Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 59

Chapter 59

Alkawarin Allah Book 1 Complete Hausa Novel 1,282 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

saiyaji a jikinsa da zuciyarsa yadda ya janyo mata bacin rai tsakar rana ba tare data shiryawa hakan ba. ***** ****** ****** ***** Tunda ta tashi washegarin take kwance abinta kamar ruwa taqi yin komai,saidai daga nan ta koma can,hasina tayi tayi ta tashi tayi wani abun ko taji qwarin jikinta amma ta qeqashe qasa,ko kallo bata ishi daada ba sangar gabanta kawai take,tana daga kwancen tana kallon daada,yadda ta cika fridge dinta da fura da nono mai kyau,lemuka da kuma ruwa,tasa hasina tayi total na kayan fulawa aka siyo komai hasina tayi dan dai dai aka adana komai,baki ta tabe ta dauke kai bacin rai na cinta sanda daada ta fito da sabuwar daddumarta da kawu ummaru ya bata sanda ya dawo daga umara ya fesheta da turare ta baiwa hasina taje ta shimfida a dakin soro. Saida komai ya kammala hasina ta isketa kwance cikin kujera tana saqa da warwara ta zauna gefanta "Ya kamata ki tashi ko ruwa ko watsa kyaji dadin jikinki?" Idanunta da suka sake girma saboda kwana biyu data yi bata saka musu kwalli ba ta watsawa hasina cikin salon tambaya "Me kikeson cewa?,kice kawai na tashi na yi masa kwalliya saboda zaizo,mutuncina ya qara zuba a idanunsa ko?" Murmushi hasina ta saki tana kada kai "Niba haka nake nufi ba,kawai nasan yadda kikeson wanka wuni guda kuma ace tun safe ga azahar ta shiga baki watsa ruwa ba bare kici wani abun ai babu dadi,a qalla kodon tsaftar jikinki ko?" Saita maida kanta ta kwantar gami da rufe ido sannan ta amsa mata "Share kawai" dubanta hasinan tayi na wasu mintunan sannan ta miqe tana cewa "Allah ya kyauta,ya kamata dai ki sawa ranki salama,tunda kinsan cewa aikin gama ya gama,kada madai azo gaba kina jin kunya yazo kiga ya miki ki kamu da sonshi,kinsan wallahi daada ba raga miki zatayi ba"da sauri ta sake bude idon ta dubi hasina "So,bakisan nayi bikin binneshi ba?" Dariya ta qwacewa hasina ta kama baki tana kallonta "Shi kuma wannan da kika kawo fa?,mutunci kuke kenan?" "Nuradden?..inason in rama halaccin da yayi minne shekaru kusan hudu" "Tabdi,kice gwara da Allah yasa daada ta zaba miki miji,ashema ba soyayya kuke ba kenan" kofin dake gefanta shahida ta wafto ta jefi hasina dashi Allah yasa ta kauce bai sameta ba,har ga Allah taso ta sametan don bata da bakinma ce mata ta fita saboda wani abu dake takore da wuyanta "Na rantse da Allah na tashi hasina saidai daada ta fiddaki daga gidan nan" cikin dariya ta fice tana cewa "A'ah,a'ah,bani nakar zomon ba,ratayarma kuma ba'a bani ba". Qarfe uku na rana da 'yan mintina daada ta shigo ta sameta "Tashi kiyi wanka ko yanzu nasa akaimin ke bandaki na sabeki" ta furta tana nuna da gaske take,saida ta gama taurin kanta ganin da gaske daadan take sannan ta shiga bandaki tayi wankan. Sanda ta fito mai kawai ta shafa sai turarenta oily data gogawa fatarta,tasaka wasu riga da skert na atamfa ta zura dogon hijabinta daya sauka har saman qafafunta ta soma da nafila kafin ta gabatar da farillar sallar la'asar. sanda ta kammala saman abun sallar ta zauna tana jan hasbunallahu wani'imal wakil,saboda faduwar da gabanta yaketa yi wanda batasan dalili ba. 👑 https://youtu.be/H7M7h6l6wNM *xafafa biyar na kudi ne,idan kika gani don girman Allah karki sharing,ga mai buqatar siya zai tuntubi wadan nan numbers din* 07067124863 *ko kuma* 09032345899 *Alqawarin Allah* 3️⃣0️⃣ "Kana nufin kaine mutumin daya kawo sadakina da mudin airena ba tare da sani ko yardata ba?" Ta furta wani bala'i na cinta,maimakon ya bata amsa da baki saiya daga mata dukka girarsa biyun yana dubanta kai tsaye ya kafeta da idanunshi,wani tashin hankali taji ya rufto mata irin wanda bata taba jin irinsa ba tunda maganar aurenta ta bullo,tashin hankali da ba'a saka masa rana,ko zata yarda da kowa ba zata yarda da anwar ba,ko zata amince da auren kowa ba zata taba amincewa da auren anwar ba koda su biyu kadai suka rage a duniyar,murmushin takaici ta saki wanda qasan zuciyarta ji take kaman zata fashe "Kaima kasan ka dauko abinda bazai taba yiwuwa ba har abada,tamkar wanda ya mutu ya dawo ne,kai bakaji kunya ba anwar?,kana tunanin akwai abinda yayi saura?,kana tsammani akwai wani sauran abinda ya rage tsakanina dakai?,to bari kaji na gaya maka,ba zaka taba samun yardata ba,ba zaka sake samun soyayyata ba,har abada aure tsakanina dakai,har abada...." Qawataccen murmushi ya saki,da alamun kwanciyar hankali kwance kan fuskarshi,sai daya sauke qafarsa ya sauya jinginar da daya sannan ya rungume hannunsa daya dayan kuma yana shafar sajensa idanunshi a kanta,fara'ar fuskarshi ta bace bata "Hajiya shahida....dukka tunaninki bai baki dai dai ba,baije inda ya kamata yaje ba" sauke qafarsa yayi ya soma takowa inda take tsaye,sai daya rage tazarar dake tsakaninsu sosai sannan ya tsaya ya soke hannayensa cikin aljihun rigarsa "Kina tunani ko tsammanin soyayya ce tasa na nemi aurenki?,ko kina tunanin neman yardarki nake kafin na aureki?"sai ya sake takowa gab da ita kamar zai hadeta da jikinsa,ya nunata da yatsa "Zan aureki don na nunawa wancan wawan cewa nidin na girmi qaramin dalili babban dalili ne ni,sannan nayi isar da zan yanke guntuwar soyayyar da yake taqama da ita,soyayyar da bai iyata ba,bai gama saninta bama bare ya iya,baisan kanta ba baisan mece ita ba!" Ya qarasa fada yana dan daga muryarsa gami da nuna qofa da yatsa kai kace nuradden ne ke tsaye a wajen,saiya sauke hannun nashi yana maidashi aljihunsa kana yaja baya kadan har yanzu bai dauke idonsa daga kanta ba "Yana tunanin ya sanki?,yana tunanin yafi kowa saninki koya riga kowa saninki?,ya gayamin magana yayi tunanin yaci bulus?,inaso yaji ciwo ya kuma ci gaba da jin ciwo a ransa duk sa'a daya da zata wuce da tunanin wani mai suna anwar ya haramta masa auren wadda yake iqirarin yanaso,wadda yake iqirarin ba wanda ya isa ya shiga tsakaninsu" yana kaiwa nan ya juya mata baya,yana jin kamar ana yankar zuciyarsa "Baki cancanci na qyaleki kici gashin kanki ba,baki cancanci na barki kiyi zabin da kikaga dama ba,bayan kin cutar da zuciyar da bata cancanci sakamakon da kika bata ba,kin bata rayuwar da alokacin ya kamata ki tattaleta kodon iyaye da qannenki,kin bada jikinki ga wani har yayi ajiya a wajen daba muhallin......" Saiya kasa qarasawa saboda wani dunqulallen abu daya tokare masa maqoshi,ya dinga jin wani turari tun daga zuciyarsa zuwa fuskarsa,bakinsa yaji ya dauki zafi ya fitar da iska zazzafa,yana jin wani irin ciwo da qunci duk lokacin daya tuna da lokacin da kuma abinda ya faru,hotunan dake wajensa da ganin da yayi kaya ido da ido sun kasa gogewa daga qwaqwalwa da zuciyarsa,yana jin wani irin ciwo mara misaltuwa,tabbas da yana da iko daya dawo da lokacin ya goge duk wani abu daya faru ko xai samawa zuciyarsa salama. Tuni hawaye ya soma wanke mata fuska tana tuna lokacin da abinda ya faru alokacin daya bayan daya,sai a sannan ta dinga tuna kaman ta ganshi,kaman a gabanshi aka sauketa,hakan na nufin ya ganta cikin maye?,ya ganta a lokacin da jini kebin qafafunta?,yaga sanda aka cillo mata pant dinta da kwalabenta?,amma me yasa ya zama mai qaramin tsinkaye?,mai yasa ya zama mai gajeran nazari?,me yasa ya yanke mata wannan danyen hukunci farat

Table of Contents

Chapters

96 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});