Chapter 48
Chapter 48
gani sai da ta mutsutstsuke idonta sannan tace "Sabeer! " Da mamaki da kuma rud'ewa da ganin shi ta sake ambatar sunan shi kafin wasu hawaye su fara zubowa daga idanun ta kallon shi take tamkar yau ta fara ganin shi. Shima wasu hawayen tausayin Mumyn tashi ne suka zubo mishi cikin sassarfa ya k'arasa ya tsugunna agabanta ya dire gwiwar shi a k'asa sannan ya d'ora kanshi saman cinyar ta, hannun ta take saman lallausan gashin kanshi tana shafawa ta kasa magana ma gaba d'aya. Muryar shi na rawa hawaye na zuba yace "Mumy baki yi murnar ganina ba koh, saboda ba'a son ranki na tafi ba, kina fushi da ni ne?" Girgiza kai take yi lokacin da yake magana, cikin sanyin murya tace "Bazan iya fushi da kai ba Son" "To gashi kin sanya damuwa a ranki kin rame ba" D'an murmishi tayi kafin tace "tunanin halin da d'ana yake ciki ne ya sanya ni ramewa da shiga tashin hankali,amman yanzu tun da nagan shi a gabana zan kwantar da hankali na " "Mumy kenan, nayi kewar ku ke da Daddy wai yana ina ne? " "I missed U too Son, Daddyn ka yana office bai dawo ba, yaushe ka dawo, zo kaci abinci " Duk ta rud'e da ganin tilon d'an nata sai faman tambaya take watsa mishi akan lafiyar shi don ta d'an razana da ramar shi da ta gani da duhun da D'an yi, hannun ta ya kamo yana kallon ta kafin yace "Mumy ki nutsu ni ina cikin lafiya sosai " "Okay zo kaci abinci, me zan zuba maka? " D'an shiru yayi kafin yace "ki ban duk abin da kika ci" Cikin farinciki tace "okay Son taso ka zauna " Haka ta kamo hannun shi ta zaunar dashi kusa da ita, kafin ta mik'e tsaye ta fara zuba mishi abincin, da kanta take bashi tana faman kallon shi tamkar wata sabon halitta a gabanta, ita kanta tasan tayi kewar d'an nata da yawa duk saboda matsiyar yarinyar nan d'anta yayi mata nisa. "Mumy tunanin me kike ne ba gashi na dawo ba" Da murmushi kan face nata tace "Son kawai ina tunanin irin wacce wahalar kayi a k'auyen da ko wutar nepa babu " "Haba Mum aikuwa suna da wuta sai dai ba'a fiye samu sosai ba" D'an ta6e bakin ta tayi sannan tace "kuma kana iyacin abincin su naga duk ka rame kayi bak'i " "Mum kibar wad'annan tambayoyin please " "Shikenan Son na bari " Tana gama bashi abincin suka koma parlor tana rik'e da hannun shi gane take tamkar zai sake guduwa ya barta, basu dad'e da zama ba Daddy ya dawo agajiye sosai yake, amman had'a ido da Sabeer yasa shi neman gajiyar tashi ya rasa nan suka yi hugging d'in junan su cikin tsananin k'aunar junan su. Nan babu dad'e wa Family d'in D'an fillo dashi kanshi Dr Ahmad d'an fillo da Hajjah Hauwaa suka samu labarin dawowar Sabeer, nan suka dunga shigowa ganin Sabeer kusan dukkanin su sunyi farincikin ganin shi, musammam Alhj Ahmad d'an fillo da Hajjah don rungume shi sukayi tamkar zasu mayar dashi cikin jikin su saboda tsabar son da suke mishi. Jiddah wadda agidan ta wuni ta d'ago kanta suka had'a ido da Sabeer wanda yake ta zuba musu shagwa6a su kuma sun shashance da lalla6a shi, dariya take son fashewa da ita amman ganin hararar ta da yake yi ne ya sanya ta kunshe dariyar ta, daga k'arshe sai ta faki idon shi tana mishi video don ta nunawa Suhaima ta shirya zama da shagwa6a66en miji..... Aishat A Muh'd ✍🏻 [3/14, 5:17 PM] Aıʂɧąɬ A Mųɧ'ɖ ✍🏻: *A SANADIN SON KI* Written by Aishat A Muh'd Dedicated to my Sadeey SaNaz *PAGE 69-70* Tun bayan tafiyar Sabeer gida Suhaima ta shiga tsananin kewar shi ranar cikin kewar shi take duk ta sanyawa kanta damuwa ko abincin kirki ta kasa ci sai tunanin Sabeer, sam ta mance bata kunna wayar da ya bata ba duk a tunanin ta a kunne take. Sabeer kuwa duk ya shiga tashin hankali da ya kirawo ta yaji wayar a kashe yana son sanar da ita ya sauka lafiya sannan ya fad'a mata yanda yayi kewarta na tsawon yini guda, daga k'arshe dai sai kiran Yayah Aliyu yayi bayan sun gaisa yake fad'a mishi ya sanarwa da Suhaima ta kunna phone nata zai kirata tukunna suka yi sallama. Tana kwance still har yanzu har bacci ya fara fisgarta sai taji sallamar Yah Aliyu ya shigo d'akin, kallon ta yayi cikin kulawa kafin yace "K'anwata me yake damun ki duk kinyi wani iri yau kodai duk tafiyar Sabeer d'in ne ya sanya ki zama haka" Ya k'arasa maganar cikin zolaya, da sauri Suhaima ta rufe fuskar ta da hannayen tana 'yar dariyar jin kunya tace "Kaiiii Yaya! " "Eh mana gaskiya ce ina kula da ke fah ko abincin kirki baki ci ba sannan baki zo munyi hira ba " Kasa magana tayi don batasan da me zata kare kanta ba don kuwa maganar shi haka take, ganin haka yasa shi mik'e wa tsaye yana murmishi yace "Sabeer yace ki kunna wayar ki zai kirawo ki sai da safe " Yana gama fad'in haka ya fita, d'an waro ido tayi kad'an tare da cewa "Daman wayar a kashe take oops! " Bata tsaya 6ata lokaci ba ta janyo wayar ta kunna ta sannan ta zuba mata ido tana sauraren kiran Sabeer. Ko mintuna goma cikakku batayi da kunna phone d'in ba taji ta d'auki ringing, d'auka tayi ba tare da duba screen d'in ba saboda sauri da zak'uwan son jin voice d'in Sabeer. "Hello Baby nah ". Lumshe idonta tayi saboda jin saukar daddad'ar muryar Sabeer cikin kunnen ta har ta shagala ma sai da ta sake jin muryar shi yana mata magana sannan ta sauke ajiyar zuciya ta amsa mishi tare da gaida shi. Bayan ya amsa ne suka d'an ta6a hira ta tsayin wajen mintuna 30 sannan suka yi sallama da junan su don ganin dare ya fara yi, kowannen su cikin kewar d'an uwanshi suke. Bayan dawowar Sabeer da kwanaki uku ne ya buk'aci da iyayen shi su je neman mishi auren Suhaima, nan take Daddy ya aminta da hakan don haka ya had'a kan 'yan uwan shi maza suka had'u zuwa part din mahaifin su suka sanar mishi don ya tsayar musu da ranar tafiya neman auren Suhaima. Sam Alhj Ahmad d'an fillo ba'a son ranshi yayi magana ba don kana kallon fuskar shi zaka karanci hakan, don farincikin Sabeer kawai ya aminta da auren nan amman sam baya so Suhaima, nan ya yanke lokaci zuwa nan da sati biyu su Daddy zasu je, aikuwa Sabeer najin haka ya tubure bazai yadda ba don sati biyu sunyi mishi nesa shi fah da ason ranshi ne aranar a d'aura auren Babyn shi ta tare a gidan shi, ganin yanda ya tada rigima ne ya sanya shi tambayar shi yaushe yake son aje. Bud'ar bakin Sabeer yace shi gobe yake son aje kuma a tsayar da lokacin biki nan da sati uku, don fah shi har ga Allah satin ukun ya fad'a ne kawai amman sunyi mishi nisa, yanda ya buk'ata haka Alhj Ahmad d'an fillo ya
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104