Chapter 2
Chapter 2
na tsane shi kamar yanda yace baya son mu ya tsane m........ " Kafin ta k'arasa fad'in maganar taji an zabga mata wani wawan mari wanda yasa ta hantsila k'asa, ledar garin kwakin ta baje a k'asa ta tarwatse cikin dandaryar k'asar tsakar gidan. Ashe basu ankara da shigowar baban nasu ba gidan, yaji abin da Suhaima ta fad'a shine yayi mata wannan marin da ko babba aka yiwa sai haka, cikin rashin imani ya kama Suhaima ya hau dukan ta kamar Allah ya aiko shi, Umma tana d'aki idar da sallahr mangarib d'in da tayi kenan tana sauri ta fito don ta jawa Suhaima kunne ta daina wad'annan maganganun, don lokacin da dawowar uban su gida yayi, sai kawai taji saukar dukan da yake yiwa Suhaima runtse idon ta tayi da k'arfi hawaye na fita a cikin su tana mai addu'ar Allah yasa kada yayi mata bugun da zai illata ta. Yana dukan ta cikin fushi yana cewa "shegiya tsinanniya daman ni ai ba son ku nake ba, da zaki ce baza ki min addu'a ba sai uwar ki da Yayan ki, na tsane ku bazan ta6a kaunar ku 'yan iska matsiyata " Cikin kuka Aliyu yace "Don Allah Baba kayi hak'uri ka dai na dukan ta, ka ga Suhaima yarinya ce k'arama ba zata jure dukan nan ba " Sakin Suhaima yayi yana haki kamar wanda yake jibgar k'atu, harara ya dalla wa Aliyu tare da cewa "Don uwar ka ni zaka fad'a wa gaskiya koh ?" Kafin Aliyu ya ankara tuni Baban ya kawo mishi duka nan ya had'a su ya dunga duka kamar Allah ya aiko shi, sai da yayi musu lilis tukunna ya ce " yanzu na fara dukan ku 'yan iska, Allah yasa ku mutu na huta da ganin ku" Da sauri Umma ta runtse idon ta tana rushe wa da kuka jin mummunan kalaman da uban su yake yiwa 'ya'yan ta wanda ba yau ta saba jin su a bakin shi ba. Yana gama fad'in haka ya fice daga gidan yana fad'a kamar wani ta6a66e, Umma tana jin yana fita ta fito waje da sauri zuwa wurin 'ya'yan nata da suke kwance magashiyan a k'asa suna kukan azabar dukan da aka yi musu. Nan Umma ta rasa me zata yi musu kawai sai ta had'a ruwa mai d'umi ta fara yiwa Suhaima wanka, daman ta d'ora ruwan tun kafin mangarib, sai da ta gama yi mata wanka ta gasa mata jikin ta, tukunna ta kai ta d'aki ta kwantar da ita, sannan ta dawo wajen Aliyu ta kai shi band'aki tare da ruwan wanka tace "kayi hak'uri Aliyu na, maza kayi wanka ka gasa jikin ka " Gid'a mata kai kawai ya iya yi, sannan ta fito ta tattara garin kwakin da ya zube ta tsince shi tukunna ta jik'a musu. Dawo wa d'akin tayi ta tashi Suhaima sanya mata kaya tayi sannan ta zuba mata garin a kofi ta mik'a mata, ai kuwa da sauri ta kar6a ta hau shan shi babu k'akk'auta wa. Ido Umma ta tsura mata tana kallon kumbararriyar fuskar ta ta zuciyar ta fal tausayin su, tana nan zaune Aliyu ya shigo d'akin dakyar ya iya yin sallah sannan ya zauna, mik'a mishi nashi garin Umma tayi girgiza kanshi yayi yana cewa "Umma ki sha kawai na k'oshi " Girgiza kanta ita ma tayi idanun ta fal hawaye tace "A'a Aliyu ka kar6a kasha idan kana son ganin kwanciyar hankali na " Bashi da yanda zai yi ya kar6a ya fara sha a nutse, ita ma Umma ta d'auki ragowar tana sha, bankad'a labulen d'akin aka yi tare da shigowa ba sallama, babu wanda ya d'ago kan shi ya kalli kofar saboda sun san wane mai shigo wa d'akin a haka. Ko kallon su bai yi ba ya shige k'uryar d'akin ya zauna saman gadon tare da bud'e kunshin tsire da gurasar da ya siyo ya hau cin abin shi hankali kwance, tuni d'akin ya d'umame da k'amshin naman da gurasar suka hau had'iyar yawu dukanin su har da Umma. Abin ka da mai ciki akwai kwad'ayi gashi ba ci ake ba nan ta shiga had'iyar yawu akai akai haka ma Suhaima, kallon Aliyu yake yi zuciyar shi tana zafi na tsanar halayyan mahaifin nashi, tashi tsaye yayi tare da cewa "Umma zan kwanta sai da safe " Don idan bai fita daga d'akin nan ba zai iya had'iyar zuciya ya mutu saboda tsabar bak'in ciki, kallon shi Umma tayi tare da cewa "Allah ya tashe mu lafia " "Amin " Yace tare da fice wa a fusace. "shege mai zuciyar tsiya da bak'in hali " Babu wanda ya tanka mishi har Suhaima bacci ya d'auke ta tana had'iyar yawu na son cin naman, kwantar da ita tayi tare da lullu6e ta da zani saboda lokacin hunturu ne. Tashi tayi tare da nufar gefen gadon k'arfen nata ta kwanta a can k'arshe tana mai tunanin makomar rayuwar su a gaba, ga cikin ta da yake k'ugin yunwa da haka bacci ya fara d'aukan ta, can cikin baccin nata taji mijin nata na lalubar ta alamar akwai abin da yake nema a wajen ta, wasu hawaye ne masu zafi suka dunga fita a idanun ta, duk dare ta saba da wannan halin mijin nata gashi ba abinci kirki yake basu ba, shi yasa kullum take tashi jiki ba kwari a gala6aice, tana kuka shi kuma yana sha'anin gaban shi har zuwa lokacin da ya rabu da ita ya juya mata baya, ba dad'e wa ta fara jin saukar minsharin shi, dakyar ta iya mik'e wa ta fito zuwa band'aki tayi wanka don bata iya bacci a haka, tana fito wa ta ga Aliyu zaune a tsakiyar gidan ga tsananin sanyin da ake zabga wa cikin mamaki tace "Aliyu lafiya? " D'ago kanshi yayi tare da cewa "Umma na kasa bacci ne, zuciya ta rad'ad'i take min " Ya k'arasa fad'a hawaye na fita a idon shi, cikin tausayin shi tace "kayi hak'uri Aliyu komai tsanani yana tare da sauk'i, bana son kana sa damuwa a ran ka wani ciwon ya kama min kai, kasan kai ne mai taimakon mu, yanzu tashi kayi alwala kayi sallah tare da addu'a, ka mik'a wa Allah buk'atun ka " Tana nan tsaye yayi alwala sannan ya shige d'akin shi, tukunna ta juya ta shige d'akin ta kwanta, jikin ta babu k'arfi da ita ma nafilar zata yi ta fad'a wa Allah matsalar ta, amman duk da haka sai da ta janyo carbi ta fara istigifari tare da salatin Annabi (SAW), da haka bacci mai k'arfi ya d'auke ta........... *** **** *** *ASALIN LABARIN SU* Aishat A Muh'd ✍🏻 [2/4, 11:28 AM] Aıʂɧąɬ A Mųɧ'ɖ ✍🏻: 💝 *A SANADIN SON KI*💝 *written by* Aishat A Muh'd ♻ £xclusive Writers Forum *Dedicated to My Sadeey (SaNaz)* *PAGE 3-4* Umaru direba miji ne a wurin Fatima, auren so da kauna suka yi don sai da suka d'an jima suna soyayya kafin su yi aure. Bayan sun yi aure ne suna zaman su lafia cike da so da kulawar junan su, don ma bai fiye zama a gida ba tun da direba ne shi suna tafiye tafiye zuwa garuruwa daban daban, amman hakan bai hana shi kula
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104