Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 89

Chapter 89

Hayateem Book 1 Complete Hausa Novel 1,201 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

kokuma idan Wani abin ne ya faru dan kuwa tasan tabarta da shirin tafiya gurin sultan. Tana isowa ta tarar da ko magana Mamee din bata iya yi kirjinta ke tsananin ciwo da zafi sosai idanuwanta sunyi jajir ajiyan zuciya kawai takeyi me Zafi da karfi akai akai bakinta baya iya furta komai. Kallan fetto Aslam din tayi ta tambayeta meya samu mameen Bayanin komai fetto tayi mata Wanda ya saka Aslam din juyowa ta kalli mahaifiyarta itama idanuwanta na sauyawa zuciyarta tayi dum tama rasa abin fada sbd alamu na sake tabbatarda masifu da ranakun baqin cikinsu zasu bude su fara ne matiqar NUAB na nan dan kuwa dasu da bokayen su sun tabbatarda shine matsalar datake tsakaninsu da dukkanin Buri,nutsuwa,kwanciyan hankali da farin cikinsu da suke buqatar kawar wa matiqar suna son rayuwa da wainnan abubuwan. Shekara sama da ashirin rabon sultan da Wishmarsa, Ya rufe ya shafe babinta a rayuwarsa da shimfidarsa kaman yanda kowa da Masarautar suka rufe shafinta a cikin matan sultan, Wace masifar ce take Neman kunno Kai da a cikin Daren nan wannan mummunan sakon zai bayyana? Me sultan yake shirin yi na maida wishmah matsayinta a dare guda batareda tsammanin kowaba, Tayaya macen da suke son ‘dan tawayen ‘danta ya tattarata ya tafi da ita ko su aika masa ita sama zaa ce an maida mata matsayinta dayake tabbatarwa duniya ita din cikakkiyar ikon da mallakar sultan ce. Wani nauyi kirjinta ya ta jefar da wayarta a kujeran dake dakin tana fasa kiran likita ta bude Baki kaman zuciyarta zatai aman wuta tace ‘Yanayin Mamee baa buqatan likita baqin ciki ne da dacin zuciya zata dawo daidai zuwa anjima idan ta samu sassauci’ Tana gama fadar hakan a koma kan kujeran ta zauna tana dafe goshinta dayake mata nauyi sbd ciwon Kai da bacin ran dayake cinta, Shiru sukai dukkaninsu kowa da yanda baqin cikinsa yake cin zuciya da kirjinsa, Meryam da aka aikawa mameen ba lafiya Kai tsaye tana zuwa taji abinda ya faru shiru tayi batareda tace komaiba ta jiya ta koma sbd batada abin fada hakama karfinta da lafiyarta Neman qarewa sukeyi a gurin dawainiya sa dakon baqin ciki da ritirin zuciya kullum Wanda a yanzu kam ta fara gajiya gangar jikinta ta fara gazawa ga daukan wannan baqin cikin da baida ranar qarewa bata fatar ta mutu a cikinsa batareda ta dandana farin ciki da kwanciyan hankalin gidan aure da tara zuria ba. ******Tenya kuwa a tsaye take qyam kan kafafunta tinda wannan sakon ya iso mata Wanda kwakwalwan kanta itama ta kasa dauka sbd babu ta yanda zaayi ace Bayan shekaru masu yawa da yafe wishmah daga zuciya da shimfidarsa rana tsaka dare daya yace ya dawo da ita a Daren da suke kallan Daren karshe na rayuwarsu a masarautar, A Daren da suke jiran gari ya waye masa su bar komai anan suje su shimfida sabuwar rayuwa, Shin sultan ya San da shirin tafiyarsu ne a goben daya yanke wannan hukuncin daya girgiza zukatansu dama duk Wanda zaiji cikakkiyar sanarwar zuwa da safe, A wane Hali NUAB zai tsinci wannan mummunan labarin ga kunnuwa da zuciyarsa sbd hakan da sultan yayi Baro Baro yana nuni da Hana cikar burin NUAB ne yayi ta hanya me sauki se karfi dan kuwa koda NUAB yake ‘danta Wanda yafi kusanci da ikonta Akan kowa zamtowanta wishmah din ubansa kuma maidata cikakken matsayinta ya kere kowace irin dama da ikon da ‘danta yake dashi akanta. Zufa ne a tsiyayo mata ahankali yana gangarowa daga gefen goshinta ta zame ahankali ta zauna gefen sakinah datai mutuwar Zaune itama idanuwanta jajir dan kuwa matiqar wannan mummunan sakon ya isa kunnan NUAB wutar tsanar mahaifinsa datake ransa ce zata sake hauhawa sbd tafiya da mahaifiyarsa bazai taba yiyuwaba gashi a yanzu datake cikin tsananin shauqin danta matiqar ya tafi yabarta batareda ya cika mata alkawarin tafiya da itaba komai zai iya faruwa da ita dan haka akwai tashin hankali a cikin wannan lamarin daya sauka a dare daya tamkar saukar aradu. Kasa isarwa da Ayanah sakon sukai dukkaninsu sbd basusan tayaya kwakwalwanta zata karbi sakon ba hakama basu saniba ko sakon ya isa kunnuwan NUAB shima basusan yaya zai amsa sakonba dan haka tamkar sakon mutuwa sakon ya zamewa kowane ba gangaren harda na maraki wadda itama daga sama taji sakon ya saukar mata kamar tsawa sbd ta Riga ta dauka ta sakawa zuciyarta sultan ya gama da wishmah kenan har karshen rayuwarta, Ko HAILE da zuriarta sun dauka ya gama da ita ya rufe babinta har qarshen rayuwarsa Shiyasa komai Yazo musu a mummunan bazata da gigita. Kowane bangare a cikin bangaren uku na matan nasa tsit ya dauka babu bangaren da ba a cikin dacin zuciya da mutuwar jiki me tsanani suke ba tareda fargaba dan kuwa abu ne dayazo babu shirinda zasu San yaya zasu tarbesa ba. Dare sake nutsuwa yakeyi Wanda ya saka tenya da suke Zaune zasuyi kwanan Zaune miqewa tayi shirin kaiwa sultan ziyara dan isar da rokon alfarmar da zasu buqata. Tareda bayi hudu ta isa bangaren sultan din ta isarwa da kadir roko da sassaucin da wishmah take nema daga sultan Akan zuwanta Ayau Yazo ba shiri sultan yayi mata Afuwan karbanta a gobe ba yau din ba sbd yanzu haka ta jima da bacci sbd yanayin jikinta. Kadir bai jima sosai a ciki ba gurin isar da sakon ya fito da sakon rokonsu ya karbu Ayau sultan ya mata Afuwa zuwa goben ta dawo cikakkiyar macensa wishmah dinsa. Da sanyin jiki tenya tayi godia da girmamawa ta juya ta bar gurin tana komawa bangarensu kowa yayi dakinsa cikin jimamin yanda zasu iya sanar da Ayanah a gobe ta Koma wishmah dinta bazata taba iya bin ‘danta ba sedai shi idan zai zauna Masarautar tareda ita. ********A daidai wannan lokacin NUAB yana tsaye tsakiyar palonsa idanuwansa jajir sunyi Wani irin jan daya saka gabaki daya Yaransa sunkuyar da kansu suna tsaye Jere a kofar palon babu me ikon cewa komai ko tambayar komai sbd fushi da wutar dake ci a idanuwan LEUL dinsu sun tabbatarda mahaifinsa ne kadai a duniyar nan ya isa ya tabasa haka batareda sun shiga ba amma wannan fadan ba gurin shigarsu bane amma dukda mahaifinsa ne yana cewa suyi Wani abin tsaf zasuyi batareda tsayawa komaiba dan haka Ayau da suke ganin fushi da tsananin bacin ran da basu taba ganiba a tattare dashi ba yasa sun tabbatarda akwai Sauran Wani abu koma menene a zuciyar NUAB gameda mahaifinsa dan ba dan hakan ba Ayau sultan YASAR bazai kwana da kansa Akan wuyansa ba batareda sun tabbatarda ya samu ganawa da malaikan daukan rai. Duk wata jijiyar dake jikinsa sun fiffito fuskarsa da kunnuwansa sunyi jajir Wanda ke bayyanarda ba qaramar wuta ce take ci a jini da zuciyarsa ba dan kuwa zuciyarsa gap take da bindiga Akan abinda yake ji, Duk yanda ya rayu cikin fushi da mahaifinsa Akan abinda yayi na rabasa da uwarsa bai taba dauka zuciyarsa takai maqurar matakin karshe na qinsa da mahaifiyarsa ba da har zai iya basa zabi biyu na abinda yasan babu Wanda zai taba yi a cikin biyu ? Bazai taba karban mulkin BOYEM ba sbd qiyayyar BOYEM da duk Wanda

Table of Contents

Chapters

106 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});