Chapter 77
Chapter 77
da sultan suke gani tinda bata gabansa babu abinda yake gabansa nata likita dayane tinda ya nadasa mai duba lafiyar Ayanah din shikenan baitaba fasa zuwa bibiyan lafiyar taba koda Yaushe a tsawon shekarun nan, ‘Ammi’ ya Ambaci sunanta cikin sanyi da kauna me girman gaske tareda nutsuwan da bayason damar da ita sbd jinta shiru. A sanyaye ta sauke bayyananniyar Numfashi jikinta gabaki daya a mace ta bude Baki tace ‘NUAB,Yene HAYATEEM,Yene LEUL idanuwana suna son ganinka, Zuciyana da ruhina duka san ganinka sukeyi kafin na…..’ Katseta yayi da tsananin nutsuwa da cewa ‘AMMI’ sbd yasan kalman mutuwa ne zata qarasa dashi, Tsigar jikinsa ne suka sake tashi a hankali Wani irin yanayin da mahaifiyarsa ce kadai ke motsa zuciyarsa na ratsashi sbd ya tabbatarda akwai abinda yake damunta ko zuciyarta dayayi girman datake buqatan ganinsa harta furta da bakinta, Dole wata damuwarce take faruwa da kila batasan tayaya zata iya gane wa ko fada masa ba kawai ta buqaci ganinsa sbd zuciya da ruhinta su sanyaya, Numfashi mara sauti ya kuma saukewa tareda dagowa idanuwansa farare tas masu Kayar da gaba da suka sauya a take suna dan rikida da ja ya bude Baki a natse yace ‘Ammi bakida lafiya ne? Girgiza masa Kai tayi a hankali da sanyi kaman yana kusa da ita Wanda sautin ya shigar masa kunne a cikin sanyi dan haka ya rufe idanuwansa ahankali ya kuma bude su yace ‘Akwai abinda yake damunki Ammi? Nan ma girgiza Kai tayi a natse batareda tinanin ba lallai ya fahimta ba, Nan ma yaji Gyada kan sbd akwai yan kunnen zinari masu dan fidda sauti kadan a kunnuwanta Wanda ya saka idan ta girgiza Kai sautin su ke shiga kunnuwansa suna narkar da zuciyarsa da babu abinda take tsananin so da kauna a duniya idan ba ita din ba ‘Ammi akwai Wanda ya saka miki damuwa’ Girgiza Kai tayi ya sauke Numfashi me sauti wannan Karan ya bude baki zaiyi magana muryanta ta Katsesa a sanyaye tace ‘Idan zaka taho kazo da Abaas,ina son ganinsa HAYATEEM’ Rufe idanuwansa yayi a Wani irin yanayin da zuciyarsa ke cizo da radadin kasa bawa macen da ita kadai ce rayuwansa abinda takeso sama da shekaru masu yawa. ‘Ammi zan taho gareki ba tareda Abaas ba amma nayi miki alkawarin indai Abaas yana raye zan kawo miki shi a gabanki, Nayi miki Alkwarin indai Abaas yana raye zan Nemo miki shi zai qarasa rayuwarsa a gabanki bazai taba barin gabanki ba har sai mutuwa ta rabaku….. Wasu hawaye ne suka gangaro idanuwanta da suka saka hankalin sakinah dake tareda ita a palo Zaune tashi sbd bata kuka Sam a yanzu sbd kuncinta da baason ya dawo dan haka a natse ta iso gurinta ta zauna gefenta ta kalli wayar hannunta ta miqa hannu tace ‘Nima zan gaisa dashi’ Miqa mata wayar Ayanah tayi cikin nutsuwa tana cewa ta yadda da NUAB zai cika mata wannan alkawarin ko Bayan ranta ne zai nema Abaas. Maganar tata har kunnuwansa ta sauka ta shigesa a hankali ya Lumshe idanuwansa yana Jin wata wuta mai Zafin gaske tana kunnuwa a zuciyarsa ta son kasancewa da mahaifiyarsa da tabbas lokaci yayi da zai dawo da ita hannunsa dan kuwa daman magana daya ce duk ranar daya saka kafa a BOYEM to bazai taba tafiya batareda mahaifiyarsa ba, Babu me buqatarta a masarautar da qasar gabaki daya hatta Wanda take zamansa baya buqatanta ya watsar da ita tin tanada kuruciya dan haka shi babu abinda yake buqata a rayuwarsa sama da ita a basa ita kawai shine cikar duk wani burinsa na rayuwa Bayan hakan baya buqatar komai a rayuwarsa. Saukar muryan Maa sakinah a kunnuwansa ya sakasa bude idanuwana jajir yana bude baki a natse da kulawa yace ‘Maa akwai abinda yake faruwa ne?? Akwai abinda ya kamata na sani ne?? Amminah na da damuwa ne? Akwai abinda yake faruwa a masarautar ne daya taba Amminah? A Jere ya jerowa Maa sakinah tambayoyin da suka saka jikinta sanyi ta sauke ajiyan zuciya mara karfi tareda bude Baki cikin nutsuwa ta manyanci tace ‘Babu komai dayake faruwa kawai dai yanayi ne na kewanka datake yi shine kadai ya saka amma ka damu babu abinda yake faruwa’ Shiru yayi itama Maa sakinan yana karantar yanayin muryanta datai sanyi sosai, Kai tsaye yace ‘Maa akwai abinda yake damunki kema? Menene yake faruwa a masarautar nan? Waye ya tabaku? Katsesa tayi da sauri tana kokarin daidaita kanta cikin sauti da dan sauri sbd Jin yanda muryansa ta fara sauyawa tana daukan Zafi da fushinsa da babu me iya kashe wutarsa tin yana yaro tace ‘Babu komai Ka yadda da hakan LEUL,kada Ka bata ranka ko kadan dukanmu muna cikin kwanciyan hankali da lafiya’ Kasa nutsar da zuciyarsa dake daukan zafi yayi ya bude Baki cikin sassauci yayi sallama da ita Kai tsaye wayar Maa tenya ya kira yana bude idanunwansa da sukai jajir Akan Agogon dayake palon dan kuwa matiqar yaji ya tabbatarda akwai damuwan dasuke ciki babu abinda zai Hana jirginsa sauka BOYEM kafin fitowan alfijir din asubar gobe. Maa tenya dake dakinta ta gama sallar nafila wayarta dake kan marble center table din dayake lafiyayyan dakinta da babu duniyar da babu a cikinsa koina na Qamshi da sanyin ac tafara ringing. Hannunta ta miqa a sanyaye ta dauki wayar tareda dauka ta Dora a kunnanta cikin sanyi tayi sallama tana miqa masa gaisuwan data zama kaman dole kasancewansa jinin BOYEM kuma asalin magajin karagar mulkin. Bai amsa gaisuwan sarautarsa ba ya miqo mata tasa gaisuwan ta zamanta uwa a garesa kafin ya Dora da cewa ‘Maa idan akwai abinda yake faruwa ki sanar dani sbd ina rasa hankalina anan sbd Amminah akwai abinda yake damunta kuma Inason saninsa koma menene’ Ajiye Numfashi me sauti sosai tayi kafin ta sake shiga sanyi da nutsuwa tace ‘Allah ya qara maka lafiyar zuciya LEUL BOYEM Amminka jikinta yana Neman dawowa sosai a kwanakin nan rikicewa kawai lafiyarta ke kokarin yi Wanda tabbas tana buqatan ganinka takeso kafin ta qarasa rasa cikakken hankalinta ta manta waye Kai………. Shiru da tsit yaji duniya gabaki daya tana masa sai yanajin muryan Maa din tamkar sautin dayake tahowa daga nesa sbd straight zuciyarsa labarin ya caka yanajin dumi na gauraye jikinsa koina musamman idanuwansa da sukai jajir. Kasa iya cewa komai yayi sai sallama da yayi mata yana kashe wayar idanuwansa na tsananta ja ya da dago ya saukewa aleey su dayake tsaye gefe yana jiran umarnin koma menene yakeson Ayi. Kallan da yayiwa aleey Wanda ke kallansa cikeda nutsuwa da girmamawa take aleey ya fahimci umarnin sa dan haka Kai tsaye cikin girmamawa da cika umarni yace ‘Aiit B’ iPad din hannunsa ya daga yafara dannawa yana fidda wayar sa itama ya saka kira yana Juyawa yabar gurin yana fara aikin da baya buqatan bata lokaci dan kuwa kome zai tsaya cak sai LEUL BOYEM ya isa fadar da tasa ce gabaki dayanta. Shi kuwa ajiye wayar hannunsa yayi tareda Dora kafarsa Ka daya a hankali yana jingina bayansa da kujeran dayake Zaune yayi folding hannuwansa duka biyu kirjinsa yana Lumshe idanuwansa ya rufe dan kuwa a yanzu komai na rayuwarsa ya tsaya cak har saiya isa yayi tozali da mahaifiyarsa wadda shekaru
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106