a baki, bayan ya gama bata ne sai tasha paracetamol saboda yanda kanta yake ciwo sosai ta kwanta kan 3siter d'in d'akin Aunty ta lumshe eyes nata hannunta d'aya dafe da kanta, tunanin kawai maganganun da Sabeer yayi mata take da yanda yace ta fice mishi daga gidan shi ya tsane ta, hawaye masu zafi ne suke zubo wa daga eyes nata. Yah Aliyu da Aunty Aliyah ne suka zage wajen gyara mata d'akin Suhaima na da gyara shi sukayi tas, suka share har zasu fito daga d'akin Yah Aliyu ya tsaya kallon d'akin na 'yan mintuna kafin ya sauke ajiyar numfashi yace "Aliyah ya kamata na gyarawa Suhaima d'akin ta yayi kyau sosai duk wani jin dad'i ma zan tanadar mata koda duk abin da na mallaka zai k'are, don haka cikin satin nan zan nemi mai siyan d'ayan gonata na siyar sai na bar d'ayar kawai ta ishemu zaman duniya dai " Gid'a kai Aunty Aliyah tayi kafin tace "Gaskiya kam ka kyauta Allah ya k'ara had'e kanku Allah kuma ya k'ara bud'i " Yana murmishi yace "Amin mata ta " Har zasu fito daga d'akin Aunty Aliyah tace "Ni kuwa ina maganar cigaba da karatun ka da kayi min maganar kwanaki naga baka k'ara cewa komai ba? " "Tana nan maganar don har na samu gurbin karatu na k'arasa secondary yanzu zan zana jarabawar wec da neco" Murmishi Aliyah ta saki tare da cewa "Masha Allah abu

Table of Contents

Chapters

104 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});