Chapter 38
Chapter 38
labule na k'ofa dana window kafin su fito kuma su shiga d'akin Aliyah sai ga Aliyu ya fito da k'aramar katifa ta k'aramin gado ya sanya d'akin Aliyah kuma ta shimfid'a mishi zanin gado a jikin katifar ta kunna turaren wata na tsinke sai d'akin ya fito fes dashi, Aliyu ya d'auki jakar Sabeer ya shigar mishi da ita kafin kuma su d'unguma shi da Sabeer su tafi masallaci don yin sallahr ishsha.... Aishat A Muh'd 💃🏻 [2/18, 5:01 PM] Aıʂɧąɬ A Mųɧ'ɖ ✍🏻: *A SANADIN SON KI* Written by Aishat A Muh'd Dedicated to my Sadeey SaNaz PAGE 53-54 Bud'e labulen d'akin Aliyah tayi tare da shigowa zama tayi kusa da Suhaim wadda ta kwanta rub da ciki a saman gadon ta, dafa bayan ta tayi kafin tace "Suhaima tashi mu yi magana " Tashi Suhaima tayi zaune tana goge hawayen fuskar ta da hannunta, kallon mamaki Aliyah take mata kafin tace "Me yasa kika yi mishi haka Suhaima?, haba Suhaima bansan ki da halayyar wulak'anta mutane ba, ki tuna saboda sanadin son ki fah ya bar gatan shi da komai nashi na jin dad'i ya dawo nan k'auye wanda bai ta6a rayuwa acikin irin wannan yankin ba ya aminta zai jure kowacce wahala indai zai same ki, koda da iya abincin mu ma kafin ya saba aiki ne zai hak'ura ya jure duk don A SANADIN SON KI, haba Suhaima ki tausaya mishi kada ki bashi wahala don na tabbatar Sabeer son ki yake tsakani da Allah ba yaudarar ki yake, idan yaudara ce ma bazai zo har nan ba don haka kiyi tunanin kafin ki yanke hukunci tukunna " Zum6ura baki Suhaima tayi tare da cewa "Ni gaskiya Aunty bana son Sabeer hasalima kinsan na tsani auren mai kud'i saboda gujewa wulak'anci, musamman gidan su Sabeer tunda na baki labarin abin da suka yi min" D'an shiru Aliyah tayi tana d'an tunani kafin tace "Kina da gaskiya don wannan amman ni ina mai baki shawara kiyi tunani sosai kafin ki yanke hukunci,tare da addu'ar neman za6in Allah kada ki yanke hukunci da gaggawa" Gid'a kai Suhaima tayi kawai tare da cewa "Ni bama zan so shi ba" "Hmmm na dai ji ki Suhaima kawai amman wannan zakad'ed'en sauryin ne kece bakya sonshi kawai ra'ayin ki ne ya hana ki tsayawa kiyi tunanin kin fad'a son Sabeer daga irin kallon da kike mishi d'azu " Wayyo aikuwa Suhaima ji take kamar ta rusa kuka jin abin da Aunty Aliyah ta fad'a mata, zum6arar baki tayi tare da kwanciya ta juyawa Aliyah baya, abin ya bata dariya tashi tsaye tayi tare da cewa "Abincin ki yana kitchen fah kije ki ci kada ya huce " Tana gama fad'in haka ta fito daga d'akin, nan ta tarar da Sabeer da Aliyu sun dawo bayan tayi musu sannu da dawowa ta yiwa Sabeer sai da safe ta wuce cikin d'aki. Sun d'an jima suna hira kafin Sabeer ya wuce d'akin da aka sauke shi bayan yayi wa Aliyu sai da safe, yana tafiya yana waiwayar d'akin Suhaima ko Allah zai sanya ya hango ta don kuwa yana son sake sakata cikin idanun shi kafin yayi bacci, Aliyu yana kallon yanda yake kallon d'akin Suhaima nan ya sake tabbatar wa Sabeer yana son Suhaima bana wasa ba, amman mene dalilin k'in amincewar Suhaima na ta kar6i soyayyar Sabeer?. Sabeer yana shiga d'akin sai yaji shi kamar wanda aka sanya shi a akurki duk da d'akin yana da d'an girma kuwa hakan bai hana sa Sabeer ganin k'ank'antar shi ba irin wanda ya saba kwanciya da shi ba. Zama yayi gefen katifar yaji ta tik'irk'ir tauri sosai, ga wani hucin zafi da d'akin yake fitarwa alamar dai ba'a yin amfani dashi a rufe yake sai shegen kukan sauro da ya addabi kunnen shi, ga ba wadataccen haske wata 'yar k'aramar fitila ce kawai a rataye jikin k'usa a bango mai irin mai batir d'in nan, zabga tagumi Sabeer yayi yana tunanin yanda ya tsinci kanshi inda bai ta6a tsammanin ganin a haka ba koda a mafarki sai gashi kwatsam lokaci d'aya ya tsinci kanshi aciki ikon Allah kenan. Zumbur ya mik'e kamar wanda aka tsikara sakamakon wani fitsari da ya matse shi, wayyo Allah nah yanzu ta ina zan fara shiga toilet d'in su, fad'in haka cikin zuciyar Sabeer yana faman matse k'afa, fuskar nan tashi tayi kalar tausayi tamkar wanda zai fashe da kuka kasa jurewa yayi kawai ya tashi da sauri ya fito daga d'akin zuwa tsakar gidan. Ba kowa a tsakar gidan ga duhu yayi tsit kake ji, yana nan tsaye sai ga Suhaima ta fito a d'aki zata shiga kitchen d'ebo ruwa suka kusan cin karo da Sabeer saboda duhu gashi babu wadataccen hasken farin wata, ba k'aramin tsorata tayi ba ta d'auka ko wani aljanin ne amman lokacin da ta fuskanci Sabeer ne sai kawai ta dake tare da d'aure fuska zata wuce daga sauri yasha gabanta ya tsaya "Malam lafiya? " "Uhm ina son ki nuna min toilet " Da hannu ta nuna mishi ba tare da tayi magana ba ta wuce shi ta d'auko ruwan ta shige d'aki ko kallon inda yake bata sake yi ba, buta ya d'auka ya wuce cikin toilet d'in a d'an tsorace, duk da a duhu ne hakan bai sanya shi gane tsabtar da band'akin yake dashi ba a tsorace yayi abin da zai yi ya fito yana share gumi sai kace wanda yayi tseren gudu duk gumin tsoro ne, da sauri ya wuce d'akin ya rufe kafin ya kwanta saman katifar. A cikin wannan daren ya zame wa Sabeer daren da bai ta6a tsammanin zai irin shi a wannan duniyar ba saboda yanda zafi da sauro suka hanashi runtsawa, idan zafin ya isheshi sai ya cire kayan jikin shi iya vest da 3quater ne kawai a jikin shi sai buge bugen sauro yake yi ko baccin kirki ya kasa samu ga wani tsananin ciwon kai da ya kamashi saboda gajiya ga rashin bacci. Washe gari kuwa jikin Sabeer yayi luhu luhu da cizon sauro abin ka da d'an hutu kuma farar fata duk tayi ja tundaga fuskarshi kuwa har jikin shi inda kaya bai rufe ba, idanun shi sun yi ja sosai ga wani zazza6i da ciwon kan ya saukar mishi dashi wajen asubah, har gari ya waye yana kwance a d'aki bai iya fitowa ba sai da Aliyu ya shiga ya ganshi kwance sai rawar sanyi yake ya tukunkune waje d'aya. Cikin tashin hankali Aliyu ya k'arasa tare da cewa "Subhanallah! Sabeer baka da lafiya ne? " D'an murmishin yak'e yayi hawaye na zuba a idanun shi na zafin ciwo yace "Zazza6i ne yake damuna da ciwon kai ko zaka taimaka min da paracetamol? " "Sannu Allah ya baka lafiya, bari na d'auko maka amman ka d'aure ka fito sai kayi brush kaci wani abin kafin ka sha maganin " D'aga kai kawai Sabeer ya iya yi sannan Aliyu ya taimaka mishi suka fito tsakar gidan bayan ya d'auko mishi maclean da brush nashi cikin bag d'in da ya taho da ita. Aunty Aliya da Suhaima suna zaune a kan tabarma ga breakfast a saman tabarmar da yake tare suke karyawa, Aunty Aliya batasan sand ta mik'e tsaye ba
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104