Chapter 10
Chapter 10
sakarwa junan su a lokaci d'aya, tukunna Daddy yace "Hey Mrs Hussein d'an fillo thanks for ur fantastic kiss" Fari da eye's nata Mummy tayi tare da kama hannun shi suka nufi upstairs don ta shirya shi zuwa fita office. WANE NE SABEER HUSSEIN D'AN FILLO? SORRY FANS BAN DA CHARGE NE, MU HAD'U A NEXT PAGE DON SANIN WANE SABEER. AISHAT A MUH'D ✍🏻 [2/4, 11:28 AM] Aıʂɧąɬ A Mųɧ'ɖ ✍🏻: 💝 A SANADIN SON KI 💝 Written by Aishat A Muh'd ♻EXCLUSIVE WRITERS FORUM Dedicated to my Sadeey saNaz PAGE 13-14 Family d'in Alhj d'an fillo asalin su irin fulanin nan ne wanda suke da arzik'i sosai na dukiya da ababan kiwo, Alhj Ahmad d'an fillo shine d'a d'aya a wajen mahaifin shi da mahaifiyar shi sai 'yan uba k'annen shi su uku dukka mata shi d'aya ne namiji mazauna garin adamawa state, shi yasa mahaifin shi ya tsaya akan bashi ilimin boko, duk da su ma matan ya sanya su a makarantar iyakar su secondary ya aurar dasu. Bayan Ahmad ya kammala karatun shi na fannin Lafiya ya samu aiki sai iyayen shi suka aura mishi wata Hauwaa wadda ta kasance 'yar uwar shi ce, watannin su uku da aure iyayen shi suka yi accident a hanyar su ta zuwa airport don zuwa k'asa mai tsarki domin gabatar da hajji, dukannin su suka rasu, mutuwar ba k'aramin girgiza Ahmad da matar shi Hauwaa tare da sauran 'yan uwan su tayi ba, sosai mutuwar ta shige su amman haka suka rungume hak'uri don sunsan haka Allah ya tsara zata faru. Bayan shekara d'aya da rasuwar iyayen shi matar shi Hauwaa ta haihu 'yan biyu suka samu, sunyi matuk'ar murna da farinciki, inda suka bar musu sunan su na Hassan da Hussein, sun cigaba da rainon yaran su cikin kulawa, watan su uku da haihuwa Hassan ya rasu sakamakon zazza6i mai zafi da ciwon ciki da yayi wanda kwanaki biyu yayi yana jinya a hospital ya rasu, sosai mutuwar Hassan ta bige su don sai zafin mutuwar iyayen shi ta dawo mishi sabuwa a lokacin, haka suka dangana suna masu bawa Hussein kulawa. Hussein yana da shekara hud'u Dr Ahmad d'an fillo ya samu transfer zuwa Malam Aminu kano teaching hospital, ba 6ata lokaci ya tattara komai nasu suka dawo garin Kano, sai da ya fara zama a gidajen hospital d'in kafin ya gina nashi gidan, don zaman garin Kano yayi mishi dad'i. Bayan an gama mishi ginin suka dawo cikin sabon gidan su a lokacin Hauwaa ta haifi d'an ta na biyu Omar, bayan shekara biyu ta sake haihuwar Usman, daga Usman sai Aminu sannan autar su Fadilah, sun cigaba da rainon yaran su cikin kulawa da k'auna makarantu masu kyau da tsada Dr Ahmad d'an fillo ya sanya yaran shi, sai dai sun fi bawa boko mahimmanci fiye da ilimin Islam, a lokacin Dr Ahmad d'an fillo ya tsunduma harkar business sosai wanda nan da nan kud'i sosai suka fara samuwa ba kad'an ba. Haka lokaci ya cigaba da tafiya yaran shi dukka sun girma kowannen su ya gama karatun shi yana aiki, Hussein business d'in da mahaifin shi yake ya tsunduma a ciki, Omar kuma yana aikin Bank, Usman kuma a wani babban company na abokin Dr Ahmad d'an fillo yake aiki a matsayin GM na company d'in, sai Aminu da yake lecturing a BUK, sai k'aramar su Fadilah da take karatun degree a wannan lokacin, wanda gab take da ta kammala har an sanya lokacin auren ta da wanda zata aura, iyayen shi masu kud'i ne shima haka yana da kud'i abokin yayan ta Omar ne, lokacin da ya nuna yana son ta sosai iyayen ta suka yi farinciki da hakan, saboda suna da kud'i don Dr Ahmad d'an fillo da 'ya'yan shi basa harka da talakan mutum sai ta kama, don akwai su da kyamar talaka harkokin shi sai da masu kud'i 'yan uwan shi. Shiyasa ba 6ata lokaci aka sanya lokacin auren Fadilah da Mustapha, bayan ta kammala degree d'in ta aka yi biki sosai sun kashe kud'i a bikin, bayan auren Fadilah suma Yayannin ta kowanne ya fito da matar aure duk yaran masu kud'i ne daman gashi akwai su da kyau irin na fulani ga kud'i kuma da wayewa, sai da ban da Babban Yaya Hussein don shi harkar neman kud'in shi ya sanya a gaba bai fiye, kuma iyayen nashi sam basu tak'ura mishi ba da yayi aure, kafin bikin ne Dr Ahmad d'an fillo ya gina k'aton gida mai d'auke da part's biyar kuma kowanne part babba ne sosai kuma upstairs ne, an kashe kud'i sosai a wannan gidan kafin bikin suka koma can da zama abin su. Sai da Omar, Usman da Aminu suka haifi yara kowanne biyu biyu kuma kowanne yaro da tazarar shekara wajen uku a tsakani,tukunna Hussein ya kawo matar da zai aura Dr Faridah cikakkiyar likitar mata ce wato gynecology a k'asar India tayi karatun ta, iyayen ta masu kud'i ne sosai ne kuma abokin Dr Alhj Ahmad d'an fillo ne sosai da sosai, lokacin da Dr Ahmad d'an fillo yaji d'an shi Hussein Dr Faridah zai aura ba k'aramin farinciki suka yi ba shi da Hajja Hauwaa, nan aka sanya lokacin biki two weeks kawai, an kashe kud'i bana wasa ba a wannan auren, don su kansu matan Omar, Usman da Aminu sun san an auro matar so kuma ta gaban goshin surukan nasu don yanda suka ga ana ji da ita tun kafin ta shigo gidan. Dr Faridah Bashir kyakkyawa ce kuma wayayyiya ce sai dai akwai ta da wulak'anci ba kad'an ba, gata kuma ta tsani wani talaka ya ra6e ta, kanta kawai ta sani, ga nuna tak'ama da tsantsar ak'idar Boko, kuma mahaifin ta hospital babba ya bud'e mata nata na kanta don su biyu kad'ai Allah ya bashi daga Faridah sai k'anwar ta Zahra, ga zata auri mai kud'i don Hussein duk yafi 'yan uwan shi kud'i, wad'annan halayen nata su suka k'ara mata matsayi cikin zuciyar surukin ta Dr Ahmad d'an fillo fiye da sauran surukan nashi, yana ji da ita matuk'ar gaske. Bayan auren Hussein da Dr Faridah sai da suka yi wajen shekara uku ko 6atan wata bata ta6ayi ba, sosai hankalin su ya tashi nan aka shiga ziyartar asibitocin k'asashen waje domin bincikar lafiyar su, amman k'alau suke lokaci ne bai yi don komai kud'in ka sai lokacin da Allah ya nufa zaka samu abu zaka same shi, balle haihuwa da lafiya wanda kud'i baya ta6a siyan su sai lokacin da Allah yaso zai baka, gajiya sukayi da zuwa hospitals suka zubawa sarautar Allah ido tare da tsananta addu'a sosai a wajen Ubangiji, Dr Ahmad d'an fillo da Hajjah Hauwaa suma duk'ufa da addu'a suka yi sosai don suna k'aunar son ganin jikan su na wurin Hussein da Dr Faridah. Sai da suka kwashe shekara hud'u da aure kafin Allah ya bawa Faridah ciki, murna da farinciki bazai fad'u ba irin wanda suka yi, nan suka dunga rainon cikin cikin so da k'auna. Bayan wata tara Faridah ta haihu an samu baby boy kyakkyawan yaro dashi, anyi murna da farinciki sosai, ranar suna ansha taro an kashe kud'i duk wanda yaje sunan yasan an haifi
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104