Chapter 87
Chapter 87
yi da yanda yake kallon su ne ya sanya su sakin murmishin yak'e tare da yi mishi sannu da zuwa, amsa musu yayi kawai yana sake bin su da kallon ban yarda daku ba. Zuciyar Suhaima da ta Aliyah tamkar zasu faso kirjin su ta fito saboda yanda take bugawa sam basu yi tsammanin ganin Yah Aliyu yanzu ba sun sakankance sai da yamma, musamman Aunty Aliyah tafi kowa tsorata tayi dana sanin sanya Sabeer shiga cikin d'akin Suhaima yanzu idan ya fito daga d'akin batasan hukuncin da Aliyu zai d'auka ba akanta don itace da wannan shishshigin, gashi kafin ya fita sai da tasha gargad'i kada ta sake tsakanin Sabeer da Suhaima magana ta had'a su, nan ta fara addu'a Allah ya sanya kada Sabeer ya fito. "Wai lafiyar ku qlau kuwa? " Cikin sauri Aunty Aliyah tace "Me kagani? " "Gani nayi kunyi wani tsuru tsuru sai rarraba ido kuke kamar marasa gaskiya " "A haba ba komai, lafiya ka dawo yanzu? " "Nayi mantuwa ne " Yana gama fad'in haka ya wuce d'akin su da sauri don kuwa sauri yake, bai dad'e ba ya fito daga d'akin ya fice daga gidan, sai lokacin suka saki ajiyar zuciya ta kwanciyar hankali. "Aunty kinga abin da nake tsoro koh da yanzu ya gane fah " Aliyah wadda jikinta ya mutu saboda tsoro ta aro dauriya tace "Kai dai Allah ya kiyaye kawai ba don haka ba da yau zanyi bayani don nice da laifi " Suhaima dariya ce ta kubce mata ganin Aunty Aliyah na goge zufa tace "Haba Aunty kinsan Yah Aliyu bazai iya ce miki komai ba sai dai kisha harara da mita " "Ke kyale Yayan nan naki kawai idan ya fusata " Cup d'in da ta had'a wa Sabeer tea ta mik'o mata tare da cewa "Gashi ki kai mishi da zafin shi yasha kada ya huce gashi jiya fah bai samu cikakken bacci ba don nasan ruwan nan ya jik'a shi sosai " D'an ta6e baki Suhaima tayi kan tace "Allah Aunty kina son wanann guy d'in ya rainani da yawa bakisan haushin shi nake ji ba wallahi " "Hakuri zakiyi Suhaima kinsan kowanne d'an adam da irin tashi k'addarar Allah ya riga ya tsara hakan sai ya faru tsakanin ku" Kar6a tayi kawai ta tafi tana zum6ura baki Aunty Aliyah ta bita da kallo tana murmishi kawai. Tana shiga d'akin ta ajiye cup d'in tea saman drower na gefen gado ta jiyo da niyyar fita daga d'akin taji an janyo hannun ta da d'an k'arfi wanda ya sanya d'an kwalin kanta mai santsi ya zame lallausa dogon gashin kanta ya tarwatse, bata tsaya ko'ina ba sai saman faffad'an kirjin shi har sai da d'an kanta ya bige kad'an, kallon shi tayi da niyyar yi mishi tsiwa sai dai suna had'a ido duk wani abu ya kunce mata kallon junan su kawai suka tsaya yi cikin wani irin shauk'i da tsananin kewar junan su............ Aıʂɧąɬ A Mųɧ'ɖ ✍🏻 [4/22, 8:52 PM] Aıʂɧąɬ A Mųɧ'ɖ ✍🏻: *A̺͆ S̺͆A̺͆N̺͆A̺͆D̺͆I̺͆N̺͆ S̺͆O̺͆N̺͆ K̺͆I̺͆* Wྂrྂiྂtྂtྂeྂnྂ bྂyྂ Aྂıʂɧąɬ Aྂ Mྂųɧ'ɖ ɖɛɖı¢ąɬɛɖ ɬơ ɱყ ʂąɖɛɛყ ʂąŋąʑ ♻ *єχ¢ℓυѕινє ωяιтєя'ѕ fσяυм* *PAGE 106-107* Kallon shi tayi da niyyar yi mishi tsiwa sai dai suna had'a ido duk wani abu ya kunce mata kallon junan su kawai suka tsaya yi cikin wani irin shauk'i da tsananin kewar junan su tare da wata irin zazzafar kauna, sun d'auki wajen 5 minute suna aikawa da junan su kallo yayin da Sabeer ya kasa jure kallon da suke aikawa junan su ya fara matsar da fuskar shi saitin fuskar ta da niyyar yayi kissing d'in cute pink lips nata wanda yayi tsananin missing d'in su a lot. Jin saukar numfashin shi kusa da hancin ta sosai ya sanya Suhaima dawowa cikin hayyacin ta ta daddage ta fiske jikin ta daga jikinshi, sai dai yanda ta fisgi jikin nata ne ya sanya ta tafiya baya da d'an k'arfi kamar zata fad'i k'asa yayin da Sabeer wanda gaba d'aya kasala ta baibaye shi ya biyo ta shima. Sauran kad'an Suhaima ta saki ihu na tsoro sai taji ta fad'a saman bed yayin da Sabeer ya biyo ta shima cikin jikinta, lokaci d'aya suka sauke wata ajiyar zuciya sai dai kowannen su da banbancin ajiyar zuciyar tasu Suhaima ita ta jin dad'in bata fad'i k'asa ba shi kuma Sabeer na jin shi rungume da Babyn shi a jikinshi wanda ya d'auke tsayin lokaci da su had'u kamar haka. Kok'arin tashi take amman ya wani rik'e ta k'am kamar wanda za'a kwace mishi itaa haushi ne ya ishe Suhaima ta d'aure fuska cikin fusata tace "Malam wai me kake nufi ne haka ni ka d'aga ni wallahi ko nayi maka ihu " Murmishi Sabeer yayi kafin yace "Haba Baby nah kinsan nayi missing d'in ki da yawa ki barni ko na samu kwanciyar hankali da nutsuwa cikin zuciya ta " Haushi ne ya k'ule Suhaima don haka tace "Kada ka mance da bakin ka kace min ka tsane ni me yasa zaka zo inda nake nima kasani na dad'e da tsanar ka tun lokacin da ka furta min haka " Jikin Sabeer ne yayi wani irin sanyi wanda Suhaima har ta samu ta ture shi daga jikinta ta mik'e tare da d'aura d'an kwalin kanta ta wani kalle shi taja tsaki ta fice daga d'akin gaba d'aya. Tana fitowa suka had'a ido da Aunty Aliyah da take zaune can gefen kitchen tana aiki, sake d'aure fuska Suhaima tayi don duk ita taja gashi ba don tayi kok'arin yakice shi ba da tuni ta bada kai bori ya hau, don haka ta samu waje ta zauna kawai ko kula Aliyah bata yi ba, sauran kad'an dariya ta kubce wa Aunty Aliyah amman ta danne ta kada ta janyo tayi mata kuka da rigima don kad'an daga aikin Suhaima don haka taja bakinta tayi tsit ta cigaba da aikinta. Wani zafi da zugi ne yake ji cikin zuciyar shi kalaman Suhaima ne kawai suke fad'o mishi a rai da jan tsakin da tayi mishi don yaji ta ya dad'e kwance a haka yana tufka da warwara tare da yin d'unbin nadamar abin da yayi dakyar ya iya shiryawa cikin wani jeans blue da T-shirt fara mai k'aramin hannu ya d'an fesa perfumes kan ya zauna ya sha tea d'in da ya fara sanyi ma. Yana gama sha ya mik'e ya d'auki kayan shi ya rik'e mai dattin a d'ayan hannun ya fito waje kallon Suhaima ya d'an yi kan ya kalli Aunty Aliyah yace "Auntyn mu nagode bari na d'an fita waje ko zanga Ashiru don bamu had'u ba tun da nazo " "Toh Sabeer sai ka dawo, amman ina zaka tafi da kayan nan masu datti haka a hannu? " D'an murmishi yayi yana cewa "Anjima zan wanke su ne zan ajiye su a inda nake kwana " Tausayin Sabeer ne ya kama Aunty Aliyah tasan bai ta6a tsammanin zai yi irin wannan kwatankwacin rayuwa ko zuwan da yayi na farko baya yin wanki Yah Aliyu ne yake had'a wa ya wanke musu da nashi. Aıʂɧąɬ A Mųɧ'ɖ ✍🏻*A̺͆ S̺͆A̺͆N̺͆A̺͆D̺͆I̺͆N̺͆ S̺͆O̺͆N̺͆ K̺͆I̺͆* Wྂrྂiྂtྂtྂeྂnྂ bྂyྂ Aྂıʂɧąɬ Aྂ Mྂųɧ'ɖ ɖɛɖı¢ąɬɛɖ ɬơ ɱყ ʂąɖɛɛყ ʂąŋąʑ ♻ *єχ¢ℓυѕινє ωяιтєя'ѕ fσяυм* *PAGE 106-107* Kallon shi tayi
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104