Chapter 75
Chapter 75
tabar wurin d'an hararar Suhaima yayi kan yace "Baby ni fah i hate dis gurl zata bar gidan nan soon a sama miki wata" "A haba dear me ta tsare maka? " "Ni bata kwanta min ba a rai " Murmishi tayi kawi ta fara shan kunun sam Sabeer kasa cin abincin yayi yana kallon ta don sai yaji zuciyar shi na ayyana mishi kunun nan bai yarda dashi ba, amman ganin bashi da wata hujja ne ya sanya shi kawai barinta tana sha. Bayan ta gama shane ta fara bashi abinci abakin shi ganin yak'i cin nashi, bayan ta gama bashi suka dawo parlour zama Sabeer yayi ita kuma Suhaima ta mik'e tsaye kallon ta yayi kafin yace "Baby ina zaki? " "Fitsari nake ji Dear bari naji na dawo " Shiga bedroom d'in ta tayi ya bita da kallo kawai, Suhaima na shiga bathroom ta tsugunna zata yi fitsari sai kawai ganin jini tayi yana zuba maimakon fitsari, a razane ta mik'e tsaye jikinta na 6ari lokaci d'aya taji marar ta tana k'ullewa kasa d'aga k'afar ta tayi sai kawai ta zube akasan tiles d'in bathroom ta kwallawa Sabeer wani irin kira da k'arfi. Sabeer da yake zaune yana kallon film d'in furious 7 a mbc 2 yaji kiran da Suhaima take mishi da sauri ya tashi ya nufi d'akin nata kai tsaye bathroom ya bud'e ganin bata cikin d'akin, idanun shi ne suka sauka akan tiles d'in toilet d'in wanda ya kasance fari jini gaba d'aya ya rina wajen, ga Babyn shi durkushe tana murk'usus tare da kiran sunan shi. Saboda tsabar tashin hankali sau ran kad'an Sabeer ya zube a k'asa jikin shi na rawa ya d'auke ta kawai ya fito daga d'akin da gudu ya nufi hanyar fita daga parlourn. Larai tana ganin haka da sauri ta shige bedroom d'in Suhaima ta sanya wasu abubuwa cikin drower ta fito. Gudu kawai Sabeer yake shararawa akan hanya har ya k'arasa hospital d'in Mumy, a rikice yayi parking tare da bud'e bayan motar ya d'auko Suhaima yayi cikin asibitin da ita. Da Mumy ya fara cin karo fitowar ta daga room d'in operation tana zame hand gloves d'in hannun ta, ganin d'an nata ne tare da Suhaima ya sanya ta kiran nurses suka kar6i Suhaima zuwa wani room na daban, yayin da Sabeer ya zube a k'asa yana kuka sosai, dafa kafad'ar shi tayi jiyowa yayi ya rungume ta had'e da fad'in "Mumy ina rok'an ki kada ki bari na sake rasa cikin nan please Mumy ki taimaka min " Tausayin d'an nata ne ya kamata amman tasan dab take da rabuwa su bazata bari tausayin shi yayi rinjaye cikin zuciyar ta ba. Da kanta ta jagoranci su Dr Aishat da Dr Nabilah zuwa room d'in da aka kwantar da Suhaima don tana son su zame mata shaidu, sunyi nasarar tsayar da jinin sai dai kuma tun kafin suzo asibitin cikin ya zube allurar bacci akayi mata tare da sanya drip suka fito domin neman jinin da zasu sanya mata. "Mumy ina fatan ban dad'a rasa shi a karo na biyu ba? " "Yalla6ai yanzu jini muke buk'ata da za'a sanya mata " Cewar Dr Aishat kenan, dole Sabeer ya hakura da tambayar yaje aka d'auki jinin shi duk yanda Mumy taso ta hanashi yak'i yarda ya biye mata. Bayan awanni biyar a lokacin Suhaima ta farfad'o in banda kuka babu abin da take yi haka ma Sabeer wanda yayi kuka ya more yana zaune agefen Suhaima ya kasa rarrashin nata. Shigowa room d'in akayi Daddy ne da Mumy suka shigo sai Jiddah, ko zama basu yi ba suka fita daga d'akin gaba d'aya har Sabeer da Suhaima tare dasu Dr Aishat mota suka shiga sai gida. Zama suka yi a parlour duk sunyi shiru kafin Daddy yace "Muna son sanin mene ne musabbabin zubewar cikin Suhaima tun da kune kuka dubata". "Yalla6ai mun gano inda matsalar take tablet d'in zubar da ciki akesha shine dalilin zubewar cikin " Ba Suhaima da Sabeer ba hatta Daddy sai da ya d'ago a matuk'ar razane yana kallon Dr Aishat, "Tabbas kuwa anyi hakan ko zubewar cikin farko ma shan maganin akayi Dr Faridah ce tace kada na fad'a a bari sai ta sake zubar da wani " "Okay mun gode kuna iya tafiya " Cewar Daddy kenan, tashi suka yi suka tafi, yayin da Suhaima, Sabeer, Jiddah da Daddy sun kasa cewa komai musamman Sabeer da Suhaima da suka ji abun wani iri. Cikin kuka Mumy tace "Innallilahi wa'inna ilaihi raji'un daman nasan za'a rina talaka bai iya samu wuri ba sai yayi rashin mutunci, daman bason Sabeer d'in take ba tun da har bazata iya had'a zuri'a dashi ba take zubar mishi da ciki " Girgiza kai tayi tana tafa hannu tace "Aikuwa tun da haka ne wallahi sai Sabeer ya rabu dake rabuwa ta har abada, yanda Allah shi kadai ya bani inason ganin ya tara min jikoki shine don bakinciki da munafarci irin naki kike zubar da cikin har sau biyu to wallahi baki isa...... " Bata gama maganar ba Daddy ya d'aga mata hannu dole tayi shiru cikin nutsuwa Daddy yace "Suhaima ki fad'a mana gaskiya shin wannan abin da ya faru da had'in hannun ki aciki?" Cikin wani irin kuka na tashin hankali tace "Wallahi Allah Daddy bansan komai akai ba ban ta6a shan wani magani ba na rantse da Allah " "Daddy Allah Suhaima bazata sha magani ba don ta zubar da ciki tana son Sabeer bazata iya aikata haka ba sai dai idan sharri akayi mata wallahi a fad'i wanda yake bata abu taci a lokacin sai cikin ya zube anan za'a gano munafikin da ya...... " Kafin Jiddah ta k'arasa maganar ta Dr Faridah ta kwad'a mata mari tare da cewa "Daman Jiddah baki da hankali yanzu sai ki bi bayan wata bare bayan kina ganin d'an uwanki take cuta tana zaluntar shi amman kin ban kunya wallahi" Basu ankara ba sai ganin Sabeer suka yi da sauri ya tashi a sukunye ya nufi bedroom d'in Suhaima ya fara hargitsa d'akin don yasan indai gaskiyar magana ne Suhaima na zubar mishi da ciki zai samu wani k'arin haske akai. Birkita d'akin yake komai sai da ya hargitsa cikin wardrobe duk ya zubo mata kayanta k'asa har katifa ya d'aga cikin toilet drawer d'in gefen gado duk ya duba bai ga komai ba a lokacin zuciyar shi ta fara aminta da maganar da Jiddah tayi sharri akayiwa Suhaima daman shi bai gama yarda ba. Har zai fito daga d'akin idanun shi suka sauka kan drower d'in jikin mirror da sauri ya k'arasa wajen yana bud'e su har ya janyo ta k'asan, lokaci d'aya jikin shi yayi wani irin sanyi ga66an jikin shi suka saki wata irin tsanar Suhaima ta fara mamaye cikin zuciyar shi ganin abin da idanun shi suka gane mishi. Kwaso kwalin maganin yayi gaba d'aya ya fito daga d'akin a fusace kamar wani zaki yana zuwa ya watsawa Suhaima maganin akanta cikin kzakkausar murya yace "Suhaima! Wannan mene? " Suhaima wadda sauran k'iris fitsari ya zubo ta ta zubawa maganin ido duk da batayi karatun likita ba jikinta ya bata wannan maganin shine wanda ake magana akan shi. "Alhamdullilah
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104