Chapter 71
Chapter 71
" Dariya aka sake kwashewa da ita, sannan Khairat tace "Ina fah zata rabu dashi Aunty taga kyakkyawan saurayi sabon jini ga kud'i da ilimi inace ko aji ma ta ta6a shiga wannan shegiyar Jiddah ce ta wayar da ita " Wani irin kuka mai tattare da bak'inciki Suhaima ta saki saboda ta kasa rik'e kukan nata, aikuwa ganin haka suka kwashe da dariya tare da tafawa, sannan Aunty Fadilah ta bud'e bottle d'in faro da yake hannun ta sai kawai Suhaima jin saukar ruwa mai sanyi da taji ajikinta har sai da ta saki ajiyar zuciya mai karfin gaske. "Shegiya mara zuciya idan kin cika ke mai zuciya ce kare bai d'auke ba ki rabu da Sabeer daga yau " "Aunty mu taya ki " Cewar Zahra da Khairat sarakan tsiwa. "Ku taho mana 'yan 'ya'yana masu kishin 'yan uwan su " "Don Allah Aunty kuyi hak'uri kada ku min haka " Cewar Jiddah tana kuka da karfi tana kare Suhaima, ture ta Aunty Fadilah tayi nan Zahra da Khairat suka dunga bud'e bottles na faro suna shek'a mata a jikinta suna zaginta da yi mata rashin mutunci duk gaba d'aya sun jik'e jikinta jagab da ruwa gashi don mugunta da ruwan sanyi suke amfani. Yusrah yayar Jiddah da batason hayaniya tabar dakin bata jin dad'in abin da suke mata ba amman da yake miskilace sai kawai ta bar wajen. Jiddah tana cikin kuka ne d'ago kan da zata yi sukayi 4 eye's da Sabeer tsaye ya hard'e hannun shi a kirjin shi eyes nashi sunyi ja tare da fuskar shi, sai da gaban Jiddah yayi mugun fad'uwa ganin yanda d'an uwan nata ya rikid'a kamar ba Sabeer ba, bata ta6a ganin shi cikin makamancin irin wannan yanayin ba. Zahra ce ta fara arba da Sabeer ta ankara dashi tuni tayi cilli da bottle d'in hannun ta jikinta ya fara rawa na tsoro, haka ma Khairat itama ta cillar da robar tana rarraba ido Aunty Fadilah kuwa sai da gabanta ya fad'i da suka had'a ido da Sabeer don bata ta6a ganin shi a haka ba batasan lokacin da ta saki nata robar ba. Cikin wani irin taku na fusata ya k'arasa shiga d'akin bai kalli inda suke ba ya k'arasa inda Suhaima ke zaune jikin ta jagab da ruwa har tsiyaya yake d'ago ta yayi tare da kallon Jiddah yace "Kai ta wani bedroom d'in ki bata kaya ta canja " Muryar shi dakyar take fitowa saboda tsananin 6acin rai jikin shi har wani rawa yake, da sauri Jiddah taja hannun Suhaima wadda take kuka sosai suka fita. Aunty Fadilah, Zahra da Khairat kuwa suman tsaye suka yi ko motsin kirki sun kasa yi, Zahra bata ankara ba taji saukar wani zazzafan mari mai saurin kurmanta mutum wani ihun k'ara ta saki da karfin gaske ya fara dukanta yana ball da ita cikin zafin nama, Khairat tun kafin azo kanta take rusa kuka sosai tana dana sanin biyewa zuciyarta da Aunty Fadilah. Bata ankara ba taji saukar nata marin wanda har sai da bakin ta ya fashe, belt d'in jikin shi ya cire ya fara narkar su cikin tsananin 6acin rai har wasu hawaye ne suke zuba a eyes nashi zuciyar shi tana zafi. "Sabeer mene haka kashe su zaka yi ne akan wannan matsiyaciyar yarinyar ne " Bata gama rufe bakin ta ba taji saukan mari akan face d'in ta da mamaki ta d'ago kanta ta d'auka Sabeer ne ya mare ta sai taga ashe Daddy ne. Zaro ido tayi cikin tsorata tace "Yaya! " Sake kwad'a mata mari yayi tare da cewa "Rufe min baki mara kunya banza mara kunyar wofi " Cikin 6acin rai Daddy yake fad'in haka ashe Jiddah ce ta kirawo shi tana kuka tana yi mishi bayanin abin da yake faruwa shine ya taho. Dakyar aka kwaci Zahra da Khairat a hannun Sabeer aka fita dasu daga d'akin duk ya farfasa musu jikin su ko kuka sun kasa saboda azaba, zubewa yayi kan carpet tare da rik'e kanshi da hannun shi yana sakin wani ajiyar zuciya. Babu dad'ewa gaba d'aya kusan family suka had'u a gidan Jiddah har da Dr Ahmad d'an fillo, Hajjah Hauwaa wadda take kuka wiwi Sabeer zai kashe mata 'yan jikoki akan wannan shegiyar yarinyar amman ta kasa yiwa Sabeer fad'a saboda son da take mishi sai hucin da take saki. Dr Faridah ma ranta a 6ace sosai da kanta tayi treatment d'in su Zahra da Khairat a inda suka ji ciwo dole ta d'auki mataki akan wannan shegiyar, Aunty Fadilah kuwa tayi tsit da ita sai raba ido take saboda ba k'aramin tsoron Daddy take ba. Suhaima bayan ta canja kaya ne tana kwance wani zazzafan zazza6i ne ya rufe ta kuka take sosai yau taga karshen wulak'anci dole ta rabu da Sabeer duk da kuwa son da take mishi bazata jure wulak'anci da zagan mata da mahaifiya da suke wadda take kwance a kabari. Dakyar Daddy ya rik'o hannun Sabeer suka fito zuwa parlour kallo d'aya Dr d'an fillo yayi mishi yaji duk haushin dukan da yayiwa su Zahra ya kau hankalin shi ya tashi sosai ganin yanda d'an lelen shi ya koma dole yayi wa su Aunty Fadilah tatas don kawai Sabeer yaji sassauci ya nuna musu abin da suka yi basu kyauta ba daga karshe kuma yayi musu iyaka da matar Sabeer. Daga karshe tafiya suka yi gaba d'ayan su, Mumy kuwa aranta haka tace kowa ya gama nashi rashin mutuncin akan wannan yarinyar yanzu lokacin ta yayi dole tayi nasarar raba Sabeer da Suhaima rabuwa ta har abadaaa......... Aıʂɧąɬ A Mųɧ'ɖ ✍🏻 [4/9, 9:15 PM] Aıʂɧąɬ A Mųɧ'ɖ ✍🏻: *A̺͆ S̺͆A̺͆N̺͆A̺͆D̺͆I̺͆N̺͆ S̺͆O̺͆N̺͆ K̺͆I̺͆* Wྂrྂiྂtྂtྂeྂnྂ bྂyྂ Aྂıʂɧąɬ Aྂ Mྂųɧ'ɖ ɖɛɖı¢ąɬɛɖ ɬơ ɱყ ʂąɖɛɛყ ʂąŋąʑ ♻ *Eҳ¢ʂųιı۷ɛ щγıɬɛγ'ʂ ʄơγųɱ* *PAGE 87-88* Shiga cikin bedroom d'in da take a kwance yayi hawa kan bed d'in yayi yana kok'arin had'a ta da jikin shi duk da jikinta ba kwari sai da tayi kok'arin matsawa da sauri, cikin marairaicewa Sabeer yace "Baby please kada ki hora ni akan abin da akayi miki, bazan jure hakan ba " Kamar zai yi kuka yake maganar, cikin muryar ta wadda ta dushashe tace "Mu hakura da junan mu Sabeer 'yan uwanka basa sona sun tsaneni" "Nooo! Baby ki daina fad'in haka bazan iya rabuwa dake ba, ni ina sonki kuma ni zan zauna dake basu ba " Duk yanda yaso yanda yaso ya had'a ta da jikin shi don ya rarrashe ta tak'i yarda, gashi kukan ta yana ta6a mishi zuciya, bata ankara ba taji Sabeer yana fitar da hawaye. Kallon shi ta tsaya yi kawai ana cikin haka Jiddah ta shigo da sauri ya goge hawayen shi don bayason ta gani, cikin sanyin murya yace "Jiddah ki tayani rarrashin Baby tace bazata koma gidana ba" Cikin jin tausayin su ta zauna tana kama hannun Suhaima tace "Haba Suhaima mene hakan idan kika yi hakan ai abin da suke so kenan, taya zaki zalunci kanku bayan kuna son junan su kice zaku rabu, kiyi hak'uri don Allah kada ki rabu da Yah Sabeer yana son ki " Rarrashin ta sosai Jiddah take dakyar ta ciyo kanta ta amince, rungume ta Sabeer yayi don jin dad'in abin da ta fad'a. Har an
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104