Chapter 43
Chapter 43
nan ta fara shara gyara gidan tsaf tayi sannan tayi wanke wanke da wanke toilet kafin ta wuce d'akin Aunty Aliyah ta gyara mata shi tsaf ta sanya turaren wuta, kallonta kawai Aunty Aliya take saboda ganin yanda take rama gashi kana kallon face nata zakasan tana d'auke da damuwa, har ta gama sanya turaren wuta ta fita daga d'akin tana kallonta ajiyar zuciya ta sauke tana mai taya Suhaima da addu'a Allah ya yaye mata abin da yake damunta. Agurguje tayi wanka ta shirya cikin wasu kaya pakistan dogon wando white ne sai rigar da tsayinta wajen gwiwar ta ne itama farace rigar sai touch d'in flower's blue ajikin gaban rigar body spray ta fesa bayan ta shafa powder da man le6e, tayi kyau duk da ba wani make up tayi ba. Hijab dogo mai hannu blue colour ta sanya sannan ta zura flat shoes akafanta white ta fito ko d'akin Aunty Aliya bata shiga ba ta fita, a k'ofar d'akin da Sabeer yake ta tsaya tana son shiga tana kuma tsoro gabanta sai fad'uwa yake, ta dad'e a haka kafin dakyar ta iya d'aga kafarta ta shiga d'akin sai dai kuma wayam babu kowa sai dai da alama bai dad'e da fita ba don ga kaya a zube a k'asa wanda ta ganshi ya sanya da safe. Da sauri ta k'arasa shiga ta tattara d'akin ta gyara ta share shi tas sannan ta hango wani diary nashi akusa da pillow d'auka tayi ta fara karanta wa. Tun da ta fara karantawa take kuka a hankali har takai da ta bud'e baki sosai tana kukan tausayin Sabeer daman ashe haka yake sonta, me yasa ta wulak'anta shi da tasan haka yake sonta da a lokacin da ya furta mata so ta amince dashi, me yasa bata tsaya ta fahimce shi ba ita wacce iri ce da bata tsaya tayi nazari akanshi ba. "Wayyo Allah nah...! " Fad'in Suhaima hawaye na zuba a idanunta. "Allah sarki Sabeer ashe kai masoyina na gaskiya dole a yau ba gobe ba na bayyana maka zuciyata ta dad'e da kamuwa da son ka!, i luv U Sabeer with oll my heart! " Tashi tayi tsaye bayan ta ajiye mishi diary d'in ta fita daga gidan gaba d'aya ma, a k'ofar gidan ta tsaya tana kalle kalle ta inda zata hango Sabeer, amman ko mai kama dashi bata hango ba sosai tayi mamaki don bai fiye yawo sosai ba sai dai idan Yaya Aliyu zai je wani wajen ya rakashi shima ba koyaushe ba sai abokin shi Ashiru da suke d'an fita amman basa nisa kuma basa dad'ewa sosai. "To ina yaje!? " Cewar Suhaima a fili ta furta hakan tana furzar da iskar bakinta, cikin sanyin jiki ta juya zata koma cikin gida kenan ta hango Ashiru, wata ajiyar zuciya ta sauke kafin ta k'arasa kusa dashi da sauri tace "Ashiru don Allah ko kaga Sabeer? " Da murmishi a fuskar shi yace "Eh yana cikin gonar Yaya Aliyu a zaune yanzu na barshi acan na taho d'auko abu " ajiyar heart Suhaima ta sauke tare da hamdala jikin zuciyar ta kafin tace "Yawwa nagode Ashiru" Tana gama fad'in haka ta wuce da sauri zuwa cikin gonar Yaya Aliyu, yayin da Ashiru ya wuce cikin gida. Tana k'arasa gonar ta fara dube duben inda yake ta d'an jima tana dubawa kafin ta hango shi kan wani dutse mai d'an girma a zaune, kallo d'aya zaka yi mishi ka fuskanci yana cikin damuwa. Ta jima tana kallon shi hawaye na zuba a idanunta na tausayin Sabeer kasa k'arasa wa inda yake tayi kawai ta tsaya tana kallon shi, jikinshi ne ya bashi ana kallon shi yasa shi d'ago kanshi yana dubawa ya hango Suhaima a tsaye ta zuba mishi ido, d'an murmishi ya saki na yak'e kafin kuma lokaci d'aya ya zaro ido waje fuskarshi d'auke da tsantsar tashin hankali da k'arfi ya furta "Suhaima! " Bazato Suhaima taji ya kirawo sunanta fuskarta d'auke da murmushi itama ta furta "Sabeer! " Ganin batasan abin da ya hango ba ne bane yasa shi zabura ya mik'e da wani irin gudu da zafin nama ya k'arasa inda take tsaye bai yi wata wata ba ya ture ta gefe guda ta fad'i k'asa. Arud'e ta d'ago kanta ta kalle shi inda kuma a daidai lokacin Sabeer ya saki wata k'ara da k'arfin gaske ya fad'i k'asa yana wani irin abu kafin kuma jikin shi ya sandare kamar matacce ya zama, cikin hargitsi Suhaima ta mik'e tsaye ta taho inda Sabeer yake kwance, sauran taku d'aya tayi ta k'arasa wajen ta hango abun da ya matuk'ar firgitata ya tsorata ta lokaci d'aya jikinta ya hau rawa na tsoro ko kwakkwaran motsi ta kasa balle ta nemi agaji....... Uhm ga Sabeer a kwance kamar matacce ko mene ya same shi sai ku biyo ni don jin abin da ya faru, mu had'u a next page don jin yanda zata kasance, ku cigaba da hak'uri fan's. Aishat A Muh'd ✍🏻 [2/28, 9:04 PM] Aıʂɧąɬ A Mųɧ'ɖ ✍🏻: *A SANADIN SON KI* Written by Aishat A Muh'd Dedicated to my Sadeey SaNaz *PAGE 61-62* Ba wani abu Suhaima ta gani ba wanda yayi matuk'ar razana ta sai wani k'aton snake baki wuluk dashi wanda batayi tantama ba shine ya harbi Sabeer, ganin yayi kanta ne yasa ta bud'e muryar ta gaba d'aya ta zuba wata k'ara ta firgita, gaba d'aya jikinta rawa yake yi saboda tsabar firgita rufe idanunta tayi kawai ta sadakar kasheta zai yi. Kafin ya k'arasa inda take ne Aliyu da Ashiru wanda suka taho gonar suka jiyo k'arar Sabeer a rud'e suka taho da gudu suna gaf da k'arasa inda suke ne suka sake jin k'arar ihun Suhaima da gudu suka k'araso ganin abin da yake kok'arin cutar da ita ne ya sanya su nufar inda yake nan Ashiru da Yaya Aliyu suka far masa da duka sai da suka kasheshi tsab tukunna suka k'arasa wajen da Sabeer yake kwance Suhaima tana rik'e dashi tana kuka kamar ta shid'e. Hankali a tashe suka k'arasa wajen sannan Yaya Aliyu da Ashiru suka d'auki Sabeer suka nufi gida, Suhaima tana biye dasu kamar tayi hauka saboda tashin hankali. Suna k'arasa gida suka shigar dashi gida nan aka kirawo mai magani na gargajiya ya fara aikin shi har ya cire dafin a k'afar Sabeer inda macijin ya cijeshi, sannan ya sanya magani a wurin nan yace musu zai iya farkawa a koda yaushe don ya auna arzik'i saboda macijin da ya harbe shi yana da dafi sosai, sannan ya ba da maganin da zai yi amfani dashi daga k'arshe kuma yace idan ya farka a kirawo shi sannan yayi musu sallama ya tafi. Aliyu da Aunty Aliyah hankalin su ba k'aramin tashi yayi ba kada d'an mutane ya mutu ta sanadin su haka kuma ta 6angaren Suhaima kuka sosai take tana zaune kusa da Sabeer idanun nan tamkar wad'anda zasu zazzago saboda kuka duk ta d'auki laifin ta d'ora wa kanta me yasa Sabeer bai bari ya harbe ta ba ya tureta, da dare wajen 11pm dakyar Yaya Aliyu da Aunty Aliyah suka lalla6a Suhaima ta tafi d'akin ta sai dai sam babu bacci a idanunta balle kuma maganar abinci. Wanda
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104