Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 97

Chapter 97

Hayateem Book 1 Complete Hausa Novel 1,203 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

Maa sakina jikinta na wata irin rawa ta fice da gudu tana nufar dakinsa idanuwanta na tara ruwan mummunan tashin hankali da tsoron dayake jijjiga rayuwarta dan kuwa bazata iya rayuwar da babu Baa dinta a ciki ba,mutuwa zatayi idan ta rasashi a rayuwarta sbd shine ginshikin rayuwarta da duka rayuwarta take tangale da soyayyarsa. Saka Kai tayi a dakin tana jefa idonta Akan gadonsa dayake kwance taga babu kowa akai, Wani irin sarawa kanta yayi ta juyo da gudu dukkanin jikinta na wata irin rawar data saka kafafunta suka yanke zata fadi sakinah data biyota da sauri tana hawaye tayi saurin tareta jikinta tana kokarin rungumeta amma ta kasa tsayawa ta nufi fada da gudu idanuwanta basa gani sbd tsananin fita hayyacin data fara ta bude baki da Wani irin sautin daya ratsa kunnuwan duk Wanda yake masarautar cikin wani irin tada tsigar jiki tace ‘Baaa’ Tana saka Kai cikin fadar Kai tsaye da wannan sautin daidai nasu sautin ya shiga kunnuwanta na Sarkin fada dayake cewa ‘Auren NUAB ALMAZZ ya dauru da AYANAH BAHAR GHAZ Wanda muna fatar mutuwa ce kadai zata rabaaaa’ Kamar saukar gudu ma a tsakiyar kanta taji saukar zancen Wanda ya saka idanuwanta qarasa rasa ganinsu ta kafesu Akan Sarkin fada tana bude baki kanta na mantawa da komai Bayan son ganin mahaifinta da sautin daya saka Aleey dagowa a cikin wani irin yanayi me sanyin jikin auren da aka daura amma ya kasa kallanta sbd a yanzu da igiyoyin auren ubangidansa suka riga suka hau kanta idanuwansu bazasu iya mata kallan Kai tsaye batareda girmamawa ba koda kuwa aure ne da a yanzu baida suna bare matsayi kwata kwata a rayuwar me BOYEM din dan kuwa bai dauka auren ne shima yayi ba abu daya ya sani koma menene yayi sa ne dan tabbatarda karban Abaas Wanda yake rayuwar Amminsa. ‘Yet niw Abaa,yet niw Esu?’ Ta fada idanuwanta na kafe Akan Sarkin fada Wanda ya sauke Numfashi me tsananin sanyi da mutuwar jikin rabuwar da zeyi dasu a lokaci daya babu shiru babu sani ba tareda tinanin hakan ba dan ya dauka shine zai shafe Abaas da kansa ya kuma zama uban BAHAR din wadda zai aurar da ita ga nasa dan amma ko a hakan baiyi baqin ciki ba sbd shi kansa zaifi farin ciki idan Abaas yaje amma idan har hakan shine zai hada Abaas da Ayanaah to wannan shine gatan karshe da zai masa shi da Bahar wadda batasan kowaba a dangin uwa da ubanta ba. Tasowa yayi ya iso gaban Bahar din zai furta sunanta ta ja da baya cikin wani irin mutuwar jiki da mafi girman tashin hankalin rayuwarta tana girgiza Kai ta sake furta sunan Abaa dinta idanuwanta na yin wani irin ja hawaye masu tsananin zafi na taruwa a cikinsu sbd kadaici ze kasheta idan Abaa yabarta shine kadai ran dayake cikin empty rayuwarta da babu kowa a ciki sai zallan sunayen da babusu maana yan uwan mahaifin nata da iya sunansu ne basu ba a rayuwarta. NUAB da idanuwansa suke rintse tin lokacinda aka shafa fatihar auren dago kansa yayi ahankali yana bude idanuwansa da sukai jajir ya saukesu Akan fararen kafafun dasuke gabansa masu haske sosai na daukan hankali sarkar Farin azurfan dayake kafar duk motsinta daya na ja da Bayan datake Wani sauti me yar qarar dake shiga kunnuwansa yake fitarwa Wanda ya sakasa dauke jajayen idanuwansa zuciyarsa na Wani irin Zafin lokacin daya bata na cetan Abaas a gurin daurin auren da bai dauru ba a zuciya da rayuwarsa dan kuwa aure ne kadai na biyan buqatar wannan lokacin da suke so na tafiya da Abaas dan haka miqewa yayi batareda ya juyo ya kallo kowaba ya nufi kofa a takunsa na natsuwa da jinin mulkin daya dame sarautar GHAZ ya fice batareda ya cewa kowa komaiba. Yana ficewa Aleey ya miqe shima yabi bayansa Bayan ya dan kalli Maa sakinah dake Bayan BAHAR da Sarkin fada yace suna jiransu a waje. NUAB na fito bike din dake nan Sauran daya daya raye shi ya hau Kai tsaye ya wuce aka bar GHAZ din dashi. Su aleey sai Sauran bikes din sun dawo da sukaji kai Abaas dan haka Aleey fidda wayar sa yayi yafara zagaya masarautar yana daukan videos din dayasan buqatan hakan zata iya tasowa daga baya dan haka ya bawa Maa sakinah da Sarkin fada guri da zasuyi magana da Bahar wadda babu abinda take son ji da gani kawai idan ba mahaifinta ba dan mantawa ma kwakwalwanta tayi da abinda taji na maganar auren da kunnuwanta sukaji an daura da sunanta kawai mahaifinta takeso da ganin idan ba tafiya yayi ya barta ba dan haka ta rikice musu gabaki daya Wani irin rawa jikinta keyi tana ambatar sunansa da karfin gasken daya saka a rikice aka fiddota aka tafi da ita zuwa garesa Bayan Sauran bikes din sun dawo. Sbd yanda Bahar din ta fice hayyacinta tana kasa yadda da kowa harma da Maa sakinah ya saka dole da Sarkin fada aka tafi dan rakiya garesu. Koda suka nufo wajen gari idanuwanta tsananta jajir sukeyi cikin wani irin nauyin kirji na zuciya take jinta duniyar na sake mata duhun da tasan itama kila a cikinsa zata rayu ta mutu kaman yanda mahaifinta ya rayu ya tsufa a cikinsa. Koda suka iso an bawa Abaas taimakon gaggawan dayake buqata amma suna buqatan gaggawar isa dashi asibiti Wanda Dr ya bada shawarar bazai iya kaiwa qasar BOYEM a hakan ba dole suna buqatan fita can cikin babban birnin wannan qasar da suke ciki su fara tsayawa anan dashi asibiti saiya samu dan saukin da zai iya qarasawa dashi qasar BOYEM indai anason ya rayu. NUAB baida raayin tsayawa kowace qasa dashi Bayan BOYEM amma kuma ga yanayin jikin nasa dayake gani dole maganar Dr din zasu bi ta tsayawa asibitin qasar kafin daga baya su wuce idan ya dan zama stable sbd mummunan nisa yayi Wanda yake girgiza zuciyar NUAB din yanajin kaman bazai taba iya fuskantar Amminsa ba idan Abaas yabar duniya sbd baisan tayaya har abada zai iya fada mata Abaas dinta ya tafi yabartaba dan hakan shine blow na karshe da rayuwarta zata iya samu dan haka zaiyi iya kokarinsa yaga ya isar mata BOYEM dashi koda ganin karshe ne su yiwa juna. Kai tsaye barin ruwan dajin ANJOM GHAZ sukai Wanda kila shikenan sun barsa a rayuwarsu, Sakinah tsirawa dajin ido tayi bata kyaftawa zuciyarta na narkewa fiyeda a baya ANJOM shine garin da har su mutu bazasu Dena marmarin dawowa su qarasa rayuwa a cikinsa ba. Bahar ma dake Zaune gaban mahaifinta hannunta ta saka ahankali cikin nasa ta Kama tareda hade tafin hannuwansu tana Lumshe idanuwanta da sukai jajir wasu hawaye masu dumin cikinsu suka gangaro mata Sarkin fada ma kusa da ita su kadai a dakin dayake Sarkin fada na fada mata ‘dan Ayanar mahaifinta ne Yazo ga mahaifin nata dan basa lafiya. Babu kowane irin farin ciki ko Jin dadi ko daya daya sauka ga zuciyarta na abinda Sarkin fadan ya fada sbd babu Sauran kowace kauna ko soyayyar datake Jin zuciyarta nada damar yiwa kowa sbd bata tashi da kowa ba a rayuwarta daga ita sai mahaifinta tayi rayuwa, Rayuwa da

Table of Contents

Chapters

106 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});