Chapter 40
Chapter 40
shigowa mutane gida kai tsaye tun kafin a amsa mishi sallamar a bashi izinin shigowa sai kace a gidan arna " D'an murmishi yayi yana girgiza kai don yaji ta tsaf sai kawai ya tashi ya koma zaure sannan yayi sallama mamaki sosai Suhaima taji da taji ya koma sai da ta d'an jima kafin ta amsa mishi sallamar sannan ya shigo yaja kujera ya zauna lokacin har ta gama yankan salad d'in. Shiru taji bai yi magana ba sai ta d'an d'ago kad'an ta kalleshi duk ya rame yayi d'an bak'i kad'an kamar ba Sabeer ba, gani tayi zai kallo inda take ya sanya ta kauda idonta da sauri zata tashi kenan taji muryar shi cikin sanyi yace "Baby taimaka min da abinci I'm very hungry wallahi please " Yi tayi kamar bata ji shi ba ta wuce kitchen kafin ta fito ta wanke salad d'in duk yana kallon ta don tayi mishi kyau cikin wata gown ta atampha duk da basu kamata ba d'inkin amman sun zauna cif a jikin ji yake kamar ya sanyata cikin jikin shi ya dunga fad'a mata irin son da yake mata ko ya samu sassaucin da yake ciki. Ya fad'a dogon tunani yana yi yaji kamshin turaren Suhaima a kanshi da sauri ya d'ago kanshi ya kalle ta tana tsaye hannun ta d'auke da plate na abinci tana mik'a mishi, hannun shi ya sanya ya kar6a hadda ta6o mata 'yan yatsun ta saboda tsokana yak'i kar6ar plate d'in aikuwa wani irin shock Suhaima taji ajikinta wanda bata ta6a jin irin shi ba da sauri ta saki plate d'in nan yayi saurin tarewa yana sakin murmishi ganin irin yanayin da ta shiga ajiye abincin yayi yana kallon shi shinkafa da wake ne sai salad da mai da yaji gefe d'aya a saman abincin ga kifi nan an sanya sosai abincin ya bashi sha'awa. "Uhm sauran ruwa Baby " Ya fad'i hakan a lokacin da Suhaima take kok'arin shiga d'akin ta ta huta don ta gaji tun safe take aiki, haushi ne yake kamata tun lokacin da Sabeer ya koyi ce mata Baby kuma ko a gaban su Yaya Aliyu haka yake fad'a mata, komawa tayi kitchen ta samu jug k'arami mai murfi ta d'ebo mishi na randa mai sanyi ta kawo ta dangwarar mishi a gaban shi. "Sannun ki Baby nah Allah ya bani ke " Ko kallon shi bata yi ba ta juya ta wuce d'aki sai kawai taji zuciyar ta tak'i aminta ta furta ba Amin ba daga addu'ar da Sabeer yayi. Cikin kwanciyar hankali ya fara cin abincin yayi mishi dad'i sai dai ko rabi bai ci ba ya ture shi saboda yayi mishi yawa yasan da gayya ta zubo mishi da yawa, yana nan zaune ya fara jiyo muryar Aliyah k'asa k'asa tana kiran Suhaima daman yinin yau a d'aki ta yini bata jin dad'in jikinta. Jin wannan kiran yasan Suhaima bazata ji ba ya sanya shi tashi ya nufi d'akin Suhaima ya shiga ba tare da neman izinin ta ba tana kwance saman bed tayi kwanciyar ringingine tana duba littafin addu'o'i. Tsayawa kallonta kawai ya tsaya yi don wannan kwanciyar ba k'aramin sanya shi a wani yanayi na daban, Suhaima ji take kamar ana kallon ta sai ta kawar da littafin daga saitin fuskar ta fuska a d'aure tace "Malam lafiya zaka shigo min d'aki ba neman izinin? " D'an sosa kai yayi kafin yace "Aunty Aliyah tana kiran ki " Yana gama fad'in haka ya fita, d'an tsaki taja kafin ta mik'e ta fita d'akin Aliyah ta shiga sai ta tarar da ita cikin wani hali don nak'uda ce ganga ganga ta taho mata da sauri ta k'arasa inda take durk'ushe ta rik'o ta tana kuka. Sabeer zai fita kenan yaji kukan Suhaima nan ya fara kiran sunan ta hankalin tashe gashi bashi da damar shiga d'akin, nan Aliyah dakyar ta fad'awa Suhaima taje ta kirawo mata Babaa Lantana. Tana fitowa taci karo da Sabeer wanda yake tsaye a bakin k'ofar hankalin shi a tashe kamar ya fad'a d'akin haka yake jin shi. Ganin Suhaima zata fita yasa shu rik'o hannun ta yace "Baby what wrong with U? " Kamar ta share shi sai kuma tace "Aunty ce zata haihu tana shan wahala " "Innalillahi bari naje na kirawo Yaya da Babaa Lantana ki zauna kusa da ita " Da sauri ya juya ya fita yayin da Suhaima ta koma cikin d'akin, babu dad'e wa da fitar shi sai ga Babaa Lantana da Aliyu sun shigo gidan tare da Sabeer nan suka shiga cikin d'akin ban da Sabeer wanda yake tsaye zuciyar fal tausayin Aliyah. Yana nan tsaye Suhaima ta fito tana kuka da Aliyu wanda idanun shi suka yi ja na tausayin halin da matar shi take ciki akabar Babaa Lantana a cikin d'akin "Ya kamata mu tafi hospital " Cewar Sabeer da ya matso kusa da Yaya Aliyu, d'an girgiza kai Aliyu yayi kafin ya bud'e baki yayi magana sun ji kukan jariri. "Alhamdullilah " Suka furta gaba d'aya suna nan tsaye Babaa Lantana ta fito fuskarta d'auke da farinciki tace "An sauka lafiya mun samu namiji " Nan fuskar su ta fad'ad'a da fara'ar farinciki, Suhaima mai kuka ta dawo dariya har da buga tsallen murna ta rungume Yayanta, kallon su Sabeer yake cike da sha'awa daman shima yana da k'anwa ko Yaya wanda suka fito ciki d'aya da shima ya nuna mishi irin son da yaga Aliyu da Suhaima da suke yiwa junan su. Suhaima ruwa ta d'ora kan wuta bayan ta hura itace bayan yayi zafi ne ta kwashe takai toilet sannan ta d'ebo wanda za'a yiwa jariri wanka ta kai d'akin Aliyah inda har Babaa Lantana ta gyara ko'ina fes ta sanya turaren wuta na kamshin d'akin. "Sannu Aunty Aliya " Suhaima ta furta tana rik'o hannunta fuskarta d'auke da murmishi, "Yawwa kanwata ke ma sannun ki " Kamata Babaa Lantana tayi ta kaita band'aki wanka tayi mata suka fito sannan tayi wa jariri lokacin da suka gama tsaf suka shirya sai ga Yaya Aliyu nan da taxi ya taro zasu je asibitin da Jiddah ta kaisu lokacin tana laulayin ciki. Suka tafi aka bar iya Suhaima a gidan tana dad'a gyarawa, bayan ta gama ne sai tayi wanka ita ma ta fito d'aure da zanin wanka ko hijab bata sanya ba da yake tasan a tunaninta Sabeer ya bi su hospital ne. Tsayawa tayi bayan ta fito daga wankan tana taje dogon gashin kanta ta sunkuyar da kan gashin yayi gaba tana taje shi, bayan ta gama irin ta d'ago kanta gashin yayi baya sai a fuskar Sabeer wanda shigowar shi kenan gidan, ya hango ta tana taje kanta. "Wash! kin sanya min gashi a ido da bakina fah" A d'an tsorace Suhaima ta jiyo jin muryar Sabeer a kusa da ita, suna had'a ido nan gabanta ya hau fad'uwa ganin irin kallon da yake jifanta dashi idanun shi har sun fara canja launi, na shiga uku ni Suhaima daman wannan mutumin bai bi su ba, ta fad'i hakan cikin zuciyar ta tana mai ja da baya shima yana bin ta da haka har bayanta ya jingina da bangon d'akin ta sai kawai ta runtse ido tare da k'ank'ame jikinta
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104