Chapter 1
Chapter 1
[2/4, 11:28 AM] Aıʂɧąɬ A Mųɧ'ɖ ✍🏻: 💝 *A SANADIN SON KI* 💝 *Written by* Aishat A Muh'd ✍🏻 ♻£xclusive Writers Forum *Dedicated to my Sadeey (saNaz)* *PAGE 1-2* Wata mata ce durk'ushe a filin tsakar gidan tana faman risgar kuka, har da shashshak'a kamar zata sume saboda tsabar kukan da take yi, sakamakon fad'an da mijin ta yake mata, gefe d'aya kuma yaran ta ne su biyu namiji da mace suna rungume da junan su, suna taya kan su da mahaifiyar su kukan tausayin kansu. Tsinkar muryar mahaifin nasu naji cikin tsantsar 6acin rai da rashin mutunci yake cewa " tun da abin haka ne zan tafi na bar muku garin gaba d'aya, na sha fad'a miki ni bana son haihuwa kwata kwata, ban shirya yin ta yanzu ba saboda bana son ta, ga kuma shegen bak'in talaucin da muke ciki, amman ke kamar kaza kina haihuwa babu dad'e wa ki dad'a samun wani cikin ni na gaji " Ya k'arasa fad'i yana wani sauke numfashi, sakamakon hayagagar fad'an da ya gama yi cikin d'aga murya da tsawa, hararar matar tashi yake da 'ya'yan nashi, zuciyar shi cike da mugun tsanar su, ji yake kamar ya shak'e su, su mutu ko ya huta da ganin su. Cikin shashshak'ar kuka matar tace "Kayi hak'uri maigida, ni kaina ba ni na bawa kaina haihuwar ba, Allah ne ya bani su taya zan butulce mishi wajen zubar da cikin da ba shege ba ne, ka tuna haihuwa rahma ce wasu da kud'in su nema suke basu samu ba, amman kai da Allah ya bawa kyauta kana neman butulce mishi" Ko gama rufe bakin ta bata yi ba ya d'auke ta da wani azababban mari har guda biyu bisa kyakkyawar fuskar ta, sake durk'ushe wa tayi tana rik'e da fuskar ta inda ya mare ta, hawaye ne kawai yake zuba a idanun ta. Nuna ta yayi da d'an yatsan shi, cikin masifa yace "bana buk'atar jin shawarar ki ko wa'azin ki, idan baki bi maganar da na fad'a miki na ki zubar da wannan cikin ba, to wallahi zan bar garin don ban shirya rainon 'ya'ya ba, naji ma da uban talaucin da ya dame ni" Yana gama fad'in haka ya juyo kan yaran, tsawa ya kwantsama musu ba shiri suka shige d'akin uwar ta su da gudu, jikin su na 6ari na tsoron mahaifin nasu. Tsaki yaja tare da cewa "shegun 'ya'ya da munafurcin tsiya da sun ga uwar su na kuka, su ma zasu fara kukan 'yan iska kawai " Yana k'arasa fad'in haka ya sake makawa matar tashi harara tare da jan tsaki ya kad'a rigar shi ya fice fuuuu a fusace kamar ya hantsila saboda sauri. A hankali yaran suka d'aga labulen d'akin suna lek'en ko mahaifin nasu ya tafi, saboda jin shirun da suka ji, ganin ya fita ne yasa su fito wa da sauri suka nufi inda mahaifiyar su take tsugunne tana kukan nata. Rungume ta suka yi suna rarrashin ta da tayi hak'uri ta daina kuka, daman sune masu rarrashin nata idan uban nasu ya gama yi mata rashin mutunci. Dak'yar ta iya mik'e wa tsaye suka shiga cikin d'aki, zama suka yi akan tsohuwar tabarmar su wadda ke shimfid'e a k'asa, kallon yaran nata tayi cikin matuk'ar tsantsar kaunar su tare da mugun tausayin su, ta kamo hannun su ta had'a waje d'aya tare da bud'e bakin ta tace "Aliyu ga amanar Suhaima nan ko da bayan rai na ina son ka kular min da ita, bana son tayi kukan maraicin na, ina son ku tsaya tsayin daka ku nemi ilimi saboda inganta rayuwar ku ko da bana raye, ina son mahaifin ku yayi alfahari da ku a gaba, ku kasance cikin yi wa mahaifin ku biyayya a duk abin da yace muku, ku cigaba da addu'a watarana sai labari komai zai zo ya wuce kamar ba'a yi ba." Cikin kuka Aliyu yace " Umma ki daina furta cewa zaki mutu ki bar mu, zamu rayu da ke Umma insha Allah, kuma zan rik'e k'anwa ta da kyau zan kula ta da ita Umma duk wani kyautata wa da bata farin ciki zan bawa Suhaima a cikin rayuwar ta." Ya k'arasa fad'i hawaye na zuba a idanun shi, cikin zuciyar shi tsanar mahaifin shi taf a ciki, Suhaima da bani wayo ne da ita ba sosai, kallon su kawai take tana kuka. Nan Umma ta janyo Suhaima jikin ta, rarrashin ta take har ta yi shiru sai sauke ajiyar zuciya da take, kafin kuma ta bud'e baki tace "Umma ni yunwa na ke ji." Umma kallon Aliyu take shima kallon Umman yake, cikin zuciyar su suna tunanin me zasu bawa Suhaima a yanzu taci, don basu da komai a gidan daman wani lokacin Aliyu ne yake fita yin 'yar sana'a ta k'arfi ya nemo musu abin da zasu ci, idan kuwa ta uban nasu ne kuwa gwara su mutu da yunwa akan ya basu abin da zasu ci. Gaba d'aya ba wanda yayi k'arfin halin bawa Suhaima amsa, jin haka ya sanya ta fashe da kuka don ko karya wa basu yi ba gashi yanzu azahar tana kok'arin yi, cikin rarrashi Aliyu ya janyo hannun ta yana goge mata hawayen fuskar ta yace "yi hak'uri 'yar k'anwa ta yanzu zan fita na samo miki abin da zaki ci, amman kada kiyi wa Umma kuka kin ji " Gid'a kanta tayi tana mai had'iye kukan nata, da sauri Aliyu ya fita daga d'akin, yayin da Umman ta bishi da kallon tausayi, yaron da bai fi ace yana k'ark'arshin kulawar iyayen shi ba amman shine yake kula da kanshi, mahaifiyar da k'anwar shi, saboda rashin dace da samun managarcin uba a gare su. Tun Suhaima na jiran Aliyu har bacci yayi awon gaba da ita a jikin Umma tana mai tsotsan 'yan yatsun ta a bakin ta, sai da bacci yayi k'arfi sannan Umma tayi mata shimfid'a ta kwantar da ita. Tashi tayi ta fito zuwa tsakar gidan tsintsinya ta d'auka ta laushi ta fara share filin tsakar gidan, tana yin sharar idanun ta na zubar hawayen tausayin kansu, wani 6angare na cikin zuciyar ta addu'a take yi tare da godewa Allah a halin da ta tsinci kanta a ciki, k'addarar tace ta auren wannan mugun mijin nata mara tausayi, mai butulce wa Allah da baiwar 'ya'ya biyu da ya bashi ga cikin na uku a jikin ta. Tun da Aliyu ya fita bai dawo gidan ba sai daf da mangarib, hannun shi rik'e da 'yar k'aramar leda bak'a, Suhaima na ganin shi ta mik'e da gudu ta k'arasa inda yake tare da kar6ar ledar hannun shi tana duba wa. Garin kwaki ne a ciki sai k'ullin sugar, kallon shi tayi fuskar ta d'auke da murmishi tace "Yaya mun gode Allah yasa ka samu sana'a kana samun kud'i kamar yanda Yayan k'awata yake aiki yana samun kud'i yana siyo musu abin dad'i " Cikin murmishi ya shafa kanta tare da cewa "Amin 'yar k'anwa ta ki cigaba da yiwa Yayan ki addu'a da Umman ki ." "Toh Yaya ina yi kullum idan nayi sallah, amman bazan yiwa baba ba tun da shi mugu ne yana dukan Umman mu, kuma yana zagin mu da dukan mu kullum, nima
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104