Chapter 69
Chapter 69
ratsashi,ita ta soma janye idanunta,ranta a hade tsaf ta taka zuwa ciki tana duban faruq,saiya miqe,anwar yace "Zan nemeka kafin na wuce kada kayi nisa" "To yaya" ya fada yana ficewa,sai da taga fitarsa sannan ta zauna hannun kujerar dake a dab da bakin qofar fita,tanason tsareshi da ido donta karanci me ya kawoshi amma batasan me yasa takejin rashin qwarin gwiwa ba,ta maida idanunta kan tafin hannunta tana murzawa ba tare data ce masa uffan ba,hakan ya bashi damar kafeta da ido,ya soma kallonta tun daga yatsan qafarta zuwa saman kanta,yana jin wasu tagwayen abubuwa na fada cikin zuciyarsa,daya nason yaqar daya gami da rinjayarsa,inda daga qarshe dayan yayi galaba,saiya runtse idanunsa yabar kallonta saboda wani bacin rai dakeson shaqeshi,kullum kwanan duniya yana son sasautawa kanshi,yana son ya daina ganin baqinta da baqin abinda ta aikata,yana son abinda idanunsa suka gane masa da hotunan daya gani su bace daga idanunsa ko zai samu salama da rangwame amma hakan ya faskara,sai komai yayi kaman zai goge saiya sake dawowa sabo fil a ransa. Walwalar da yake jin kaman zata samu a ruhinsa ta dusashe,sauran faragar fuskarsa ta bace bat. Zaman kurame ne yaci gaba da wanzuwa tsakaninsu harna tsahon wasu mintuna,sai daya gama zamanshi don kanshi sannan ya miqe,cikin wani taku ya isa dab da ita ya tsaya akanta,kana ya ranqwafa gefanta har tana iya jiyo qamshin ya aje envalope din hannunshi,ba tare daya dago ba yace mata "Baki iya gaisuwa ba saikace a gidan mashaya inda kowa yake ogan kanshi,karki tsammaci xaki gidana da wannan dabi'ar ki tsira,ga saqon da muhsin ya kawo miki daxu kika maidashi nina dawo dashi,idan kin isa karkiyi amfani dashi yadda ya dace kiga yadda zata kaya mana nidake,tunda na fahimci cikin halayen da kika koyo kala daban daban harda taurin kai ko?,good....inason wannan sabon halin naki,idan kin tashi gayyatarki karki sake ki kwaso min tarkacen 'yan maye,ko tarkacen qazaman tsaffin samarinki" daga haka ya dago yana shirin wucewa zuciyarta taje iya wuya,ta kasa daurewa "Idan ba haka bafa?,me zakayi?" Ta fada a tsiwace cikin fushi da fusata,saiya sake dawowa gabanta ya tsaya,ya dubeta na wasu mintuna sannan ya saki murmushi "Ki aikata din sai kiga sakamakon" miqewa tsaye tana masa kallon tara saura kwata sannan tace dashi cikin salo na masifa dake cin zuciyarta "Baka isa ka sakani abinda banyi niyya ba,baka isa komai ba idan ma kana tunin ka isa" murmushi ya sake saki wannan karon mai sauti,yadan buga qafarsa sannan yace "Ko a haka aka tsaya ai inga irin tawa isar ko?,hukuncin da zan miki ba isata kawai zai nuna miki ba,izzar aure da izzar anwar namiji" "Namiji shine zai tsaya takara da abokan adawarshi ya kuma samu nasara,ba wanda zai wafta koya biyo ta bayan gida ba,koya taka wani tsani don kaiwa wannan bigiren,ka daina batawa kanka lokaci wajen kiran kanka da namiji,ba namiji bane kai saidai mata maza" idanunsa ya qura mata qir sanda take maganar cikin dakiya da rashin nuna tsoro,hakanan bilhaqqi da gaske,ganin takai aya saiya soma takowa inda take tsaye,ta tsaya cak don ganin iya gudun ruwanshi,saidai harya iso gab da ita bai daina takowa ba,hakan na nufin zai hade gap din dake tsakaninsu kenan,don haka ta soma ja baya ga zatonta zai tsaya amma ina,bai barta ba sai daya tabbatar ya hada bayanta da bango,qafarshi dake saye da takalmi saman tata qafar wanda yana iya jin zafi zafi na tudun takalminsa daya take mata qafa,kusancin dake tsakaninsu yayi yawa,tana iya ganin fuskarsa tarwai wadda kyau ya cikata gamida iya gyara,idanunsa sai suke juye mata irin na anwar dinta na wancan lokacin sak,janye qwayar idanunta tayi gabanta na bugawa da sauri da sauri,tsoro da fargabar me zaiyi mata na shigarta,saitaga ya daga hannu kaman yana shirin marinta,ta runtse idonta da sauri tana wassafa me zata masa ita bayan ya gama marin nata,ji tayi yaja baya da sauri cikin kaushi yace "Sai na saki kinyi nadamar lafazinki,tsautsayi kuma yasa bakiyi yadda nace miki ba" daga haka ya juya da sauri sauri ya fice daga dakin,cikin hanzari ta daga murya "Idan ka isa ka tsaya mana ka dakenin kaga yadda akeyinta" gab da zai fice ya waiwayo yace "Aiba a gidan syrup muke ba" kalmar ta tsaya tana fassarawa,take wani abu ya cushe mata maqoshi,cikin qanqanin lokaci hawaye ya ballewa idanunta,tana jin zafi a zuciyarta duk sanda yayi wani lafazi dazai iya tuna mata da abinda ta aikata a baya,sulalewa tayi ta zauna a wajen,ba shakka ba'a bari a kwashe duka,shaye shaye ashe wani tabone da tambarinsa bai barin jikin maishi?,koda kowa ya manta ba'a rasa burbushi,ta jima a wajen tana jin ciwo kala kala kafin ta miqe ta fice daga dakin,ko kallo envalope din basu isheta ba bare ta dauka. A falo anty zubaida tace ta tsaya ta duba dinkunanta na biki wanda ita batasan ankai bama,don ko kayan har yau bata kalla ba bare ta gane me takeso a ciki har tayi tunanin kaiwa dinki?,bata cikin yanayin da zata iya zama cikinsu saboda haka tabawa anty zubaidan uzurin kanta na ciwo zata duba zuwa safiya da haka ta wuce dakinta. Washegari sun fito da anty zubaida zata koma gidan gyaran jiki tanata kumbure kumburenta da mita cikin ranta na yadda aka takura mata ba gaira babu dalili faruq dake sharar dakin da uncle hisham ya sakashi sabida zaiyi baqi ya fito da envalope din yana miqawa anty zubaida "Anty wannan a dakin na gansu,kaman na anty shahida ne don jiya na gansu a hannun uncle anwar" hanu tasa ta karba sannan ta waiwaya tana duban shahidan "Me yasa kika barsu a dakin?,abinda kikayi dai dai kenan?" Saita langabe kai,ita abun goma da ashirin,komai tayi batayi dai dai ba,saita saka hannu kawai ta amsa suka wuce,suna shiga mota ta kasa daurewa ta saki kuka tana kife fuskarta saman cinyarta,anty zubaida batace komai ba saidai ta dora hannunta saman bayan shahidan,saida tayi kukan na wani lokaci sannan anty zubaida tace mata.......*Alqawarin Allah* 3️⃣4️⃣ "Abubuwa da yawa da mukeso muke qwallafa rai a garesu ba alkhairi bane ga bawa,kiyi qoqarin rage wannan kaifin qiyayyar kamar yadda annabi yayi umarni saboda kada ta juye miki zuwa soyayya mai zafi daga baya,kiyita addu'a Allah yasa abinda zai faru dake ya zama shine mafi akhairi a rayuwarki duniyarki da lahirarki" da ire iren wannan nasihar suka isa wajen gyaran jikin. Anty zubaidan ita ta karbi envalope din ta bude taga abunda ke ciki,saita amsa ta aje tana jiran hasina tazo ta raba cikin 'yan uwa,don shahidan a yanzu bata da wata qawa banda zunnurah da take sokoto,tunda abun ya faru gaba daya ta cure qawa daga tsarin rayuwarta,saidai gaisuwa kawai ta mutunci,sabida card din bashi da wani yawa sosai,da alama dinner ce da akayi selecting iya adadin mutanen da zasu shiga. 🎍🎍🎍🎍🎍🎍🎍🎍🎍🎍 Gaba daya ta susuce cikin kwanakin ta fita hayyacinta,idan ka ganta saika dauka ba ita bace ba,gashi daga mummy har abban nata ba wanda ya sake bi ta kanta koya tanka mata dangane da hukuncin data yanke na ba zata auri anwar ba bare ta fadi abunda yake ranta ko zataji dadi,kullum kwanan duniya kamar ibada kuwa saita kira number mima sau babu adadi amma tana a kashe amsar kenan kullu yaumin,ko fita yanzu ba kasafai take ba,kishin anwar da
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96