Chapter 31
Chapter 31
gyara tsab tamkar ba yanzu ya gama hargitsa d'akin ba, kwanciya yayi kan bed yana tunanin ta inda zai fara shawo kan Suhaima don yafi jin haka fiye da shawo kan iyayen shi... Ya kuka ji page d'in nan, Sabeer kamar sabon kamu 😹 ya koma, ni Mumy da Alhj Ahmad sun fi ban dariya 😂 da suka sashi a gaba suna kuka, ina fatan zan ga Comment's, idan na samu Comment's da yawa zan k'ara muku 1 page anjima 😹 Aishat A Muh'd ✍🏻 [2/4, 11:28 AM] Aıʂɧąɬ A Mųɧ'ɖ ✍🏻: A SANADIN SON KI Written by Aishat A Muh'd ♻ EXCLUSIVE WRITER'S FORUM Dedicated to my Sadeey saNaz PAGE 44-45 Yana nan kwance kan bed idanun shi a lumshe hawaye ne har yanzu suke zuba gaba d'aya brain nashi ya d'auki zafi har ya kasa tunanin abin yi, banko k'ofar akayi da k'arfi aka shigo Hajjah Hauwaa ce ta shigo a matukar kid'ime bayan ta Alhj Ahmad, Mumy da Daddyn Sabeer ne suka k'arasa shigowa cikin bedroom d'in. Cikin kuka Hajjah Hauwaa ta k'arasa inda Sabeer yake kwance idanu a lumshe suna zubar da hawaye, fyace hancin ta tayi da hankycif d'in hannun ta kafin ta zauna saman drower na gefen bed, hannun Sabeer ta kamo cikin tashin hankali tace "Sabeer me yake damun ka?, wane ya 6ata maka rai?, ka sanar damu yanzu kaga irin mataki da zamu d'auka akan kowanne d'an mara mutunci ne, ka sanar da mu yanzu kaji d'an lele na ba wanda zai ta6a min kai ya kwana lafiya kowa ne maza ka sanar da ni...?" Shiru Sabeer yayi mata tamkar baisan da mutum kusa dashi ba, "Bana son ka Sabeer bazan iya auren ka ba" Maganar Suhaima ce take ta amsa kuwwa a kunnen shi tamkar yanzu take fad'i, hannu shi yasa ya damk'o zanin gadon da k'arfi tamkar irin mace mai nak'udar nan kafin ya furta "Suhaima ki so ni bazan iya rayuwa bake ba please idan kika baki soni ba mutuwa zan yi " Wayyo tashin hankali a wajen iyayen Sabeer da su Hajjah ba kad'an ba najin abin da Sabeer yake fad'a, hannu Hajjah Hauwaa ta d'ora saman kanta ga hawaye kace kace saman fuskar ta tana cewa "Hussein kuyi wani abin kai na shiga uku Sabeer ya haukace ko wata aljannar ce ta shafe shi " Abin da Hajjah ta fad'i ne yasa Sabeer bud'e jajayen idanun shi ya watsa mata wani kallo, ai tuni Hajjah tayi wani tsalle ta koma bayan Alhj Ahmad tana rawar jiki tare da zare idanu tana lek'en Sabeer ta d'auka fisgota zai yi ya shak'eta don da gani kasan baya cikin hayyacin shi. Ganin haka ya sanya Daddy kallon iyayen shi da Mumy wadda take shar6ar kuka yace "Abba ku d'an bani wuri zanyi magana dashi " Jikin a sanyaye suka fita daga bedroom d'in kowanne na sak'e sak'e cikin zuciyar shi. Bayan sun fita ne Daddy ya samu waje kusa da Sabeer ya zauna tare da janyo shi cikin jikin shi yana bubbuga bayan shi na rarrashi, sun d'an dad'e a haka kafin Daddy ya raba jikinshi dana Sabeer kallon shi yayi sannan ya janyo wata bottle d'in faro ya bud'e ya sanya wa Sabeer a bakin shi, ba musu Sabeer ya fara sha kafin ya d'auke bakin shi alamar ya isheshi ajiye bottle d'in yayi, ta6a jikin Sabeer yayi yaji har jikinshi ya d'auki d'umi alamar zazza6i yana son rufe shi. Cikin nutsuwa Daddy ya kalle shi kafin yace "me yake damun ka Son ka fad'a min damuwar ka ko da abin da zan iya taimaka maka? " Sai da Sabeer yayi shiru na tsayin lokaci kamar bazai yi magana ba kafin kuma ya bud'e baki yace "Daddy ko na fad'a maka matsala ta babu abin da zaka iya akai saboda ba irin ra'ayin ku ba ne" D'an shiru Daddy yayi cikin mamakin abin da Sabeer ya fad'a, kawar da mamakin yayi ta hanyar yin murmishi na kwantar da hankali kafin yace "Ka sanar da ni Son idan abin da ka fad'a min abin da zai yiwu ne why not mu baka had'in kai " Kai tsaye Sabeer yace "Daddy aure nake son yi kuma Suhaima nake so Daddy " Abin ya bawa Daddy dariya sai kawai ya murmusa sannan yace "Toh Sabeer ban da abin ka mene na damuwa kuma?, wace ce Suhaima?, me akai akayi ta fad'a min sunan Baban ta a fad'in Nigeria a gobe za'a d'aura aure " Kallon Daddy kawai Sabeer yake cikin zuciyar shi yana cewa lallai Daddy bakasan wace Suhaima ba ita ba 'yar kowa bace amman ta fita daban da sauran mata sannan kud'in bazai iya siyan ra'ayin ta ba....... Katse mishi tunani Daddy yayi ta hanyar rik'o hannun shi yace "Son wace Suhaima tell me? " Cikin muryar damuwa Sabeer yace "Daddy bata sona bazata iya aure na tace min" "K'arya take yi Son dole ta soka kuma ta aure ka, fad'a min ita wace zata kalli idon d'ana tace batason shi, fad'a min wane Ubanta? " Daddy ya k'arasa fad'in haka rai a 6ace. "Daddy Suhaima ba kowa bace haka iyayenta bakowa bane infact ita a k'auye take renon k'auye ce" "What! Son me kace, kasan abin da kake fad'a? " Daddy ya fad'i hakan yana tashi tsaye, tashi Sabeer shima yayi tsaye babu alamar tsoro ko fargaba yace "Yes! Daddy nasan abin da na fad'a kuma ina cikin hayyaci na " "Bazai yiwu ba Son ka sake nemo wata amman sam wannan yarinyar bata dace da kai ba 'yar talaka ce kuma 'yar k'auye bata da ilimi ko kad'an bazan iya had'a zuri'a da ita, kai kad'ai Allah ya bani bazan iya zuba ido naga kayan takaicin nan ba don haka ka sake tunani! " Cikin tsantsar 6acin rai da abin da Daddy ya fad'a yasa Sabeer naushin dressing mirror da k'afar shi da k'arfi wanda sai da tayi k'ara tsabar had'uwar kafar shi da katakon dressing mirror wata k'ara mai razanar wa Sabeer ya saki da sauri Daddy ya juyo a razane da sauri ya k'arasa wajen Sabeer zai rik'e shi "Don't touch me! " Ya fad'a cikin wata irin voice, hankalin Daddy ya tashi sosai cikin rarrashi yace "Saboda na hanaka auren yarinyar nan zaka nakasta kanka Sabeer? " Idanun shi na tsiyayar hawayen kallon shi yake cikin ido kafin yace "Idan baku barni na aureta ba zan iya mutuwa ma Daddy!" A matak'ar razane Daddy yake kallon d'an nashi cikin wani irin yanayi na tsantsar tashin hankali. Sabeer bai k'ara kallon inda Daddy yake ba ya fara tafiya cikin d'ingisa d'ayan k'afar nashi wanda ya dakidaki dressing mirror da ita, yana runtse ido saboda azaba da haka ya shiga bathroom yana shiga ya kunna shower ya rasa yanda zaiyi sai kawai ya fashe da wani irin kuka yana bubbuga jikin bango da hannun shi ga ruwa yana zuba a kanshi da jikin shi. Ya d'auki lokaci mai tsayi kafin ya fito k'afar shi ta isheshi da zugi da azaba ji yake tamkar ya cireta dakyar ya iya sanya kayan shi ya kwanta saman sofa fuskar nan tayi ja da ita saboda tsabar kuka, a haka wani wahalallen bacci yayi awon gaba dashi. Azabar da k'afar shi
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104