Chapter 80
Chapter 80
sanya ni ba laifi na bane " "Wacce Hajia? " Cewar Daddy cikin zak'uwa. "Hajiya Faridah ce wallahi take sanya ni zubawa Suhaima maganai a abu tasha sai cikin ya zube " "What!? " Cewar Daddy da Sabeer a lokaci d'aya suka furta hakan cikin matuk'ar razana tare da firgita da jin abin da tace, sulalewa Sabeer yayi a k'asa tare da d'ora hannun akai shikenan Mumy ta cuce shi ta gama dashi wayyo Allah nah Suhaima daman ba laifin ki bane yanzu ta ina zan iya dawo da Suhaima a rayuwa ta. Wata zabura da yayi sai da ya firgita Daddy cikin tsananin fusata ya nufi cikin palo yana kwallawa Mumy kira, yayin da Daddy ya tura Larai cikin d'aki ya sanya key ya 6ame k'ofar don baza'a barta ta gudu a banza ba sai ta fuskanci hukunci dai dai da abin da ta aikata, kafin ya bu bayan Sabeer don yau za'a yi tashin hankali.............. Aıʂɧąɬ A Mųɧ'ɖ ✍🏻 [4/14, 9:08 PM] Aıʂɧąɬ A Mųɧ'ɖ ✍🏻: *A̺͆ S̺͆A̺͆N̺͆A̺͆D̺͆I̺͆N̺͆ S̺͆O̺͆N̺͆ K̺͆I̺͆* Wྂrྂiྂtྂtྂeྂnྂ bྂyྂ Aྂıʂɧąɬ Aྂ Mྂųɧ'ɖ ɖɛɖı¢ąɬɛɖ ɬơ ɱყ ʂąɖɛɛყ ʂąŋąʑ ♻ *єχ¢ℓυѕινє ωяιтєя'ѕ fσяυм* *PAGE 99-100* Mumy har ta fara gyangyad'in bacci acikin bedroom d'in ta bacci ne take son yi ko hospital bata lek'a ba sai da yamma, kamar cikin mafarki taji Sabeer na kwalla mata kira a firgice ta fito saboda tasan wannan kiran bana lafiya bane. Cikin sauri take taka steps na bene saboda har yanzu Sabeer bai bar kiranta ba, cikin sauri ta k'arasa wajen shi inda yake tsaye tsakiyar parlour yana faman kiranta ga hawaye da suke zuba a eyes nashi. "Son lafiya irin wannan kira haka? " Kallon ta yayi hawaye na kwaranya a idon shi yace "Mumy ashe bakya son bakya kaunata ko kad'an Mumy kin cuce ni kin cuce ni! " Gaban Mumy ne yayi wani irin fad'uwa sosai da sauri ta dafe kirjin ta da hannu tare da zaro ido irin na shiga rud'u tace "Son me kake nufi, me nayi maka har na cuce ka anya kanka d'aya ko wani abun kasha ne, ina matsayin mahaifiyar ka zan cuce ka ne ? " Idanun shi jawur yace " Mumy sam baki cika uwa mai bawa d'anta farinciki a rayuwa ba, kin rabani da 'ya'yana har biyu tun kafin su zama mutum kika zubar min dasu bayan haka kin rabani da mata ta Suhaima anya Mumy zan iya yafe miki kuwa? " Sauran kad'an Mumy ta kife a k'asa tsabar firgita da kalaman Sabeer, amman sai ta wayance da cewa "Haba Son wanne munafiki ne ya shirya maka wannan zancen kamar a mafarki, kada ka yarda da wannan shirmen zancen" Kallonta Sabeer yake ba don mahaifiyar shi bace da idan ya shak'eta sai ta kusan daina numfashi, kasa magana ma yayi saboda takaici da bak'inciki sai wani irin kallo da yake mata mai tattare da nuna kin cuce ni, wannan kallon da Sabeer yake yiwa Mumy shi yafi komai d'aga mata hankali. "Kada ki nemi ki raina mana hankali Faridah daman nasan duk wannan abun da ya faru da sanya hannun ki aciki" Cewar Daddy a fusace wanda k'arasowar shi palourn kenan. Kukan kissa da munafurci Mumy ta saki tare da cewa "Na shiga uku Daddyn Sabeer ni kuke cewa na aikata hakan ta ina, na ta6a zuwa gidan Sabeer ko kuma na ta6a bata wani abun da hannuna taci cikin ya zube? " Sam Mumy ta d'auka Larai tabar gidan kamar yanda ta umarce ta. Cikin fusata Daddy yace "Ta dalilin 'yar aikin ki Larai mukasan komai, wadda kika turata gidan Sabeer don tana taimaka wa matar shi ayyukan gida ina fatan ba sai na k'arasa miki maganar ba kinsan komai tunda ke kika shirya hakan" Da sauri Mumy ta dafa bango don ganin yanda take kok'arin fad'uwa kallon Sabeer da Daddy take tamkar wasu sababbin hallita agabanta yanda suka rikid'e mata kamar wasu zakuna, can kuma ta aro jarumta ita ma afusace tace "Nayi nayi d'in! Duk abin da kuka fad'a na aikata su saboda bana son yarinyar da Sabeer i hate her bazan iya had'a zuri'a da shegiyar matsiyaciyar yariny..... " "Stop it Mumy! Kada ki k'ara aibata min mata ta, nagodewa Allah da ban sake ta ba!" Sabeer ya fad'a cikin hargowa, kallon shi Mumy kawai take cikin mamaki yau Sabeer ne yake mata tsawa. "Son ni kake yiwa tsawa akan waccan 'yar iskar yarinyar " Kuka ya fashe dashi kan yace "Daddy! Daddy ka fad'awa Mumy ta daina danganta Suhaima da wad'annan kalaman" Hugging nashi Daddy yayi yana bubbuga bayan shi yayin da yake jifan Mumy da wani irin kallo, saboda tsantsar rashin gaskiya Dr Faridah sai wani had'a uban gumi take kamar wadda ta had'iyi kunama abin da bata ta6a zaton zai faru da ita ba ya faru a lokacin da batayi tsammani ba ganin Sabeer d'anta kwaya d'aya tal da masoyin ta kuma mijinta suna kok'arin kubce mata a lokaci d'aya. "Ni fah Daddy duk abin da zaku yi kuyi min amman gaskiya bazan iya kar6ar yarinyar nan ba matsayin suruka ta " Cikin dakewa tayi maganar nan, da gudu Sabeer ya haye upstairs yana kuka zuciyar shi tana wani bugawa da k'arfi, cikin tsantsar 6acin rai Daddy yace "Faridah da bak'incikin ki ya kashe min yaro gwara na rabu da ke! " "What Daddyn Sabeer! Kana nufin akan waccan 'yar kauyen zaka sake ni? " "Ofcourse Dr Faridah bazan zuba ido ki kashe min d'a ba wanda ya kasance shi kadai ne d'ana a duniya" Matse hannun ta yayi da k'arfi tare da murd'asu har sai da tayi k'ara kafin yace "Kina tantama ne bazan iya ba yanzu zakisan baki da wayo yarinya " Wani irin lugude kirjin Mumy yake kamar zuciyar ta zata faso kirjinta ta fito, ganin tana daf da rasa mijinta amman duk da haka tana nan kan bakanta tasan Daddy bazai iya rabuwa da ita ba koda ya sake ta sai ya dawo da ita, tunanin ta ne ya katse a lokacin da Daddy yace "Faridah ki tafi gidan ku na sa....... " Kafin ya k'arasa fad'a yaji anyi sauri an toshe mishi baki, d'ago kanshi da zai yi suka had'a ido da Dr AhmadAhmad d'an fillo ranshi a 6ace yace "Haba Hussein kamar baka da hankali taya zaka biyewa zuciyar ka ta aikata abin da zaka zo kana dana sani, ko da wasa kada ka k'ara yunkurin cewa zaka saki Faridah don duk cikin surukaina nafi kaunarta sakinta da zaka yi shine datse duk wani alak'a tsakanin mu da kai " Sakin baki Daddy yayi yana kallon mahaifin nashi cikin mamaki kafin yace "Abbah! Yanzu baka ga laifin Faridah anan ba?" Cikin irin I don't care d'in na yace "Yo wane baya yin kuskure Hussein tun da abun ya wuce ba shikenan ba a kiyayi gaba kawai " Haushi ne ya turnik'e Daddy kallon Faridah yayi kafin yace "Abbah! Duk da ka hanani sakinta amman ta tafi gidan su bazata dawo gidan nan sai Sabeer ya dawo da Suhaima matsayin matar shi " Yana gama fad'in haka ya wuce fuuuu a fusace zuwa wajen Sabeer don ya rarrashe d'an nashi, yayin da Dr Ahmad d'an fillo da Dr Faridah suka bishi da kallo kafin lokaci d'aya
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104