Chapter 33
Chapter 33
d'aya cikin jikokin shi, anya shine kuwa da hankalin shi ya aikata wannan abin ko dai mafarki yake yi ba gaske ba ne kamar wani mutum mutumi haka ya koma ya rasa me zaiyi ma. Dakyar Daddy ya lalla6a su Mumy da Hajjah suka fita don a bawa Doctor damar duba Sabeer haka Daddy yazo ya janye Alhj Ahmad dakyar suka fita tare da jan k'ofar bedroom d'in. Likita yana cikin duba Sabeer yaga ya bud'e idon shi tare da tashi ya zauna cike da mamaki Doctor yake kallon shi, kamo hannun likitan Sabeer yayi sannan yace "Doctor ina son abin da zan fad'a maka yanzu ka sanar da iyaye na bana son a samu matsala fah" Gid'a kai likita yayi kafin yace "Okay baza'a samu matsala ba insha Allah " A hankali Sabeer ya matso kusa da likitan kafin ya fara yi mishi magana cikin k'asa k'asan murya, bayan ya gama yi mishi maganar ne ya koma ya kwanta tare da rufe idon shi. Suna zaune jugum jugum a parlour kowannen su ya rafka tagumi suna tunani ba mai yin magana a tsakanin su, k'arar bud'e door suka ji da sauri suka mik'e tsaye tare da nufar Doctor da sauri kowanne na jefo mishi tambayar jikin Sabeer. D'an share zufa likitan yayi yayi shiru baiyi magana ba, cakumar wuyan shi Alhj Ahmad yayi tare da cewa "Kai wanne irin wawa ne muna maka magana ya jikin Sabeer zaka zuba mana ido kana kallon mu kamar ka samu tv" Ba k'aramin shak'a likita yasha ba dakyar Daddy ya cire hannun Alhj Ahmad daga wuyan shi, kafin yace "Abba mu bi a hankali please " Zama suka yi sannan likita ya shafa wuyan shi tare da jujjuya shi yace "A binciken da nayi damuwa ce tayi wa Sabeer yawa sosai wanda a yanzu yana d'auke da hawan jini, idan kuka cigaba da matsanta mishi da 6acin rai ko ku k'i mishi abin da yake so idan ranshi ya 6aci zuciyar shi zata iya bugawa na lokaci d'aya don haka ku kiyaye " "K'arya kake zuciyar Sabeer bazata ta6a bugawa ba " Cewar Alhj Ahmad cikin tsawa gaba d'aya hankalin shi a tashe yake, "a cigaba da kwantar mishi da hankali a bashi abin da yake so, zanje na kawo maganin da zai sha yanzu " Babu wanda ya kula shi haka ya zame ya tafi sannan suka shiga cikin d'akin inda Sabeer yake kwance, nan Alhj Ahmad ya zauna kusa dashi tare da rik'o hannun Sabeer yana mai nadamar abin da yayi mishi, a lokacin Daddy ya kirawo mai gyaran k'afa ya fara gyarawa Sabeer kafar shi kuka sosai Sabeer yasha shi a lokacin haka Hajjah da Mummy tare da Alhj Ahmad sun zubar mishi da hawayen tausayi Daddy ne kawai yayi dauriya ta rik'e Sabeer har aka gama gyara mishi kafin daga k'arshe wani wahalallen bacci ya sake d'aukan shi sai sauke ajiyar zuciya yake....... Aishat A Muh'd ✍🏻 [2/6, 8:12 PM] Aıʂɧąɬ A Mųɧ'ɖ ✍🏻: *A SANADIN SON KI* Written by Aishat A Muh'd Dedicated to my Sadeey SaNaz Dis page is dedicated to my Biebie dee ina tayaki murnar k'arin shekara Allah ya k'aro shekaru masu albarka Allah ya baki miji nagari wanda zai kular mana dake muzo musha biki 💃🏻😍😅. _fan's kuyi hak'uri akan rashin yi muku typing kwana 2 akwai uzirin da ya dakatar da ni but yanzu insha Allah zan cigaba da yi muku daidai iyawata, inason ku oll my fan's_❣ *PAGE 48-49* Sai after mangarib Sabeer ya tashi daga wahalallen baccin da ya d'auke shi, lokacin da ya tashi zugin k'afar ya ragu babu laifi nan ya yunkura ya tashi bathroom ya shiga alwala yayi ya fito yana d'ingishi haka ya gabatar da sallahr la'asar da ta tsere mishi tare da mangarib, bayan ya idar ya zauna yin addu'o'in neman za6in Allah akan neman auren Suhaima, da haka har aka kirawo sallahr ishsha ya gabatar. Bayan ya idar ne ya tashi ya shiga bathroom wanka yayi da ruwa mai d'umi kafin ya fito ya shirya cikin sleeping dress koma wa yayi ya kwanta a ringingine ya fad'a kogin tunani, ta yanda zai tunkari k'auyen su Suhaima don neman soyayyar ta, yana cikin haka 'yan uwan shi da k'annen Daddy da kuma matansu suka shigo duba Sabeer, dakyar ya iya k'ak'alo yak'en dole ya sanya saman fuskar shi yana amsa musu sannun da suke mishi, kowanne fuskar shi da tausayin Sabeer ganin yanda k'afar shi ta kumbura sai wurin 9 na dare suka bar bedroom d'in nashi wanda har zuwa lokacin ba ga Mumyn shi ba da Hajjah. Bayan fitar su babu dad'e wa Daddy ya shigo bedroom d'in bayan shi kuma 'yar aikin Mumy ce da babban plate a hannun ta saman shi cike da kaya ajiyewa tayi saman k'aramin table d'in d'akin sannan tayi wa Sabeer sannu da jiki ko amsawa bai yi ba ta fita don shi ba wannan ne a gaban shi ba. "Son ya kake jin jikin naka?" D'an yatsina fuska yayi kafin yace "Daddy na samu sauk'i" D'an ajiyar zuciya Daddy ya saki tare da cewa "Allahmdullilah Son naji dad'in abin da ka ce, oya zo kaci abinci nasan rabon ka da abinci tun breakfast da kayi " Girgiza kai Sabeer yayi tare da cewa "Na k'oshi Daddy" D'an zaro ido yayi tare da cewa "What! Son kanason illata kanka ne? " Sai kuma ya sassauta murya cikin sigar rarrashi yace "Haba Son tun da na amince da buk'atar ka ya kamata kaci wani abin zan jure duk wata matsala da zan fuskanta a wurin Abba, Hajjah da kuma Mumyn ka duk don farincikin ka ". Kallon Daddy yayi sai yaga kamar ya fad'a a fuskar shi wani tausayin Daddy ne ya kama Sabeer har yana kok'arin fitar da kwalla duk don farincikin shi Daddy ya zama haka, yasan yanda bai ci wani abincin kirki ba yinin yau haka shima ya zauna. Tashi tsaye Sabeer yake kok'arin yi da sauri Daddy ya taimaka mishi ya tashi tsaye zuwa saman kujera wanda kujeru guda biyu ne kacal daga gefe tsakiyar su kuma table ne nan Daddy ya zaunar da Sabeer a d'aya daga cikin kujerar, sannan shima ya zauna a baki ya fara baiwa Sabeer abinci haka shima Sabeer yake bawa Daddyn shi a baki. Bayan sun kammala ci ne Daddy ya lalla6a Sabeer yasha maganin shi don sam baya k'aunar shan magani, k'ofar bedroom d'in aka bud'e aka shigo kallo d'aya Sabeer yayi mata ya d'auke kanshi gaban shi yana fad'uwa, Mumy ce ta shigo fuskar ta a had'e babu alamar fara'a bata yiwa kowa magana ba ta wuce bathroom babu dad'ewa ta fito hannun ta rik'e da wani d'an madaidaicin bowl ruwan d'umi ne a cikin shi sai wani small towel a hannun ta. Inda Sabeer yake ta nufa tana zuwa ta zauna kan carpet tare da d'aukan k'afar Sabeer mai ciwon ta d'ora saman k'afar ta, towel d'in ta sanya cikin ruwan d'umin ta fara gasa k'afar Sabeer, daga Sabeer har Daddyn babu wanda ya samu fuska wajen Mumy balle su yi mata magana, runtse ido Sabeer yayi wani rad'ad'i da zafi yana shiga cikin zuciyar shi gefe d'aya na cikin zuciyar shi kuma yana tunanin hanyar
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104