Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 73

Chapter 73

Hayateem Book 1 Complete Hausa Novel 1,203 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

Aslm da meryam ta ukunsu neesat tayi aurenta sbd rayuwarta akwai sauki sabanin ta yan uwanta, Rashin aurensu nada nasaba ne da rashin shaawan auren da basu da shi sbd raayin hakan da mahaifiyarsu ta cusa musu sbd batason su taba aure Masarautar da batai ko kusan matsayin ta mahaifinsu ba, Duk masarautun da ake aurar da yayan masarautar BOYEM basuyi ikon Masarautar boyem dinba sbd ta boyem din itace wadda babu kamarta dan hakanne dole sai wadda bata kaitaba amma suma Masarautun baa baya sukeba ko kadan ga tarin arziki da dukiyar da bata Jin kashewa tareda iko da mulki me karfi ta qasashe daban daban amma duk da hakan HAILE ta kasa barin yayanta su zaba ko daya daga cikin duk masauratun da ake kawo musu tayin aure gashi a al’adar BOYEM sukuma mazan ne kadai basada ikon auren macen daba jinin ahalin ba amma matan Ana aurar dasu wani gurin kuma Sam baa taba yiwa macen datake jinin BOYEM auren tilas saida cikakken raayinta sbd zataje ne qasar daba tata ba idan akai mata tilas zata rasa ahalinta kuma taje tayi qunci dan haka basa tilas tin farko ga matan boyem, Wannan dalilin ne ya saka yayan nata suke Zaune masarautar mahaifinsu haryanzu hakama a tsaye suke qyam Akan tabbatarda karban mulkin dan uwansu Wanda tsufa ya kamasu a gida batareda sun ankare ba takai sultan ya rufe kofar Neman aurensu kwata kwata hukuncin su sai ranar da aka nada sabon sultan a Masarautar BOYEM shine zai bude musu kofar Neman aurensu daya rufe, Hukuncin ya rikitar da rayuwarsu kwata kwata ta juye ta zama baqin cikin da babu Sauran hasken sauki a cikinsu sai zallar rashin imanin yadda da hakura daga abinda suke so dan kuwa indai wannan hukuncin dake kansu zasu jira to ko zasu kashe rai nawa suma saisun tabbatarda ASIM ne ya zama sultan dan kuwa idan ba shidinba ya hau babu me dauke wannan hukuncin zasu tsufa su mutu ne ba aure dan haka babban burinsu na rayuwa Akan tasu dalilin na tsananin son aure ya karfafa kudirinsu Akan hawan ASIM boyem dan yanzu wannan ne ma babban dalilinsu na jajircewa, Ita kanta queen HAILE wannan shine dalili na biyu me karfi daya sakata tsayuwa Akan qudiri daya na tabbatar da ASIM ya karbi mulkin boyem sbd ganin yayanta zasu suna shirin tsufa su mutu babu aure ga qanwarsu neesat dake aure Masarautar Malaysia yayanta hudu babban ‘danta ma yana kokarin shiga university amma su Sauran suna gida manyanci yana sako musu Kai dan kuwa shekaru ashirin ake magana yanzu ko Bayan Barin NUAB ALMAZZ kasar idan aka hada da shekarunsu na baya ma suna hararar shekarun da suke Neman na wuce aure ma. *******wishmah Ayanah tinda ‘danta hasken idaniyarta da zuciyarta ya tafi bata taba sake walwala ba a tsayin shekarun nan, Bata taba manta tsananin soyayya da kaunar datake masa ba kona daqiqa daya, Bata taba manta kamanninsa ba, Bata taba dena kewa da tsananin son ganinsa ba duk da babu ranar da baya wuni kiransu akai akai yana video call da itaba sbd tsananin kauna da soyayyar dayake mata wadda ta zarta rayuwarsa da babu komai a ciki sai emptiness da Wani irin Zafin jinin sarauta dayake yawo a jininsa fiyeda mahaifinsa, Wishmah a hankali taci gaba da manta komai da kowa harta gama mance komai a rayuwarta bata tina komai da kowa Bayan mutane biyar da sune rayuwarta,sune ji da ganinta a yanzu datake tamkar sabuwar haihuwa, Qunci da baqin cikinta sun wanke babusu a zuciyarta sbd Manta komai datai dan haka rayuwarta take simple fayau ba damuwa da tashin hankali Bayan damuwan rashin HAYATEEM dinta da baya tareda ita Wanda shima hakanan koyaushe take rasa dalilin daya saka bakinta yake furta masa kada ya dawo qasar BOYEM Wanda shi kansa NUAB din wannan furucin nata ne ya hanasa dawowa qasar wadda har abada ya fitar da ita cikin ransa baida niyar dawowa rayuwa a cikinta. Mutane biyar da su kadai ne a zuciya da kwakwalwan wishmah sune, Shi kansa HAYATEEM din nata sai Mahaifinsa sultan data kasa cirewa a cikin kanta Wanda duk tsawon shekarun nan babu ranar da shima baya video call da ita kowace asuba sedai bata cewa komai haka zai kira ya zuba mata idanuwansa yana kallanta tana masa shiru batareda cewa komaiba itama tana kallansa harta gaji ta kife wayar tayi kwanciyarta tenya tazo ta dauki wayar ta fice da ita Wanda hakan wani sirri ne da babu Wanda ya sani a duniya daga sultan din se tenya wadda itama ta rasa dalilin sa na hakan a kowace asubar bayan kuma ya Riga ya nunawa duniya wishmah da ‘danta basa gabansa. #MAMUH #LEUL NUAB ALMAZZ BOYEM #BOYEM LEUL #ALMAZZ NUAB HAYATEEM by Mamuhgee 700 0022419171 AccessBank Maraym Sani gummi 09033181070 Yan Nijar kuma 89825722 Depot my nita Nissaiba laouali [09/12, 10:47 am] Asia ahmd: *_HAYATEEM_* Mamuhgee 48 Bayan NUAB da sultan YASAR dake zuciyar Ayanah ABAAS ne Wanda bakinta bai taba qasa da kasa fada ba hakama zuciyarta bata taba mantawa da tsananin sonsa da kaunarsa ba hakama bakinta bai taba gazawa da fadawa NUAB yayi mata alkawarin kawo mata Abaas kada ta mutu bata gansa ba ta sake rungumar sa a jikin taba Wanda ba ita kadaiba zuwa yanzu babban kudurinsa na rayuwa ya zama na bawa mahaifiyarsa abinda takeso, Sauran mutum da sukafi kowa zamowa rayuwarta ta yau da kullum Bayan ‘danta da Abaas sune sakinah da tenya da suka sadaukar da rayuwarsu tin daga Sauran yarinta da suke da ita har zuwa yanzu da manyanci ya Kama su dukan sun tsaya da lafiyarsu da lokacinsu da rayuwarsu sun bata kariya da kulawa kuma sun shirya hakan har qarshen rayuwarsu data rage musu dan haka itama duk da a yanayi na rashin memory da rashin nutsuwa da lafiyar tinani sune wainda ta sani kadai a rayuwarta datake jinsu har jini da ruhinta da suka zame jininta koda basu hada jinin ba a yanzu sune asalin jininta datake kalla dan a lokuta da dama idan dan tinaninta da ya hau daidai takan zauna ta qura musu ido ta ringa kiransu da Zuhrah da Nurat tana hawaye tana rintse ido sbd ciwo da radadin na taso mata a kirji da baa son kwata kwata taba tinawa da wannan kuncin sbd lafiyarta da kome zai iya faruwa idan wannan quncin da baqin cikin ya dawo mata cikin kwakwalwa dan hakanne kwata kwata Bayan kokarin kulawa da sake mantar da ita komai babu abinda su tenya ke kokarin yi, Baa iya zuciyar wishmah sukeda matsayi me girma ba a zuciyar NUAB ALMAZZ su din taurari biyu ne da bazai taba iya biya ba har qarshen rayuwarsa, Su din haske ne a rayuwarsa da suka bawa halittar datafi komai na duniyarsa daraja kulawa da tattalin datake buqata a lokacin da bata kowa a duniya Bayan shi kadai kuma aka rabasa da ita, Sun kular masa da ita tin baizo duniya ba harma Yazo duniyar ya zama abinda ya zama yanzu Amma haryanxu sune suke tsaye akanta Bayan Wanda take full responsibility yayi watsi da rayuwarta batada amfanin komai a rayuwarsa baya buqatanta bayin matarsa ma sunfita daraja. Bayan zallar kauna mai girma da darajar su dayake

Table of Contents

Chapters

106 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});