Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 94

Chapter 94

Alkawarin Allah Book 1 Complete Hausa Novel 1,308 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

an murda qofar dakin,wanda hakan yaja hankalinta zuwa kallon qofar,yana shigowa idanunshi cikin nata,mamaki ya sanyata miqewa ta zauna sosai saman gadon,tama mance da irin dinkin da yake jikinta,idanunta fal da alamun tambaya,jingina yayi daura da qofar ya goye hannayensa a qirji yana qare mata kallo,sai a sannan ta tuna da rigar jikinta,tabi kanta da kanta da kallo saita daga kai tana hade fuskarta tsaf,miqewa tayi ta nufi wardrobe dinta ta soma lalubar mayafi,yana tsaye still yana kallonta har yanzu baice komai ba,harta gama yafa mayafin ta dawo gefan gadonta ta zauna "Ki shirya gobe qarfe tara na safe xamu fita tare xan saukeki gida" fuska a tattare ta bishi fa kallo har ya fice,saita ja qaramin tsaki ta koma ta kwanta tana tunanin ina zai kaita?,kuma me zata fita tayi. Tara saura tana tsaka da shirinta wayarta ta shiga ruri,ta qarasa inda take aje ta daga tana duba mai kiran,anty usaina ta gani,a ladabce ta daga suka gaisa sannan tace "Na kasa samun layin anwar,inata kira busy,taimaka don Allah ki gaya masa idan zai fito ya fito da wadan nan takardun" "Toh anty" ta amsa mata a ladabce tana aje wayar,qarasa shiryawa tayi sannan ta fito ta haura saman nashi,tana shiga yana aje wayar gami da miqewa ya tura qofar toilet ya shige,bata masa magana ba don qyashin hakan takeji,saita barshi ta samu saman kujerar mudubi inda ya tashi ta zauna tana dakon fitowarsa. Wayar daya aje saman mudubi wanda take dab da ita ta dauki ruri,idanunta kai kan me kiran,nafisa ta gani,ta riga data haddace sunan,saita dauke kai saidai hankalinta ya kasa daukuwa daga kai,tana jin sautin ringing din har cikin kanta harta katse,aka sake kira ta sake katsewa,ba jima wani kira yasake shigowa,batasan sanda taja wani mugun tsaki ba ta finciko wayar ta kasheta gaba daya ta dangwarar da ita awajen,tana tuna sanda ta shigo waya taga ya gama,wala'alla ma shi yasa anty usaina ta gaza samunshi wayama yake kenan "Ina ruwana da wayarshi" ta gayawa kanta tana sake tsuke fuska ita kadai,daidai lokacin daya fito daga bandakin jikinsa jiqe da lema,da alama wanka yayi,fuskarta a dinke tsaf cikin kaushi tace dashi tana miqewa "Anty tace karka manta ka fito da takardun nan" daga haka tayi gaba,binta yayi da kallo,tana gab da ficewa yasha gabanta,ya murza key ya rufe qofar,saita danja da baya tana dubanshi,kuka takeson tayi amma batasonyi a gabansa,don tasha alwashin ta daina yi din yana gani yana jin dadi "Ka budemin na fita na qarasa shiryawa" ta fada cikin sanyi,wanda ba haka taso,taso tayi maganar ne cikin kaushi da zafi,saiya kada kai yana duban idanunta wansa hakan yaso mata tasiri,saita zare nata idon gami da kauda kanta wani sashen daban. tokare _Dadai zakuyi haquri harmu cimma manufar labarin,don kowanne labari yana da manufar da akeso a cimma,idan kuma kunason shortcut shikenan_🤷🏽‍♀️ Mai yiwuwa gobe kujini shuru,idan kuma Allah ya bada dama to. *karku manta kuyi wekend dinku da tashar SAUTIN HIKIMA dake youtube,ku saurari littafanmu ba tare da kunsha wahalar karatu ba kuna daga kwance*💃🏻 *Asha weekend lafiya*🤝🏽 *Alqawarin Allah* 45 "Zuwa yanzu ya kamata ki fara koyan wasu abubuwan,saboda karta shigo ta rainaki" ya fada yana son dawo da salon tsokanarshi. Wani kallo ta watsa masa da idanunta sanda yake komawa zuwa bakin mudubi,wani abu ya tokare mata wuya "Wace zata shigo din?,bani ya kamata ka gayawa wannan maganar ba,don ni ba kallon mijina nake maka ba" saiya waiwayo yana zare idanu "Da gaske?,lallai kinci tuwo da yawa,wait....waima kallon me kike min?" Harara ta sake watsa masa ganin yanason maida abun shirme kamar yadda ya saba,baisan yadda ranta ke tafasa ba "Oho,koma meye ba damuwarka bane,ka budemin qofa kawai na wuce,abu daya na sani shine,daga kai har ita kada wanda ya sake yashiga hurumina" baki ya kama yana kallonta,sau tari yakanso yaga tana rashin kunya,sai dan qaramin bakinta yayita burgeshi,don a tsahon xamansu na baya bai taba ganin tana tsiwa ba sai yanzu "Idan kuma akaqi fa?" "Raine zai baci" ta amsashi kai tsaye,qaramar dariya ya bushe da ita "Kinga...kawai ki fito kice kishi ne yake damunki ko?,to kiyi haquri,na miki laifi" sake hararshi tayi,tanajin kaman ta makeshi ko zataji sauqi "Ni na gaya maka duka wannan na damuwata bace,bama kallon miji nake maka ba bare nayi kishinka,ka budemin na fice kawai" "Aiko kin makaro,dakin yadda kawai da hakan yanzu zan bude miki qofar salin alin,amma tunda kika musa to sai na gama shiryawa tsaf sannan zan bude ki mu sauka tare" tanaji tana gani yayi funfurus yahau shiryawa a gabanta ko kunya baiji,haka ta zauna ta kallo bango harya gama ya budeta. Har daki yabita ta gama daukar abinda zata dauka kaman wani body guard,tana kumburi tana komai amma bai kula ba ta fito suka fita. Gidansu ya soma kaita,ta cika da mamaki sanda suka isa taga ya sake cikinsu sosai kaman yadda suka saba a baya,sai taga kamar ma sunfi zumudin zuwanshi akan nata,hira suke abinsu da umma kamar danta,baqinciki yasa ta kasa sakewa ma bare tayi hira,basu bar gidan ba sai qarfe daya da rabi na rana bayan yaje masallacin layinsu yayi sallah sannan yace ta taso,kaman ba zata tashin ba,don ita sam lokacin bai isheta ba,amma yadda umma ke jifanta da harara yasa dole ta miqe tabi bayanshi. Daga nan gidan anty zubaida sukayi,can dinma haka suka gaisa da antyn cike da sabo,sannan ya yiwa anty zubaidan sallama kan zaije anjima zai dawo ya dauki shahidan. Kusan fiye da rabin hirarsu ya ranar jirwaye me kama da wanka anty zubaidan ta dinga mata da gugar zana,ta kuma fahimceta sarai saidai tayi kaman bata gane ba,duka dai kan zamantakewarsu ne da nafisa dake shirin shigowa gidan,wanda duka ita tana ganin wannan ba matsalarta bace,dubanta anty zubaidan tayi sanda suke tsaye cikin kitchen tana tayata yanka cabbage zata hada coleslow "Ranar yaushe zaki yinin naki ne banji kince komai ba,yaufa alhamis,lahadi kuma daurin aure" baki ta tabe bayan ta dubi anty zubaidan "Ko nawa bikinma ban tsaya wani tsara wuni ba bare bikin wasu" ta fadi cikin qunquni,murmushi ya subucewa anty zubaida saita kada kai,lallai yaro yaro ne,ga zallar kishi na bayyana kan fuskarta da kalamanta amma taqi yarda da cewa kishi take "Wancan daban wannan daban,bakyace ba zakiyi ba kodon idon mutane,kuma kema zaki buqaci wadanda zasu tayaki karbar amarya" "Waini zan karbeta ma?" Ta fada tana nuna kanta da wuqar hannunta "Eh mana,haka akeyi ai" saita jijjiga kai tana ci gaba da yankanta "Lalllai kam" anty zubaida ta fuskanci zancan ciwo yake mata ba tare datasan da hakan ba,sai kawai ta shareta suka shiga wata maganar daban. Bayan sunyi sallar la'asar anty zubaidan tace tazo ta rakata kitso,ba musu ya dauki mayafinta suka fita a motarta,huda tace zata bisu antyn yace sam tayi zamanta,suna tafe a motar antyn na nuwa shahidan wasu robobi masu dauke da gumba ta kwakwa da dabino,wanda idan kanaci zaka xaci an hada kayan qwalamane kawai sai aiki a jiki,wadda takan jima jikin mace bata bar jikinta ba,ta dinga mata dabara kanta dandana mata taji,haka ta dinga ci suna hira,antyn tana tuqi a hankali har sai dataci da yawa,ta sake nuna mata wata roba wadda ke cike da tsumi tace "Sha kiji wannan fa"dan bata fuska shahidan tayi "Wainikam anty wadan nan ba irin kayan

Table of Contents

Chapters

96 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});