Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 4

Chapter 4

A Sanadin Sonki Book 1 Complete Hausa Novel – A Story of Love, Sacrifice and Destiny 1,188 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

yiwa Aliyu saboda yanda take jin jikin nata, yayin da Suhaima take kuka sosai, saboda ganin halin da mahaifiyar tasu take ciki, da gudu Aliyu ya fice daga gidan har yana cin tuntu6e da dutse, yana saurin k'arasa wa gidan Babaa lantana mak'ociyar su, domin neman taimakon ta......... Aishat A Muh'd ✍🏻 [2/4, 11:28 AM] Aıʂɧąɬ A Mųɧ'ɖ ✍🏻: 💝 *A SANADIN SON KI* 💝 *Written by* Aishat A Muh'd ♻ £xclusive Writer's Forum Dedicated to my Sadeey SaNaz PAGE 5-6 Da gudu Aliyu ya shiga cikin gidan Babaa Lantana yana kuka sosai, Babaa Lantana mak'obciyar su fatima ce, mutunci sosai suke yi, tana tsananin tausayin Fatima da yaran ta, ita da mijin ta shi yasa wani lokacin suke taimka musu da abin da Allah ya hore musu, don su ma ba wani kud'i suke dashi ba sai rufin asirin Allah, suna da yarinya d'aya mai suna Aliyah ta d'an girmi Suhaima da kusan shekara hud'u, ita kad'ai Allah ya basu rayayyiya cikin duk yaran da take haihuwa suke mutu. A madafa Aliyu ya tarar da Babaa Lantana tana sauke abinci daga kan murhu, d'ago kanta tayi da sauri ganin yanda aka shigo mata gida kai tsaye babu sallama, mamaki ne ya kamata ganin Aliyu ne ya shigo yana kuka, cikin mamaki tace "Aliyu lafiya, mai ya faru kake kuka? " Cikin rawar murya da hakin gudun da yayi yace "Babaa Lantana ki taimaka mana, Inna ce bata da lafiya gashi ji...... ' Kafin ya k'arasa maganar da yake yi ne, tuni Babaa Lantana ta d'auko fallen zanin ta na atampa a saman igiyar shanya ta lullu6a shi a kanta, ta fita da sauri shima Aliyu ya bi bayan ta, har suna rige rigen shiga gidan. Cikin d'akin suka shige da sauri inda Fatima da Suhaima suke, Fatima sai murk'uk'usun azabar ciwo take tana hawaye, yayin da Suhaima take zabga kuka da k'arfi don ganin halin da Innar su take, da sauri Babaa Lantana da Aliyu suka k'arasa inda take, ganin halin da take ciki ne ya sanya Babaa Lantana cewa "Subhanallah Fatima 6ari ne sannu Allah ya baki lafiya " Kallon Aliyu tayi tace "Aliyu kama hannun Suhaima ku fita tsakar gida " Girgiza kai Aliyu da Suhaima suka yi lokaci d'aya, kafin Aliyu ya iya cewa "Babaa Lantana kiyi hak'uri ki bar mu a wurin Innar mu " Itama girgiza kai tayi tare da cewa "A'a Aliyu kayi hak'uri ku je waje " Dakyar Babaa Lantana ta shawo kan Aliyu ya kama hannun Suhaima suka fita waje, suna waiwaiyar Innar su, da batasan halin da take ciki don ta fara fita a hayyacin ta. Bayan fitar su ne Babaa Lantana ta fara yiwa Fatima dabarin su irin na zamanin da, ganin abin yana kok'arin gagarar ta ne ya sanya ta fito waje inda Aliyu suke raku6e waje d'aya, kallon su tayi wani tausayin su ne ya kamata dakyar ta iya cewa "Aliyu kayi sauri kaje ka kirawo Ladi ungozoma " Gid'a kanshi yayi sannan ya fita da gudu, ita kuma Babaa Lantana ta koma cikin d'akin wajen Fatima, ta bar Suhaima anan zaune tana kuka. Babu dad'e wa Aliyu ya dawo Ladi ungozoma tana bin shi a baya, d'akin da Fatima take ciki ya iya nuna mata da d'an yatsan shi, Ladi ungozoma kuwa wadda ke d'auke da k'aramin buhu a hannun ta na kayan aikin ungomanci irin na zamanin da, ta shige cikin d'akin. Duk yanda suka yi kok'ari wajen kada cikin Fatima ya zube, sai da cikin ya zube sai dai jini yak'i tsayawa sai zuba yake, nan dai ungozoma ta bayar da maganin da za'a jik'a mata ta sha, sannan Babaa Lantana ta biya ta kud'in ta, ta had'a kayan nata ta tafi. Babaa Lantana sai da ta gyara jikin Fatima tsaf da d'akin, sannan ta kirawo Aliyu da Suhaima don su zo wajen ta, sannan ta tafi gida don d'ebowa Fatima abinci don ba k'aramin gala6aita tayi ba sosai, tun da ba wani abincin kirki take samu ta ci ba, da sannu Allah zai saka ita da yaran ta a wajen Umaru, tabbas yaci amana bai rik'e amanar da Allah ya bashi ba ya azabtar da su, duk don son rai irin shi nashi. Suna shiga d'akin wajen Fatima suka nufa, zama suka yi a gefen ta gaba d'aya sun zuba mata suna kallon ta tamkar yau suka fara ganin ta. Kallo d'aya mutum zai mata yasan bata da ishashshan jini a cikin jikin ta, saboda yanda tayi wani fari sosai, gashi ta rame sosai dakyar take iya motsi ma, kallon yaran nata tayu tana daga kwance, wani tausayin sune ya kamata, a hankali wasu hawaye suka shiga zubowa daga idanun ta, bud'e bakin ta tayi wanda ya bushe saman le6en yayi fari tace "Aliyu ga Suhaima nan koda na mutu ka rik'e ta cikin amana, ina horan ka da ka tsaya tsayin daka ku nemi ilimi, don zama da jahilci bashi da amfani, sannan kada ku ce zaku ji haushin mahaifin ku, ku cigaba da yi mishi biyayya koda ya dawo wajen ku, ku kasance cikin yi mishi addu'a Allah yasa ya gane gaskiya, yasan 'ya'ya rahma ne, komai runtsi ina son ka kasance da Suhaima kada ka guje ta, duk laifin da tayi maka kayi hak'uri kai babba ne " D'an dakatawa tayi ta had'iyi yawu sannan ta d'an yamutsa fuska saboda jin yanda marar ta take wani murd'awa wa, cikin kuka Aliyu ya kamo hannun ta yace "A'a Inna baza ki mutu ba, zamu rayu tare da junan mu, don Allah ki daina wannan maganar Inna, hankali na yana tashi wani tunani yana d'arsuwa a zuciya ta sannan gaba na yana fad'uwa " Wani d'an murmishi Fatima tayi tare da cewa "Kayi hak'uri d'ana ni kaina bansan dalilin yi maka wad'annan maganganun ba, ina son duk lokacin da mahaifin ku ya dawo ku sanar dashi na yafe mishi duk abin da yayi min, nima kuma ya yafe ni idan nayi mishi wani laifin a zaman mu, Allah ya albarkaci rayuwar ku, Allah ya raya min ku ya baku ilimi mai amfani ya kuma kare min ku a duk inda kuke 'ya'yana, ku rik'e Babaa Lantana da Baba Adamu a mataayin iyayen ku, don mutanen kirki ne kuma zasu rik'e ku tamkar Aliya 'yar su, duk abin da suka baku shawara kuyi amfani da ita don nasan baza su baku mummunan shawara ba Allah yayi muku albarka " Fatima ta k'arasa fad'in haka tana hawaye sosai, nana Aliyu da Suhaima suka sake fashe wa da kuka sosai, ana cikin Babaa Lantana ta shigo d'akin turus taja ta tsaya ganin su da tayi suna kuka, jikin ta ne yayi sanyi sannn wasu hawaye na tausayin su ya zubo mata, wayance wa tayi tare da fakar idon su don kada su ganta ta goge nata hawayen sannan ta k'arasa inda suke tace "Haba Fatima taya zaki na saka su a gaba kina kuka suna yi, ke da zaki rarrashe su ki kwantar musu da hankali " Murmishin yak'e kawai Fatima tayi, nan Babaa Lantana ta rarrashe su dakyar suka yi shiru, sannan ta basu abincin suka fara ci hannu baka hannu kwarya. Sannan ta d'ago Fatima a hankali ta kara mata kofin madarar shanu

Table of Contents

Chapters

104 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});