Chapter 49
Chapter 49
amince ba don yaso ba sai don baya k'aunar 6acin ran d'an lelen shi, don haka ya kirawo 'ya'yanshi ya shaida musu gobe kowa ya tashi cikin shirin tafiya don zuwa neman wa Sabeer aure nan take suka amince da hakan. Sabeer ba k'aramin farinciki yayi ba da jin sun amince da abin da yake so, da dare Daddy yake sanarwa da Mummy yanda suka tsara shi da 'yan uwan shi ko uffan Mumy bata ce ba k'arshe sai juya mishi baya tayi ranta a k'untace batason Suhaima bazata ta6a son yarinyar da ta fito daga k'auye ba kuma 'yar talakawa ta had'a zuri'a da ita dole ta sami mafita ta tarwatsa auren kafin lokaci ya k'ure mata. *** *** *** Duk wasu shirye shirye sun kammala shi na saukar bak'in su, anyi musu lafiyayyen girki sannan Yah Aliyu ya siyo musu drinks na kwali da faro, d'akin da Sabeer ya zauna nan suka tsaftace shi aka sanya mishi turaren wuta aka shimfid'a tabarmi don nan zasu sauki bak'in su. Bayan Suhaima ta k'arasa gyaran gidan taje tayi wanka ta shirya cikin wani maroon less d'inkin riga da skirt sunyi mata kyau sannan ta zuba hijab agurguje ta fice daga gidan don tana kunyar su zo su sameta, ban da wani irin nishad'i da take ji a cikin zuciyar na daban a yau d'in nan gashi tana son ganin kyakkyawar fuskar Sabeer. Tana shiga gidan Babaa Lantana da sallama a bakin ta suna had'a ido da Babaa Lantana ta sanya dariya tare da cewa "Oh amarya Suhaima ai na d'auka bazaki bar gidan ma zama zaki yi da na ji ki shiru " Akunyace tayi 'yar dariya tare da zama a gefen ta tana cewa "Haba Babaa kinsan bazan iya zama ina jin kunya ne " "Ai na d'auka ku 'yan zamani babu wannan kunyar a wajen ku ashe da akwai masu ita " "Uhmmm" Kawai Suhaima tace kafin ta d'ora da cewa "Ni daga zuwa kin isheni da surutu ko ruwa baki ban balle ki kawo min abin dad'in da Baba ya kawo miki " "Lallai gidan bakon ki ne ko yau kika ta6a zuwa ai kinsan hanyar wajen ajiye ruwan" "Tabbb d'an tsohon nan naki yana kok'ari nasan shima idan ya dawo gida ko ruwan sha bakya kawo mishi " 'Yar hararar wasa Babaa Lantana tayi wa Suhaima kafim tace "Ku yanzu mai kuka iyama a yiwa miji hidima, wata ma miji ya dawo daga aiki ko sannu da zuwa babu balle aje batun kawo mishi ruwa mai sanyi ya jik'a mak'ogaran shi, wata ma ko kallon inda yake baza tayi ba balle yasa ran ayi mishi magana duk wata kulawar miji da hidimar shi ba'a fiye sauke mishi ba sai afkin kwalliya kamar ta aljanu da kyalakyalen da basu zu amfane su ba, wata ma ba don mijin nata zata yi kwalliya ba sai don zata fita anguwa gasu nan da yawa muna gani kuma muna jin labari, idan kika ga wata awaje ma fes da ita idan kika je gidan watak'il ko ruwan gidan baza ki iya sha ba sannan....." "Kaiii Babaa Lantana daga tsokana zaki d'auko dogon sharhi haka kamar wata ma'aikaciyar gidan redio sai zuba kike " Cewar Suhaima kenan bayan ta katse Babaa Lantana daga maganar da take. D'an hararar ta tayi kafin tace "Yo ai gaskiya nake fad'a da kin barni na cigaba sai ki d'auki abubuwa masu amfani ke da zaki tafi birni ga mijin ki kyakkyawa kamar balarabe don nasan baza ya rasa mata masu rububin son shi ba, don yanzu mun zo wani irin zamani da sam wasu matan basu da alkunya sai kaga mace har mace amman ta zubar da k'imar ta tana furta wa namiji so babu kunya wannan abin yana ban takaici " "Allah ya kyauta " Abin da Suhaima tace kenan tana jin wani abu yana mata tuk'uk'i cikin zuciyar ta da taji Babaa Lantana tace yanzu haka da akwai wasu matan da suke son Sabeer wad'anda suka fita kyau, wayewa da ilimi na boko tunda ita iyakar ta secondary kawai. "Yanzu me kika shirya mishi wanda zai ci idan yazo? " D'an yatsina fuska Suhaima tayi tare da cewa "Tabbb ni ban wani shirya mishi komai ba sai abubuwan da aka tanadarwa bak'in" Kama baki Babaa Lantana tayi sannan tace "Allah ya shirye ki Suhaima yanzu baki d'an yi mishi abu na musamman ba shi d'aya haka ake tar6ar saurayin" Cikin yanayin shagwa6a tace "Toh ni me zanyi mishi kawai yaci wannan na gaji tun safe nake aiki wallahi " "Ke tafi can tsaya sanyin jiki na kwace miki shi " Dariya Suhaima tayi kawai nan Babaa Lantana ta tashi ta fara kiciniyar aiki. "Babaa me zaki yi ne haka? " D'an hararar ta tayi kafin tace "Tsaya ki gani yarinya kiga yanda ake tar6ar bak'o " D'an ta6e baki Suhaima tayi tare da kwanciya tana ganin yanda Babaa Lantana take zirga zirga k'arshe ma fita tayi daga gidan, tayi mintuna goma da fita sai ga ta da kaji biyu yankakku ta cigaba da aikinta bata k'ara bi takan Suhaima ba. Phone nata ta d'auka ta bud'e data da yake tayi downloading what's app da Instagram sai fb da yake taga yanda Jiddah take charting shi yasa batasha wahala wajen iyawa ba, message's ne suka fara shigowa duk da iya Jiddah da Sabeer ne kawai take what's app dasu sai wani group na kitchen da na novels sai na make up wanda Jiddah ta sanya ta. Kan number d'in Jiddah ta shiga nan taga ta turo wani video tare a tsokanar ta amarya, bud'e videon tayi bayan ya gama bud'e wa sai ta fara kallo tun tana murmishi har ya sanya ta fara tuntsira dariya ganin irin shagwa6ar da Sabeer yake yiwa su Daddy sai kace wani d'an yayen yaro k'arami dariya tayi sosai har da hawaye, Babaa Lantana kuwa sakin baki tayi tana kallonta kafin kuma ta girgiza kanta tana cewa "Allah ya shirya " Ta wuce ta cigaba da aikinta. Bayan ta gama dariyar ta fad'a dogon tunani daman haka Sabeer yake duk da tasan daga yanayin shi zai yi shagwa6a bata zaci shagwa6ar zata yi haka wani murmishi kawai take saki wanda ita kadai tasan ma'anar shi. Wajen misalin karfe 2 na rana su Daddy suka k'araso tare da jagorantar Sabeer don yana son ganin Babyn shi, suna k'araso wa sun samu kyakkyawar tar6a daga wajen Yaya Aliyu, Baba Adamu da kuma wasu amintattun dattijai biyu abokanan Baba Adamu kuma mak'obtan su, su Daddy sunyi mamakin ganin irin wajen da Sabeer yaje neman aure duk da haka kuma k'auyen ya basu sha'awa gashi sun ji dad'in tar6ar karamcin da aka yi musu. Bayan sun yi sallahr azahar ne don a hanya ta riske su, sai aka yi zaman gaisawa kafin kuma a fara cin abinci, a d'an kyamace suka fara kai abincin bakin su amman da suka ji irin dad'in d'and'anon shi tuni suka zage suka fara ci. Ganin sun fara cin abincin ce yasa Sabeer zamewa zuwa cikin gidan suka gaisa da Aunty Aliyah sannan ta fad'a mishi a inda Suhaima take wani murmishi ya saki kafin ya fita kuma. "Wannan 'yar tsohuwar me kike girkawa ne duk kin cika
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104