Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 6

Chapter 6

A Sanadin Sonki Book 1 Complete Hausa Novel – A Story of Love, Sacrifice and Destiny 1,188 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

💝 A SANADIN SON KI 💝 Written by Aishat A Muh'd ♻£xclusive Writer's Forum Dedicated to my Sadeey SaNaz PAGE 7-8 Babu wanda yayi k'arfin halin yi mishi magana a tsakanin Baba Adamu tare da Babaa Lantana, ganin haka ya sanya shi kutsa kai cikin d'akin, lokaci d'aya kuma gaban shi na bugawa da k'arfi sosai. Aliyu yana sanya k'afar shi cikin d'akin idanun shi suka hango mishi Umman shi kwance an lullu6e da zani, da sauri ya k'arasa wajen gaban shi na tsananta fad'uwa, hannun shi na rawa ya sanya akan zanin ya fara janye shi a hankali, fuskar Fatima ce ta bayyana kamar an kirata ta amsa, sai kace ba matacciya ba, tuni Aliyu ya durkushe tare da sakin wani irin kuka yana cewa "Umma ki tashi don Allah kada ki tafi ki barmu a wannan duniyar mu kad'ai" Kuka sosai Aliyu yake yana sumbatu, ganin haka ya sanya Baba Adamu ya janye shi daga gaban gawar Fatima dakyar don shima hawayen yake yi, Babaa Lantana kuwa da Aliyah Suhaima kuka suke yi sosai. Daga k'arshe Baba Adamu ya fita don sanar wa da jama'ar gari, cikin k'ank'anin lokaci mutuwar Fatima baiwar Allah ta zagaye cikin k'auyen nasu, sosai mutane sun jimanta rasuwar ta tare da yaba kyawawan halayen ta, da irin yanda take hak'uri da jure irin rashin mutunci irin na mijin ta wanda sam kanshi ya sani. Babu jimawa mutane suka taru akayi wa Fatima wanka aka had'a ta cikin likkafani, sannan daga k'arshe aka sadata da gidan ta na gaskiya, gidan da shi muke jira Allah ya jik'an wad'anda suka mutu mu kuma Allah yasa mu cika da imani Amin. Aliyu da Suhaima sun sha kuka kuwa, musamman Aliyu don yafi Suhaima hankali sai yafi jin rad'ad'in mutuwar fiye da ita, su Baba Adamu da Babaa Lantana ne suke tausar su tare da yi musu nasihar yarda da k'addara, lokacin Fatima ne yayi don haka Allah ya d'auki abarshi, kowanne mutum da iyakacin lokacin da Allah ya d'ibar mishi yanzu Fatima addu'a tafi buk'ata fiye da komai, Allah yasa mu dace duniya da lahira Amin. Haka Aliyu da Suhaima suka rungume maraicin su, sun koma abin tausayi, bayan sadakar bakwai ne 'yan uwan Fatima suka nemi tafiya da Suhaima shi kuma Aliyu ya zauna a wajen 'yan uwan uban shi, amman k'ememe Aliyu ya yak'i yarda da tafiya da Suhaima, anyi rarrashin sunyi fad'an amman ina yak'i aminta dole suka damk'a amanar su hannun Babaa Lantana da Baba Adamu, tukunna suka tafi bayan su bawa Aliyu wani d'an taimakon da zai nemi wata sana'ar ta domin kula da kansu. Haka rayuwa ta cigaba da tafiya, inda Aliyu da Suhaima suka sake shak'uwa da junan su, komai Aliyu ya samu zaka ji bakin shi na ambatar Suhaima, kulawa sosai yake bata don shi yafi tausayin ta fiye da kanshi, sai dai ita Suhaima ta koma gidan Babaa Lantana da zama sai dai tana shigowa wajen Yayan nata tana tayashi 'yar hira. Aliyu ya dage da yin sana'a kowacce iri ce indai zai samu halal d'in shi, aiki yake yi sosai na k'arfi kuma, haka ya dunga tara kud'i har ya sanya Suhaima a makarantar primary tana nan cikin k'auyen nasu tare da islamiya, babu dad'e wa Suhaima ta fara zuwa makaranta hankali kwance, kullum shi zai kai ta a tsohon keken da Baba Adamu ya cika mishi kud'i ya siya, haka idan aka taso su zai zo ya d'auke ta. Ganin Aliyu ya fi karkata akan son yin noma da kiwo yasa Baba Adamu bashi aron gonar shi guda d'aya don yana yin amfani da ita, shi kuma ya rik'e guda d'aya, da yake gonakin nashi guda biyu ne manya, gashi gonar da ya bawa Aliyu aro a kusa da gidan su Aliyun take, idan ma mutum bai kula ba ya d'auka kamar gidan a tsakiyar gonar yake, sosai Aliyu yayi murna da wannan karamcin da Baba Adamu yayi mishi. **** **** **** Haka lokaci ya cigaba da tafiya watanni da shekaru na wuce wa kamar kiftawar ido, Suhaima an fara zama 'yammata an don har ta kammala makarantar primary sun zana commen interest tana gida ana jiran fitowar result sai makarantar islamiyya da take cigaba da zuwa. Yayin da Aliyu an zama matashin saurayi, ya zama cikakken manomi a yanzu, don ya rik'e sana'ar noma da kiwo, da wannan gonar da Baba Adamu ya bashi aro yake noman shi and cikin ta har zuwa yanzu da ta zama mallakin shi, don tuni Baba Adamu ya siyar mishi da ita, bayan aikin noma kuma yana yin kiwo irin su kaji, awakai da shanu sai kuma yana siyar da kwan kaji sosai yake samu bud'i a harkar shi, ga taimakawar wani amintaccen yaron shi da Baba Adamu ya sama mishi yana taimaka mishi. Ya gyara gidan su sosai yayi kyau, inda a lokacin kuma Baba Adamu ya nemi da yayi aure, babu 6ata lokaci ya sanar musu da Aliyah d'iyar shi yake sosai, babu wanda bai yi farinciki da hakan ba don haka babu 6ata Lokaci akayi aure amarya ta tare a gidan ta, nan kusa da gidan su tun da Aliyu a asalin gidan su ya zauna, a lokacin kuma Suhaima ta dawo hannun Yayan ta da zama, zaman su suke cikin kwanciyar hankali da farinciki, Aliyu ya mayar da hankalin shi sosai kan sana'ar tashi, ya dad'a zama wani babban mutum musamm da yanzu yayi aure. Kamar yau ne ranar laraba ranar da kasuwar garin nasu take ci, tun safe Aliyu ya bar k'auyen nasu ya tafi cikin birni kai wasu kwai masu yawa, wajen mutumin da yake kaiwa ya siya a kan machine d'in shi, don haka gidan ya rage daga Aliyah sai Suhaima a ciki. Ranar Suhaima cikin farinciki take saboda Yayan ta baya nan, zata je cin kasuwa don haka da wuri tayi wanka ta ci gayun ta cikin wata atampa mai kalar milk da brown a jiki, ta sanya hijab d'in ta k'arami kalar brown, sannan ta fito daga d'akin ta zuwa wajen da Aliyah take. Aliyah tana zaune tana gyaran kayan miya don tana son gama girki da wuri kafin Aliyu ya dawo, ta hango Suhaima tana tahowa zuwa wajen ta, fuskar ta d'auke da murmishi tace " Suhaima wannan gayun fa ina zuwa? " Cikin dariya Suhaima tace "Yaya Aliyah nayi kyau ne?" Itama Aliyah tana dariya tace "Sosai ma 'yar k'anwata kinyi kyau, ina zuwa? " "Cin kasuwa zan je " Zaro ido Aliyah tayi tare da cewa "Haba Suhaima kin mance Yayan ki baya son kina zuwa koh, yanzu idan ya dawo bakyanan nasan fad'a zai mana ni da ke " Shagwa6e fuska Suhaima tayi tare da cewa "Haba Yayah Aliyah kafin ya dawo fah na dawo, ba dad'e wa zanyi ba " "Toh shikenan amman don Allah kada ki dad'e " "Yawwa Yayah Aliyah nagode, kuma bazan dad'e ba " Murmishi suka yiwa junan su, sannan Aliyah ta d'auko kud'i ta bata, godiya tayi tukunna ta tafi cikin zuciyar ta fal farinciki. Tana fita waje ta tarar da k'awayen ta suna jiran ta, nan suka tafi kasuwar suna tarar ana tacin kasuwa ga mutane daban daban har da na maraya ma suna zuwa cin kasuwar. Suhaima

Table of Contents

Chapters

104 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});