Chapter 97
Chapter 97
shi kulawa sosai take samu daga mijinta, Yayanta da Aunty Aliyah ga su Babaa Lantana nan har Baban ta ma kullum sai ya shigo dubata kuma sai ya taho mata da d'an abin kwad'ayi gaba d'aya yayi wani sanyi kamar ba Umaru ba, Jiddah tayi farinciki sosai da albishir d'in da Sabeer yayi mata na Suhaima tana da ciki. "Baby nah yau me zaki ce ne? " Sabeer ya tambaye ta yana sanya kaya fitowar shi daga wanka kenan. Kallon shi tayi idanun ta tap da kwalla tace "Ni bana sha'awar cin komai " K'arasa sanya kayan yayi sannan ya zauna kusa da ita tare da d'ago ta ya d'aura ta kan k'afafun shi, kallon ta yake cikin tausayi yace "Bazan barki baki ci komai ba Baby ki fad'a min please " Shiru tayi na d'an mintuna kafin tace "Zan sha fruits toh sun ishe ni " D'an murmishi yayi kan yace "Yawwa Baby nah haka nake son ji bari naje na samo miki " Kwantar da ita yayi saboda jikin ba k'arfi, ya bud'e mata curtains d'in window da na k'ofa don ta samu iska tana shigowa, sannan ya dawo yayi kissing nata a goshi ya fita, ya dad'e tsaye a k'ofar gida yana tunani don duk kud'in da yazo dasu sun k'are ragowar d'ari biyar ce dashi yanzu ya siyowa Suhaima fruit's da ita sun k'are, gashi gobe ko anjima idan tana son wani abu baisan yanda zai yi ba kuma shi bazai ta6a neman kud'i wajen Aliyu ba wanda shima fama yake da hidimar karatu ga d'aukan ciyar su abin da yawa gaskiya gashi duk master card d'in shi da atm card's nashi duk suna gida bai taho dasu ba da wannan tunanin ya tafi. Wajen 30 minute's da fitar shi ya dawo lokacin Aunty Aliyah ta shiga duba ta kuma tana tambayar ta abin da zata ci, d'auko wani bowl na silver yayi da wuk'a bayan ya wanke fruits d'in zama yayi saman carpet din d'akin zai fara yanka mata Aunty Aliyah tace "Sabeer kawo na yanka mana " Murmishi yayi yana cewa "Mamin Ameer ki barni aiki nane kije ki huta kawai " Itama murmishi tayi kafin ta wuce ta fita, Suhaima na kallon shi har ya gama yanka rabi iya yanda zata iya sha anjima sai ya yanka mata sauran. Kusa da ita ya dawo tare da tashin ta zaune ya jingina bayanta da pillow ya fara bata fruit d'in a hankali take bud'e bakin yake bata, duk da Sabeer yana iyakar d'auke damuwa akan fuskar shi ta rashin kud'i da kewar iyayen shi da 'yan uwan shi ga kuma rashin lafiyar Suhaima duk dashi wannan laulayi ne sai anyi hak'uri na d'an wani lokaci amman lalurar ta tsaya mishi a rai har wani d'an rame wa yayi amman duk da haka sai da Suhaima ta gane akwai wani abin da yake damun shi koda ta tambaye shi baya sanar da ita abin da ke damunshi sai dai ya fad'a mata rashin lafiyar tace take damunshi kyale shi kawai tayi amman tasan da wani abin sai dai ta dage da addu'a Allah ya yaye mishi koma mene. Bayan ya gama bata ta shanye shi gaba d'aya cikin tausayin ta ya kalle ta tare da cewa "Na k'ara miki wani? " Murmishin yak'e tayi kafin ta girgiza kanta kawai. "Okay ni zan fita Baby zamu fita da Ashiru amman bazan dad'e ba" Cikin sanyin murya irin ta mara lafiya tace "Allah ya kiyaye hanya ya dawo min da kai lafiya " Cikin murmishi yace "Amin Sweetie nah " Ya k'arasa maganar yana bata peck a kumatu itama tayi mishi a saman lips d'in shi daga haka ya fita daga d'akin Suhaima tabi shi da kallon tausayi. Haka lokaci ya cigaba da tafiy har aka shiga watan ramadan zuwa wannan lokacin jikin Suhaima ya d'an warware zata ci kowann abinci sai dai har idan ita zata dafa da kanta ba zata iya ci ba, kulawa babu irin wadda bata samu, har azumin ma tun da aka fara take jarumtar yinshi batason tasha, Sabeer kam matsalar kud'i ta yi mishi sauk'i don Daddyn shi ya sanya Jiddah kawo mishi atm card nash duk lokacin da yake buk'ata zai je ya cira amman sai dai idan ya kasance muhimmiya ce saboda yana ganin Aliyu bazai ji dad'i ba zai yi tunanin ya raina duk kulawar da yake bashi. Da haka suka cinye wata ramadan aka shiga hidimar sallah, Yah Aliyu yayi matuk'ar kok'arin yi musu d'inkunan sallah haka aka cinye bikin sallah lafia, sosai cikin Suhaima yake girma zama dakyar tashi dakyar sosai cikin yake da girma. Sabeer ba k'aramin tausayin ta yake ji ba haka da dare zai sanya ta a gaba yana faman kallonta tare da shafa cikin kafin ya tashi ya d'aura alwala yana kai kukan shi gun mai dukka akan ya sauki Suhaima lafiya, har wata rama yayi ta fargaba idan ya tuna yasha jin labarin haihuwa akwai wahala, daman tana zuwa awo amman a asibitin cikin gari duk ranar awo shi yake kaita ya jira ta gama su shiga adaidaita sahu ko taxi su dawo gida. Cikin haka cikin Suhaima ya shiga watan haihuwar shi sai zuba ido ake ana jiran haihuwa shiru, yayin da Jiddah da siyo duk wani abin daya danganci kayan jariri unisex da duk wani abin buk'ata Sabeer ya bata atm card nashi taje ta ciri kud'i ta siyo, duk an gama shirin komai sai jiran haihuwa duk wani masoyin Suhaima yana mata addu'a ta Allah ya rabata lafiya da abin da yake cikinta saboda girman cikin kadai ya isa firgita mutum duk ta wani kumbura tayi wani iri kamar ba ita ba kaya sai dai ta zura dogowar riga saboda riga da siket ko da zani bata jin dad'in amfani dasu dogowar rigar ma irin buba nan mara shape, Baba Adamu kullum cikin yi mata rubutu yake na sauk'in nakuda tana sha. Sai da cikin Suhaima ya shiga wata goma cif cikin wata safiya ta monday ta tashi da azababben ciwon nakuda Allah yaso Yah Aliyu da Sabeer duk suna gida basu fita ba nan da nan aka samo taxi suka tafi asibitin da take zuwa awo, suna zuwa aka kar6eta cikin gaggawa suka wuce da ita labour room Sabeer ji yake kamar ya bita ciki amman Yah Aliyu ya rik'e shi gam ganin yanda jikin shi yake rawa yace "Sabeer addu'a kawa zaka yi mata " Nan ya zube akan benci kawai yana faman yin addu'ar duk wadda tazo cikin bakin shi. Suhaima kuwa abin ba'a cewa komai iyakar wahala tasha ta kamar bazata iya haihuwa da kanta ba ma, tasha kukan har hawayen suka daina fita daga idonta saboda azaba addu'a kowacce yin ta take tana fatan Allah ya rabata da cikin nan lafiya, tun safe ake abu d'aya har zuwa k'arfe 9 na dare sannan wahalar ta tazo k'arshe inda ta haifi kyawawa yaran ta guda biyu duk maza wanda suka kasance lafiyayyu masu koshin lafiya, tana gama haihuwar su da taja wani numfashi sai ta zube nan nurse suka yi kok'arin wajen farfad'owar ta sannan suka gyara mata jikinta tsaf bayan sun gama suka sanya mata drip na k'ara k'arfin jiki da kuma allurar
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104