Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 40

Chapter 40

Hayateem Book 1 Complete Hausa Novel 1,202 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

da abinda yasa aka kawo su gurin, Taku sukeyi suna qarasa shiga ahankali a bayansu Zuhrah din Wanda Zuhrah na jin sautin saukar kowane takun Ayanaah din dake bayanta yana karya zuciyarta tana jin a daidai wannan lokacin ma Allah ya cika mata burinta tana taka guri daya tareda Ayanah tana shakar numfashin guri daya da Ayanah,jajir idanuwanta sukai itama tana ci gaba da taku mai sanyi batareda alaman ko juyowa ba kaman yanda itama Ayanah bata dago kai ba kanta a qasa yake tana bin sawun da Zuhrah ke wucewa da idanuwanta kaman ta durqusa ta sumbaci gurin, Ciki gabaki daya inda wani fadeden gurin gyaran jiki da wankan asalin lalle da qamshi dayake cike da pool din ruwan dumi da har wani hayaqi me qamshi yake tashi a cikinsa, Su tara ne cif aka zaba dan haka duk wadda aka shigo da ita ahankali ake tayata zare Kayan jikinta ta shiga ruwan Lallen da qamshi masu dumi Wanda zaa jiqa su a cikinsa tsawon wuni guda kullum haka zaa musu tsawon kwana uku sbd lalle yana tsotsewa da kashe kowace irin cuta dake jikin dan Adam dan haka sai an riqa jiqa su tsawon kwana uku sun rabu da kowace irin cutar wahala dake jikinsu tsaf kafin a fara jiqasu cikin ruwan madarar nonon raqumi shima. Zuhrah dake gaba bayin dake tareda ita ne ahankali suka zare mata Kayan jikinta daga ita sai kamfai irin na jikin kowa Wanda ake raba musu tareda uniform sai qarama rigar halfvest datake kame nonuwansu qarama ce sosai, Kama hannunta sukai suka isa bakin pool din da ita suna riqe da hannuwanta duka biyu ta zura kafafunta ahankali ta shige ruwan idanuwanta da zuciyarta babu inda suke Sai a tinanin Ayanaah dake bayanta wadda itama ahankali aka zare mata nata Kayan take gashinta ya sauka bayanta aka sakota cikin ruwan ahankali ta tako ta iso gefen Zuhrah wadda itace karshen shiga ruwan a tare suka zauna cikin ruwan ahankali gabaki daya jikinsu na shigewa har zuwa sama kirjinsu iya inda ruwan ya tsaya kenan. Wata Mutum daya ce aka sake shigowa da ita ta karshe kafin aka taho da wani sabon lallen mai dan yawa aka zuba a cikin ruwan tareda ruwan zafi dazai qarawa ruwan nasu dumi sosai ta yanda lallen zai ratsa koina a jikinsu sosai. Ana gama zuba musu komai Juyawa maaikatan sukai gabaki dayansu suka fice daga gurin tareda rufe kofar suka tsare bakin kofar sbd bazaa taba budewa ba sai lokacin fitowansu ruwan yayi. Daga Ayanah har Zuhrah babu tinanin dayake ransu Bayan son kasancewa a tare daidai wannan lokacin tareda son jin junansu dan haka gabaki daya sun manta da mummunan qazamin lamarin daya sakosu gurin fatansu daya kawai su kasance tare. Shiru gurin yayi kowacensu su taran da abinda yake ranta na wannan nannauyan kaddarar data hau kansu, Ratsasu ruwan dumin lallen keyi tako Ina suna jin dumin me zafi har cikin zuciyarsu sbd tsoron d suke ciki yafi komai yawa a cikin zama imebēti sbd kowane lokaci zasu iya rasa rayuwarsu dan haka kowa shiru yayi jiki a sanyaye ba kowane irin dogon motsi. Ayanaah ce ta bude idanuwanta da sukai jajir ahankali batareda ta juyo gefenta ba ta kalli Zuhrah da suke shaqan Numfashin guri daya ta miqa hannunta dake wata irin rawa sbd shauqin samun abinda zuciya ke so ta cikin ruwan ta Dora tafin hannunta ahankali kan na Zuhrah wadda tana jin saukan hannun Ayanah a kan fatar hannunta rintse idanuwanta tayi wasu hawaye masu tsananin zafi na gangarowa daga idanuwanta kanta na yin qasa ta damqa hannun Ayanah din tana qanqamewa cikin nata hawayenta na tsananta gudu cikeda shauqi da tsananin farin cikin data manta yaya dandanonsa yake a zuciya, Itama Ayanah hawayen ne ke ciko idanuwanta da sukai jajir tana hana nata hawayen sauka sbd kada a gano halinda suke ciki sedai tata zuciyar harma tafi ta Zuhrah karaya da samun wata irin nutsuwar ruhi da bata taba samu ba tinda rayuwarsu ta wargaje, Qanqame hannun juna sukai batareda sun juyo sun kalli juna ba ko motsin da zaa gane kowa da abinda yakeji a zuciya da gangar jiki, Zuhrah kuka takeyi sosai tana sake sunkuyar da kanta qasa sosai tana rokon Allah kada ya raba hannunta dana Ayanah har sai ranta yabar jikinta. Ayanah ma da kukanta ke komawa zuciyarta kukan zucin takeyi sosai jikinta na wata irin rawa tana sake qanqame hannun da shine hasken rayuwarta. A wannan yanayin suka share duka awannin da aka dibar musu a cikin ruwan har saida ruwan ya wuce salap suna cikinsa tukuna aka bude kofar tareda shigowa da wasu irin tsaftaccin towels masu dan girma farare qal a basket me kyau kowannensu da baiwar da zata basa nasa. A cikin wata irin saa me girman gaske saiga sakinah a cikin masu kawowan wadda kai tsaye gurin Ayanah ta nufa a natse kanta a qasa tana isa ta durqusa gaban a hankali tareda dago mata kyakkyawan kwandon da towel din yake ciki yana fidda qamshi me dadi. Cikin karfin Hali zuciyarsu na yanka suka raba hannuwansu kowacensu na Juyawa ta fice batareda kowa yaji muryan kowa ba sbd basuda daman magana baa basu damar ba. Towel din Ayanah ta dauka ahankali ta daura a jikinta Bayan sakinah ta miqe a natse ta tayata zare halfvst din jikinta, Juyawa sakinah tayi zata bar gurin kanta a qasa idanuwanta suka sauka akan Zuhrah wadda ke fitowa daga ruwan itama take jiri me karfin gaske ya dibeta saura kiris ta kife Allah ya bata ikon tsayawa dakyau tana hana firgicinta bayyana sbd zata iya rasa rayuwarta. Tsurawa Zuhrah idanuwanta tayi tana tafiya kanta na tsananin sarawa da abinda take gani, ‘Zuhrah da Ayanah a matsayin imebēti na Mutum daya?’ Wace irin mummunan qazamiya kuma haramtacciyar kaddara ce wannan? Tayaya Mutum daya zai kusance su kuma su samu cikinsa su haihu? Tayaya ma wannan tashin hankalin kaddarar zata fara? Shin Ayanah da Zuhrahn sunga junansu kuwa? Idan sun gani sun kuwa San menene yake shirin faruwa dasu? Idan har sun sani tasani zasu gwammaci su mutu su dukan dasu yadda da wannan mugun tashin hankalin’ Koda sakinah ta fito daga gurin bata ganin gabanta sosai sbd tama kasa yadda da Zuhrah ce idanuwanta suka gano mata dan bama zai taba yiyuwaba wannan kaddarar a yanzu kam tayi nauyin da kila dole zaa iya rasa dayansu biyun. Su kuwa suna gama daura towels din daya bayan aka nuna musu wata kofa suka shiga toilet ne masu kyau da tsari a jere dan suyi wanka da ruwan dumi sosai kafin su fito kowacensu akaita sabon gurin da zata zauna, Suna shiga gurin a kebe yake dan haka rufe su akai sbd su ayanzu ba kowa akeso yaga jikinsu ba dan kuwa sun zama tamkar Al’aurar da haramun ne ganin jikinsu, Ana rufe su kowacensu ta nufi toilet daya ta shige aka bar Ayanah a tsaye tareda Zuhrah wadda itama take tsaye cak babu Wanda ya motsa a cikinsu tsawon mintina uku, Tsit gurin yayi sai motsin ruwan daya fara tashi ahankali na fara wankan da Sauran sukai, Sai a lokacin Ayanah ta dago ahankali cikin wani irin slow na tsananin mutuwan jiki ta Dora fararen idanuwanta masu

Table of Contents

Chapters

106 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});