Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 31

Chapter 31

Alkawarin Allah Book 1 Complete Hausa Novel 1,318 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

adam domin gusar da baqinciki bacin rai ko kuma damuwa bashi da wani tasiri a gareshi,baya haifarwa da bawa komai face sake sanyashi cikin damuwar,baya yaye damuwa ta har abada face ya sake sanyaka cikin wasu sabbin matsalolin,ya haifar maka da ciwuka masu kai d'an adam ga kushewa,Kana daukan cuta ne kana laftawa kanka,kana kashe kanka da kanka,Allah S W T da kansa yace kada ku kashe kawunanku,shan abun maye ba komai bane face kashe kai,don baka da maraba da mutumin daya dauki makami ya dabawa kansa,domin kuwa shaye shaye ba cutar da baya haifarwa,lalacewar qoda,lalacewar hanta,ciwon cancer,ciwon zuciya,yana nakasta hunhu,yana kuma lalata qwaqwalwa wanda hakan yake jagoranci zuwa ga haukacewa,dukka daya daga cikin wannan cututtuka idan aka bar mutum dasu sun isheshi azabar nan duniya,sun ishi mai hankali gujewa abun maye"ajiyar zuciya anty zubaida ta saki sannan ta dora "A duniyance shaye shaye bai haifar maka da komai sai zubewar qima da mutunci,mummunar dabi'a ce dako wanda yake yinta yake boyewa,kuma baiso a sani,dabi'ace dakan gusar da imani da hasken fuska,dabi'ace dake barin tabo cikin rayuwar wanda ya taba aikatata,sannan ba'a sanyaka cikin sahun managarta mutane ko mutane masu dattako har abada,saboda kowa kallon mahaukaci yake maka,sannan a addinance manzan rahama yace dukkan wani abu da zai saka maye haramunne,musulunci yafimu sanin cewa kayan maye abubuwane masu cutarwa ga lafiyarmu,shi kuma ko yaushe tattalin lafiyarmu yake,sannan addini ne dake kare mutunci da martabar dan adam,bambancin mutum da dabba hankali,kinsha abinda zai gusar da hankalin me sunanki kenan a wannan lokacin?,dalili kenan daya sanya aka haramta mana su,duk sanda kake cikin maye babu kunya tattare dakai,hakan na nufin ba alkhairi a tare dakai kenan,saboda ma'aiki ya gaya mana duk inda kaga kunya akwai alkhairi a wajen,sanda kuma babu kunya tare dakai zaka iya aikata dukkan komai ciki kuwa harda kisan kai!,tunda kike sha din damuwarki ta taba tafiya gaba daya?" Kai shahida ta girgaza,don da zarar ta farka dukkan wata damuwa take dawo mata sabuwa fil,harma tafi ta dazun "Zaki iya tuna sau nawa kikayi loosing sallah saboda tazo ta riskeki kina cikin bacci sanadin abinda kika sha?"shuru shahidan tayi tana tunani hawaye masu dumi nabin fuskarta har cikin kunnenta,kome take komai runtsi sallah bata taba wuceta ba sai a wannan karon,sai data shiga wannan mugunyar dabi'ar "Kina tunanin hujjace da zaki gayawa Allah ranar gobe qiyama na dalilin jinkirta sallahrki?" Ta jefo mata tambayar data sanya shahida fidda sabuwar qwalla,dana sani da nadama mara misaltuwa na sake shigarta,kaico da rayuwarta da haduwarta da fiddausi "Kina da yaqinin sanda kika farka kika ramata Allah zai amsa ya saka miki a mizanin ayyukanki wajen sallahrki na lokacin bazai tashi blank ba?,bayan kina baccin sabo ne bana ibada ba?" Sabon kuka shahidan ta sake saki,tsoron Allah na sake kamata,tana jin kaman yanzu Allah zai amshi rayuwarta,me ta tanada?,wacce amsa zata bayar?. "Allah yana karban tuban bayinsa ne matuqar ran bawa baizo gargara ba,sannan kuma rana bata fito daga mafadarta ba,bai halatta bawa ya jinkirta tuba kan wani aikin sabo da yake ba,yace har sai Allah ya shiryeshi,don haka yana daga cikin alamar 'yanwuta,kuma alamace dake nuna bawa ya tabe,sannan alamace ta toshewar basira,anaso koda yaushe bawa ya dinga gaggauta tuba saboda baisan randa ajalinsa zai riskeshi ba" "Astagfirullah...astagfirullah" shahida ta dinga maimaitawa a fili har na tsahon wani lokaci,sai data fuskanci ta samu nutsuwa sannnan ta dagota suna kallon juna "Shahida...maganar anwar....." wani abu mai ciwo taji ya tokareta,abinda yayi mata ya dinga yawo cikin idanunta kamar tariyar film,da sauri ta katsi antyn "Anty...don Allah ki daina kiramin sunanshi....don Allah anty ki dainamin maganarsa,yanzu bashi a gabana,yadda ya buqaci na barshi na barshi har abada...yadda ya nuna bai buqatata saboda wani kuskure dana aikata nima bana buqatarsa har abada" murmushi anty zubaida tayi tana karantar yanayinta da yadda maganar ke fita daga zuciyarta zuwa harshenta,kai ta girgiza tasan cewa wani bacin raine dake qonata tun daga cikin jiki zuwa zuciyarta,kowa ya shaida irin qauna da soyayya dake tsakanin shahida da anwar,koda baka sansu ba labarinsu ba shakka ya iskeka,bata da tabbaci ko yaqinin kan abunda shahidan ke furtawa saboda ta riga ta sani cewa soyayya ba qarya bace,ba qaramin dalili ne yake da qarfi da isar da zai karyata ba,karyawa ta har abada,karayar da ba zata doru ba "Duk wannan lafazin shahida ban buqatar jinsa daga bakinki,ba'a ciwa soyayya alwashi kuma ba'a cika mata baki....kiyi addu'a kawai a yanzun,ki tattara hankalinki waje guda,ki karbi qaddararki,kiyi moving forward,stop worrying about what u have to loose,and start focusing on what u have to gain,har yanzu yarinyace ke,shekarunki nawa?,me kika soma gani cikin rayuwa?,akwai abubuwa daya kamata ace kinyi achieving a rayuwarki,karki bari wani abu guda daya ya tsaidaki waje guda,ya ruguza dukkan wani kyakkyawan tanadi daya kamata kiwa rayuwarki,wannan abun daya faru ba komai bane cikin rayuwarki,daya daga cikin challanges kenan na rayuwa,ki godewa Allah kina da chance,kina da dama,kamar ya baki wata dama ne naci gaba da gina sabuwar duka rayuwar da kikaso kikaga dama,just choose tobe strong rather than letting it drown you" wadan nan sune ire iren kalaman da anty zubaida ta dinga amfani dasu tsahon shekara biyar don dawo da rayuwar shahida cikin nutsuwarta. Cikin qaramin lokaci taji anwar din ya wanke mata a rai tas,ya sire mata,ya fice mata daga ruhinta,taji zata iya rayuwa babu shi,taji abune mai sauqi hakan,saidai baizo mata da sauqi ba yadda ta tsammata,ta share darare da yawa bata samu bacci ba,ta ga wuninnika da darare masu tsaho da tsauri cikin rayuwarta a wannan lokaci,ta cika bangon dakinta da shafukan littafanta ta kalaman qarfafa kai da qarfafa gwiwa akaran kanta,ta siya littafi tayi rubutu mai tsaho da yawa kan rayuwarta har kawo bigiren da yau take kai,ta tattara duk wani abu da zai iya tuna mata da anwar ta ajesu waje daya,ta shiga tsara yadda rayuwarta zata kasance nan gaba,tun saga lokacin ko masoya ta gani sai taji tana tausayinsu,musamman mace idan taga ta zura jiki da yawa. Bayan umma ta fita takaba uncle hisham shi ya karbi ragamar daidaita musu duka al'amuran gidan,sannan suka yanke shawara dashi shahida zata koma hannun anty zubaidan,tunda har yanzu bata gama daidaita ba,saidai cikin kaso dari an samu sauyi na kaso shida,rabata da unguwar da duk wani tsohon memory dinta zai sake taimakawa wajen saita tunaninta,da wannan suka dauke shahidan ta koma wajensu. Makarantu daban daban anty zubaida ta sakata wanda zata qaru ta fanni da dama,wasu na koyon harshen larabci wani na koyon turanci bawai don bata iya ba,a'ah saidon ta maidata busy sosai wanda hakan zai sanya bata da lokacin zama ma ta tuna wani abu mara dadi daya faru da ita a baya,tayi hakanne kuma kafin wata shekarar ta zagayo su nema nata admission saboda wannan shekarar ta qwace mata. Rayuwarta ta soma samun sauye sauye,kullum kwanan duniya saitayi kukan dabi'ar shaye shaye data ta taba tsintar kanta a ciki,kullum sai tayi nadamar sanin fiddausi a rayuwarta,sai tayi nadamar sakin jiki ga duk qawar data kutso rayuwarki sama taka,abune mak wahala da idan ka sake ka jefa kanka da wuya ya fice daga rayuwarka salin alin ba tare daya haifar maka da nadama da danasani ba,bai kuma bar maka qatoton tabo ko baqin fenti a rayuwarka ba,ta godewa Allah da yayi gaggawar fiddata tun batayi

Table of Contents

Chapters

96 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});