Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 12

Chapter 12

Hayateem Book 1 Complete Hausa Novel 1,202 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

Juyawa sosai amma har lokacin karesu takeyi da hannuwanta, Jin kaman zuciyarta na Neman bugawa ta juyo tsoronta da tsananin tausayinta akansu na qaruwa sbd sun riga sun rasa yanci da gata harma da asalinsu tareda rayuwansu batareda sun San yaya duniyar take ba a wajen gidansu,a kuma wajen garinsu,a Bayan ran iyayensu, Basusan yaya zasu gudanar da rayuwarda babu iyayensu a cikinta ba koda iyayensu na raye bare yanxu da basa duniyar, Ko a darasin ilimin rayuwa da iyayensu ke musu tareda tarihi da labarun rayuwar dake gudana a duniya wadda baa cikin ANJOM ba baa taba fada musu menene asalin zamowa bawa ba da ukubar dake cikin bauta wadda bakasan karshentaba ko Ka samu yanci wata rana kokuma Ka mutu a cikinta. Wani irin Jan rikitarwa idanuwanta suka tana saka hannunta daya a kirjinta tana dafewa Ahankali ta kalli Ayanah tareda bude bakinta ahankali ta Ambaci sunanta kafin ta maida idanuwanta Akan Abaas datafi shaquwa dashi tareda tsananin kauna a tsakaninsu me karfin gaske ta qura masa ido wasu irin hawaye masu tsananin ciwo na gangaro mata ta sunkuyar da kanta qasa tana jin rayuwarta kwata kwata bata da sauran amfani. Dagowa tayi ta kalli kusrawan da sukayo kansu kowannesu na zaro mummunar wuqar da zata yanka Mutum a qanqanin daqiqu fit ta rabaka da ranka. Lumshe idanuwa Ayanah tayi suna sake rungume junansu dukkaninsu suna samun nutsuwa da saukin a rabasu da ransu su bi iyayensu yafi musu saukin rayuwan da basusan yaya ake gudanar da itaba, Rayuwar da babu tabbacin ko zasu take ko wahala da gagari zasu yi karshe su mutu a cikin garari dan haka gwara tin a qasar garinsu batareda sun bar garin da gawar iyayensu take ba subar duniyar. Abaas dayansu ya fizgo da karfin gaske yana Dora wuqa mai tsananin kaifi da wani mummunan fadi a wuyansa zai fizge jijiyar wuyansa da wuqar Asamah ce da idanuwanta ke cikowa da hawaye masu radadin gaske ta bude baki jikinta na saki tace ‘Inada damar alfarma guda daya tak da khams ya bani a matsayin abinda zaa biyani dashi kuma dukkaninku kun San da hakan’ Cikin rashin Imani Wanda yake riqe da wuqar a wuyan Abaas yace ‘Damarki guda daya ce tak kina fadarta shikenan kin rasa kowace irin dama…… Katsesa tayi muryanta na sake raunana da cewa ‘Kar a kashe ko dayansu shine abu daya tak danake so…… Dukkanin kusra dariya me karfi suna kece da ita kafin babban cikinsu ya kalleta cikin tinatar da ita babban gangancin da zatai wa rayuwarta sbd Ana cika mata wannan buqatar ita rasa nata ran zatai yace ‘Kina sane a dama daya tak da aka baki zaki iya zabar abarki da rayuwarki kitafi duk inda zaki ki Gina sabuwar rayuwa? Kina sane da hakan? Sannan Kina sane da idan kika zabi rayuwarsu ke bazaki rayu ba??? Gangarowa hawayen cikin idanuwanta da sukai jajir sukai ta juya sake kallansu babu Wanda jikinsa baya kakkarwa cikin wani irin mummunan halin daya saka zuciyarta sake nauyi, Abaas ta zubawa idanuwanta idanuwansa na rufe yana jiran barin duniyar kafin ta dawo da idanuwanta Akan Ayanah dake kallanta cikin yanayin da suka fi buqatan mutuwan Akan rayuwar Zuhrah ce ta iya bude baki da tsananin kuka me ratsa zuciya tace ‘Asamah mun zabi bin iyayenmu dan Allah karki zabi barin mu kema sbd kece wadda a yanzu muke kallan zaki zame mana ido a wannan rayuwar da muke makafi bamusan komaiba dan haka munfi tsananin buqatan komawa ga mahaliccinmu kaman iyayenmu…… Ayanah data kasa magana sbd tsananin shidewan datake sbd tsananin tashin hankali da kukan da hawaye basa fita a cikin dare daya da wuni hawayenta sun kafe kallan Asaman takeyi tana girgiza kai dukkanin jikinta na rawar da bata hayyaci bace. Rintse idanuwa Asamah tayi ahankali tana bude su Akan su duka tace ‘Allah zai zama gatanku, Allah zai Baku kariya, Allah zai kawo ido da haske a rayuwarku kudai ku jajirce karku rabu duk tsanani ku kasance bangon juna’ Maida kallanta tayi kan kusran ta basa amsarsa da cewa ‘Na zabi rayuwansu Akan tawa a cika mun damar da aka ban ta hanyar barinsu da rayuwansu harsai lokacin da ubangijin daya halitta musu ita zai karba da kansa… Ayanah ce tayi saurin yunqurowa da rarrafe mai sauri ga Asaman tana miqa hannu zata riqeta sbd suna tsananin buqatanta a yanzu…….. Jinin daya fesu a fuskanta da hannunta data miqa ne yawa na Asamah ya sakata sanqamewa a gurin tana dauke wuta hannunata na kakkarwa me tsanani. Wuqar da kawai aka fizge fatar wuyan tareda jijiyan Asamah kaman wucewan iska Wanda ya saka jinin bartsi sosai ta kalla a hannun Wanda yayi aikin batareda bata lokacin su ba sbd zabinta ne. Wurgar da Abaas sukai a gaban yan uwansa da gawar Asamah dake gangaro da jini, Mutuwan Zaune dukkaninsu sukai tareda dauke wuta sbd babu Wanda a jikinsu jinin bai bartsanwa ba, Abaas daya kasa matsawa yana kwance a inda suka jehosa kaman mataciyar dabba rufe idanuwansa yayi hawaye na zubowa idanuwansa yana kasa motsawa. Babu Wanda yace musu komai haka suka juya suka bar gurin shugaban cikinsu ma dago murya yace ‘Kusra bata tada Alkawari idan tayi dan haka ku tafi an cika mata burinta ko bata raye amma wannan damar itace ta cika Alkawari idan mun sake haduwa daku kun zamo namu’ Har suka bace wa gurin babu Wanda ya motsa a cikinsu Ayanah sbd babu wanda ya dawo hayyacinsa, Sakinah dake Bayan Ayanah motsawa tayi ahankali tareda qarasowa gaban gawar Asamah ta saka hannunta yana rawa sosai ta shafe idanuwanta suka rufe tana fasa kuka mai tsima zuciya itama. A lokacinne Zuhrah ta fasa kukan itama me karfin gaske tana fadawa jikin Ayanah. Nurat da bata hayyacinta miqewa tayi da sauri a zare tana bin hanyar daji kafafunta na hardewa tana qwala kiran sunan Abaansu. Ganin tana Neman nisa ne ya saka Abaas miqewa da gudu yana kamota ya rungume yana kiran sunanta da karfi da fashewa da sabon kuka. A lokacin ne Ayanah da Zuhrah suka taso suma suna riqeta tana kwacewa cikin wani irin ihu na gushewan hankali Wanda ya saka yan uwanta suna fasa sabon kuka me taba zuciya dukkaninsu suna qara riqeta sbd zaucewa takeyi. Sakinah ma kukan take fasawa itama tana rungume dukansu. Ihun Nurat ke fasawa tana fizge fizge tana yakushin kanta da karfi tana kwala kiran Abaa dajin na amsawa sosai. Qin Sakinta sukai suna sake saka karfinsu su duka suna riqeta sosai kukansu na qaruwa. Sun jima a cikin wannan sabon tashin hankalin kafin Nurat din ta zube qasa suma suka zube gabaki dayansu har lokacin basu iya Sakinta ba sbd kada ta gudu. Shiru sukai sai ajiyan zuciyar kukansu dake sauka akai akai na tsawon lokaci shima kafin suka miqe hannun Zuhrah na riqe dana Nurat din suka bar gurin. Gabas suka kalla suka sake miqa suna kutsawa hanya batareda sunsan inda suka dosa ba. Yunwa da azaba ce kawai a cike da rayuwarsu a lokacin tareda mafi girman baqin ciki da qunci, Wuni suka sake shudewa suna zagayen dajin sun rasa hanyar fita bare komawa ANJOM duk da sunsan garin ya zama na kusra yanzu. Cikin dare sosai suka sake samun wani guri suka zauna tareda

Table of Contents

Chapters

106 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});