Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 70

Chapter 70

A Sanadin Sonki Book 1 Complete Hausa Novel – A Story of Love, Sacrifice and Destiny 1,206 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

_To fah reader's kunji tunanin Dr Faridah ko zata yi nasara akan Suhaima ta rabata da Sabeer, ina jiran comments naku yanzu labari zai fara, ƙų ¢ıɠąცą ɖą ცıŋą ɖơŋ ʝıŋ ყąŋɖą ʑąɬą ƙąʂąŋ¢ɛ_. Aıʂɧąɬ A Mųɧ'ɖ ✍🏻 [4/9, 6:30 PM] Aıʂɧąɬ A Mųɧ'ɖ ✍🏻: *A̺͆ S̺͆A̺͆N̺͆A̺͆D̺͆I̺͆N̺͆ S̺͆O̺͆N̺͆ K̺͆I̺͆* Wྂrྂiྂtྂtྂeྂnྂ bྂyྂ Aྂıʂɧąɬ Aྂ Mྂųɧ'ɖ ɖɛɖı¢ąɬɛɖ ɬơ ɱყ ʂąɖɛɛყ ʂąŋąʑ *PAGE 85-86* Da kallon mamaki Sabeer da Suhaima suka bita dashi kawai kafin kuma Sabeer ya rik'o hannunta yace "Sorry Baby nah akan abin da Mumy take miki bana jin dad'in haka ko kad'an " Cikin rarrashi ya k'arasa maganar gashi fuskar shi d'auke da damuwa, d'an murmishin yak'e Suhaima ta saki sannan tace "Kada ka damu don Allah komai mai wuce wa ne, mu tafi ka ga Baby kada ka makara a office ". "Thank U Baby nah da yanda kike da fahimta i luv U " Suhaima na shirin bashi amsa kenan Jiddah ta lek'o da kanta tana cewa "Don Allah Yah Sabeer mene haka tun d'azu kuna tsaye anan ka hanata shigowa " Hannun shi ya sanya tare da janyo kunnen ta d'aya yace "Jiddah kin raina ni da yawa zan miki duka na tsayar da ita d'in mata ta ce ai " D'an ihu ta saki na jin zafi kafin ta marairaice fuska tace "Sorry Yah Sabeer na tuba na daina " Yanda tayi d'in dole yasan ya shi murmishi ya cika mata kunnen, kamo hannun Suhaima tayi suka wuce cikin gidan. Masha Allah abin da Sabeer ya fad'a lokacin da ya kar6i Babyn fara ce tas har wani ja ja take yi kyakkyawa da ita ta d'ebo kamannin D'an fillo family, wani son yarinyar ne ya shiga zuciyar Sabeer har yana imagine gashi Suhaima ta haifa mishi Baby yana d'auke da shi. Kallon Suhaima yayi wadda take zaune kusa dashi tana lek'en Babyn don itama kanta tayi mata kyau ba kad'an ba. "Baby kema kina so koh, ki haifa mana mu ma please " D'an murmishi tayi kafin tace "Toh my dear kayi addu'a Allah ya bamu masu albarka " "Amin Baby " Jiddah ya mik'awa Babyn don ya makara ma sosai, tashi Suhaima tayi ta rakashi har bakin mota suka yi sallama ta dawo cikin gidan, bayan ta gama ganin Babyn ne sai ta gyarawa Jiddah bedroom nata sannan ta wuce kitchen don shirya abincin rana. Tana tsaka da girkin 'yan uwan Jiddah suka fara zuwa gidan kasa fita tayi su gaisa tayi don gabanta sai fad'uwa yake, dakyar ta k'arasa girkin ta zuba a foodflaks sai kawai taja kujera a kitchen ta zauna tare da had'a kai da gwiwa tana tunani. Awannan yanayin Jiddah tazo ta same ta tausayin Suhaima ne ya kamata, dafa kafad'ar ta tayi a tsorace Suhaima ta d'ago kanta ganin Jiddah ce ya sanyata sakin ajiyar zuciya. "Suhaima ki rage tsoron su fah wallahi, taya zaki zauna a kitchen bazaki fito ba saboda su? " "Uhmmm Jiddah wallahi bana son kallon wulak'anci da k'ask'ancin da suke min, ina jin tsoron fita mu gaisa dasu kada su gwasale ni kamar yanda suke yi min " "Kada ki damu Suhaima komai zai wuce amman baza ki tak'ura kanki ba saboda su don haka ki fito daga kitchen " Babu yanda zatayi haka ta fito hannunta rik'e dana Jiddah, wani kallo na wulak'anci suka bita dashi kamar yanda Suhaima ta tsani ayi mata, babu wanda ya amsa gaisuwar ta sai ta6e baki da suke Jiddah ma sai da ta samu alakoran harara a wajen su. Bedroom d'in ta Jiddah ta kaita ta zauna amman duk da haka a tak'ure take har so take lokacin tashin Sabeer daga office yayi yazo su wuce gida, duk da ya kirawo ta awaya amman ba'a kwanciyar hankali ta amsa ba mishi ba, har tunanin ranar suna take batasan irin wulak'ancin da zasu yi mata cikin mutane ba. Atak'ure take har zuwa bayan mangarib sannan Sabeer yazo suka tafi gida, kallo d'aya yayi mata ya fuskanci tana cikin damuwa girgiza kanshi yayi yana yana sauke numfashi dole ya takawa 'yan uwan shi birki akan abin da suke yiwa Babyn shi bazai jure ba ko kad'an ganin ta cikin damuwa. Duk damuwar da take tattare da ita sai da Sabeer ya cire mata ita ya mayar da gurbin farinciki a wannan daren sosai Suhaima ta k'ara jin wani son mijinta cikin zuciyar ta yanda yake faranta mata rai itama tana addu'ar Allah ya sanya ta haihu don cika mishi burin shi. Ranar suna tun safe Sabeer ya kaita don yak'i barin ta ta kwana ko komawa bata sake yi ba sabida yana gudun kada a sake 6ata mata rai duk da kuwa nacin da tayi mishi, sosai Sabeer da Suhaima suka kashe kud'i wajen had'a wa Babyn kaya da kuma ita kanta Jiddah don duk abin da suka yi mata baza su biyata abin da tayi musu ba ita kadai ce mai kaunar ganin su tare sai Daddy adukkan familyn Sabeer. Sosai Jiddah taji dad'i abubuwan da suka kai mata tayi musu godiya tare da addu'ar Allah ya basu suma yaran masu albarka, Sabeer yaji dad'in addu'ar da tayi musu sosai duk cikin 'yan uwanshi yafison Jiddah fiye da kowa don itace mai kaunar abin da yake so. Baby taci sunan Babar Khaleel wato Khadijah suna ce mata Islam, ansha suna sosai don har walima da yamma sai da aka shirya an kashe kud'i sosai, amman duk wannan abun Suhaima bata shigaba tana zaune waje d'aya kanta ma yake masifar ciwo sosai, gashi tasha kukan habaici da wulak'ancin da su kayi mata. Sai bayan mangarib 'yan uwa suka fara tafiya, zaune Suhaima take kan abin sallah idar da sallahr ishsha da tayi kenan tana addu'a cikin zuciyar ta tana mai tunanin inda Sabeer ya tsaya baizo sun tafi ba don kanta sosa yake ciwo kamar ya cire ga idanun ta da suka kumbura saboda kuka, ta kirawo phones nashi basa shiga dukka, gashi hadari ya had'u sosai sai walk'iya ake. "Munafuka har yanzu zaman me kike da baki tafi ba, mun gaji da ganin fah ya kamata kisan nayi " Cewar Aunty Fadilah 'yar autar su Daddy kenan tana wani hararar Suhaima, sunkuyar da kanta Suhaima kawai tayi idanun ta suna zubar da hawaye. "Wallahi na tsani yarinyar nan kyau kamar aljanna duk tabi ta asirce mana Sabeer sai yanda tayi dashi daman 'yan kauyen nan da shegen yin asiri" Dariya aka kwashe da ita irin mai k'ulawar nan suna cewa "Sai Auntyn mu fad'a mata dai munsan asiri tayi ta mallake mana d'an uwa don Yah Sabeer bazai ta6a son wannan talakar ba yana cikin hayyacin shi" Cewar Zahra kenan, bak'inciki da takaici ya ishe Jiddah cikin d'aga murya tace "Ke Zahra wallahi ki kiyayi kanki Allah zan fad'awa Yah Sabeer yaci uban ki matar shi kike fad'awa haka " Make mata bakinta Aunty Fadilah tayi tana cewa "Ta fad'a d'in ya kashe ta idan ya isa " Kuka Jiddah ta sanya saboda make mata bakin da tayi don da ba k'aramin zafi taji ba, yayi da Zahra take danna mata harara. "Ni na rasa abin da zamu yiwa wannan mayyar yarinyar ta rabu da Sabeer ba irin wulak'anci da bamu yi mata ba amman ta lik'e mishi

Table of Contents

Chapters

104 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});