Chapter 57
Chapter 57
wannan maganganun babu dad'i " Cewar Jiddah tana turo baki wata uwar harara Aunty Fadilah ta aikawa Jiddah kafin tace "Daman ina zaki ga rashin dacewar hakan bayan an shanye mana ke da Sabeer har da Yaya Hussein, idan ban da k'addara ina mu ina neman aure a irin wannan wurin " Ta k'arasa maganar tana jan tsaki, cikin rashin kunya Jiddah tace "Allah Aunty kika sake magana sai na gayawa Daddy tun da har kin mance abin da Daddy ya fad'a kafin mu taho " Wata hararar ta sake zabga mata tamkar idanunta ya fad'o amman bata sake magana ba don tasan sarai halin Jiddah tsaf zata fad'awa Daddy kuma tasan tsaf zai ci mutuncin ta. Sai bayan la'asar da suka yi sallah suka taho da tarin kayan snacks da drink's d'in da Jiddah ta bayar akayi, sai kuma cikin kud'in da suka kawo aka basu tukwicin dubu d'ari biyar, a wulak'anci suka kar6a kud'in babu sallamar arzik'i suka tafi. Sai bayan tafiyar su ne aka saki jiki ana kallon lefen akwatina har 15 kowacce cike da kaya damk'an dakyar bag's ake zuge zipe saboda cikar kayan. Duk kwakwkwafar mutum dai ya hak'ura da ganin kayan, k'arshe bayan an gama gani Aunty Aliya suka tattara su aka zuba su cikin d'akin Suhaima, daman Suhaima bata gidan tana can gidan Babaa Lantana ita da wasu kawayen ta biyu wad'anda suke shiri dasu. Sai dare Suhaima ta dawo gida kasa kallon kayan tayi sabida kunya sai da Aunty Aliya ta dunga fito mata dasu tana gani a haka shima Yah Aliyu ya tarar dasu ya d'an kalla sama sama kafin yace "Masha Allah kanwar tawa tayi goshi sai dai gaskiya kayan sunyi yawa sosai wallahi" "Gaskiya kam sunyi kyau sai dai yawan su mu muke ganin haka amman su ba wani abun ne rabon ta ne" Cewar Aunty Aliya kenan tana bud'e bag d'in da aka zuba sark'ok'i, sannan ta d'ora da cewa "Yanzu ya zamu yi da motar ta? " Sai lokacin Suhaima tasan har da mota haka ma Yah Aliyu. "Tabd'ijam har mota fah kika ce Aliyah? " "Kwarai kuwa baka ganta a waje ba? " "Naga mota na d'auka ko lalace musu tayi " "A'a ta Suhaima ce " "Yanzu yanda za'a yi idan Sabeer yazo sai ya tafi da ita ya ajiye mata acan gidan nashi ko kuma Jiddah ta tafar mata da ita ta ajiye " "Haka za'a yi kuwa don shine mafita nan ba wajen zaman ta ba ne " Suhaima tana jin su duk wannan tattaunawar da suke bata ce komai ba sai tagumi da ta yi, bayan su Yah Aliyu sun fita daga d'akin har Yah Aliyu yana tsokanar ta da "ke fah yanzu Suhaima kin zama matar manya koh? " Murmishi kawai tayi ta turo mishi baki dariya yayi ya fice abin shi Aunty Aliyah na taya shi. Suna fita wayar Suhaima ta d'auki k'ara ganin Sabeer ne ya sanyata d'auka had'e da yin sallama, lumshe idanun shi yayi kafin ya bud'e su yana amsa sallamar ta throughout yau bai ji wannan muryarta ta ba. "Amarya ta kinsha k'amshi nayi missing naki fah Baby yaushe zan zo? " D'an murmishi ta saki mai d'an sauti sannan tace "sai nan da 4 week's zaka zo " D'an zaro ido yayi kamar tana ganin shi yace "Washsh! Allah nah kice Baby sai dai ki zo dubiya ta asibiti don nasan sai Doctor ya kwantar dani " Dariya ta kyalkyale da ita tana cewa "Haba lallai da ka cika rago kuwa" Da sigar tsokana ta fad'a. "Baby nine ragon koh, tabbb yarinya zaki bayani ne idan na rik'e ki a hannuna a time d'in ne zaki fahimci irin jarumta ta " Gaban Suhaima ne ya d'an fad'i har ta kasa magana duk da bata fahimci maganar tashi sosai ba, jin tayi shiru ya sanya shi murmushi ya basar da zancen da cewa "Baby kaya sun yi miki kuwa? " "Laaa sunyi kyau sosai sai dai Sabeer gaskiya sunyi yawa, bayan haka har da mota fah sai kace wadda za'a siyar " Dariya ya d'an yi jin yanda ta k'arasa maganar cikin shagwa6a. "Baby nah kenan toh ai motar ba ni na baki ba Daddy nane ya baki, kuma zancen yawan kaya ki daina zancen su don kin cancanci fiye da haka " "Ina godiya sosai a mik'a min godiya ta wajen Daddy " "Toh Baby yanzu mene tsare tsaren bikin ne, mai kuke son yi, don ina son zan zo nida friend nawa Musaddiq " "Daman kana da aboki ne? " "Baby ina da aboki mana amman duk acikin su da d'aya na aminta dashi wato Musaddiq sai dai shi miskili ne na ajin k'arshe shi yasa baki san shi ba " "Ayyah amman wannan kafin ya samu macen aure zai sha wahala " "Baby ai yana da aure matar shi Mufidah da yaran shi twins sai dai yana rik'on d'iyar Yayan shi wanda ya rasu" (dafatan masu karatu baku manta labarin littafin YAYI SAKE ba), nan Sabeer ya bata d'an labarin shi a takaice sosai Suhaima ta matuk'ar tausaya musu jin irin gwagwarmayar da Musaddiq yasha a cikin rayuwar shi. "Allah ya jik'an Abubakar Sadeeq" "Amin ya rabbi Baby, yanzu kije ki kwanta dare yayi ranar friday ko Saturday zan shigo" "Okay Allah ya kawo ka lafiya " "Amin Baby nah kiyi bacci mai dad'i da sweet dreams dani aciki " D'an murmishi kawai tayi nan suka yi sallama abin su zuciyar kowannen su cikin farinciki. **** **** **** Bayan kwana 2 da kawo lefe Jiddah tazo ta d'auki Suhaima don kai d'inkin kaya, kaya da D'an yawa ta zazza6o cikin kayan lefen ta had'a da wanda zatayi amfani dasu ranar bikin sannan ta had'a da wanda Yah Aliyu da Aunty Aliya suka yi mata, wajen tailor d'in Jiddah suka kai bayan sun gama za6ar irin style's d'in da suke so aka yi total na kud'i bana wasa ba nan take Jiddah ta biya su ko ragi babu don tana son su cika mata alkawari don nan da 2 week's zata dawo ta kar6e su dukka, duk wannan kud'in d'inkin a wajen Sabeer Jiddah ta kar6o, sannan suka zarce zuwa gidan Jiddah yini Suhaima tayi acan sai yamma driven Jiddah ya dawo da ita gida, motar Suhaima kuwa tana gidan Jiddah a ajiye don tun washe gari Yah Aliyu ya fad'a mata a waya ta turo driven ta ya dauka sai ya hau taxi drop har k'ofar gidan sai ya koma da motar. Sai shirye shiryen biki ake ta koina duk da family d'in D'an fillo basa maraba da shigowar Suhaima cikin su hakan bai hanasu shirya bikin ba fiye ma dana kowanne d'a a gidan,har dinner suka shirya ta family da suke yi har da yin ankon su kamar irin gasken nan, haka ta 6angaren Suhaima ma sosai Yah Aliyu da Aunty Aliyah suka zage wajen shirya bikin nasu dai dai gwargwadon iyawar su, Jiddah sun gama tsara event's d'in da zasu yi dinner, walimah, kamu sai kuma dinner d'in family d'in Sabeer wadda zasu yi ranar da aka kawo amarya........ Ku cigaba da hak'uri da ni Fan's. Aishat A Muh'd ✍🏻 [3/29, 8:54 PM] Aıʂɧąɬ A Mųɧ'ɖ ✍🏻: *A SANADIN SON KI*
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104